Month: May 2021

An sako ɗaya daga cikin ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Kaduna

An sako ɗaya daga cikin ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Kaduna

Daga AISHA ASAS 'Yan bindiga sun sako ɗaya daga cikin ɗaliban jami'ar Greenfield da suka yi garkuwa da su kwanan nan a Kaduna. Kodayake dai babu wani bayani a hukumance da ya tabbatar da hakan, amma mahaifiyar ɗalibin da ya kuɓutan, Lauritta Attahiru ta tabbatar wa manema labarai kan cewa ɗanta ya dawo gida. Sai dai Lauritta ba ta yi cikakken bayani ba dangane da yadda aka yi ɗan nata ya dawo gida ba, sai da aka biya fansa ko kuwa a'a. Wata majiya ta faɗa cewa a ranar Asabar da ta gabata aka sako ɗalibin bayan kuma mahaifiyarsa ta…
Read More
Arewa ta Tsakiya na kwaɗayin shugabancin APC na ƙasa

Arewa ta Tsakiya na kwaɗayin shugabancin APC na ƙasa

Daga BASHIR ISAH Yankin Arewa ta tsakiya ya nuna ƙudirinsa na neman shugabancin jam'iyyar APC a matakin ƙasa. Yankin ya bayyana sha'awarsa kan neman shugabancin jam'iyyar ne sa'ilin da masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar a yankin suka ziyarci Gwamnan Neja kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta Tsakiya, Abubakar Sani Bello, s fadar gwamnatin jihar da Minna, babban birnin jihar. Yayin da yake bayani kan irin gwagwarmayar da yankin ya sha dangane da yi wa APC hidima tun bayan kafiwarta, Gwamna Sani ya ce bai kamata a baro yankin a baya ba. Yana mai cewa sun amince su shiga a…
Read More
Buhari ya ƙirƙiro cibiyar kula da tu’ammali da ƙananan makamai

Buhari ya ƙirƙiro cibiyar kula da tu’ammali da ƙananan makamai

Daga AISHA ASAS Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da batun ƙirƙiro Cibiyar Kula da Ƙananan Makamai ta Ƙasa (NCCSALW) wadda za ta kasance ƙarƙashin kulawar ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan sha'anin tsaro. NCCSALW ita ce cibiyar da za ta yi aiki a madadin Kwamitin Shugaban Ƙasa Kan Kula da Ƙananan Makamai da aka rusa. Har wa yau, za ta kasance cibiya ta bincike, yin dokoki tare da sanya ido kan harkar ƙananan makamai a Nijeriya. Tuni Shugaba Buhari ya naɗa Major General AM Dikko (Rtd) a matsayin Kodinetan da zai kula da cibiyar. Sanarwar da ta…
Read More
Hoto: Gwamna Bala ya yi maraba da Gamal

Hoto: Gwamna Bala ya yi maraba da Gamal

A kwannan ne ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta jihar Bauchi, Wikki Tourist, ta samu sabon ɗan wasa daga ƙasar Masar, Mahmud Gamal, inda zai ci gaba da ɓarje gyaɗarsa a fagen ta-maula a ƙungiyar. Da wannan ne Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya yi wa sabon ɗan wasan marhabin da zuwa Bauchi, tare kuma da miƙa masa kayayyakin da zai riƙa amfani da su wajen buga wasanni.
Read More
Za a soma cin tarar N100,000 kan masu kada bishiyoyi ba da izinin gwamnati ba a Abuja

Za a soma cin tarar N100,000 kan masu kada bishiyoyi ba da izinin gwamnati ba a Abuja

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Abuja ta ce haramun me ga mazauna birnin su kada bishiyoyin cikin gidajensu da na wuraren da jama'a ke haɗuwa suna shakatawa ba tare da izinin gwamnati ba. Hukumar ta yi gargaɗin duk wanda ta kama da laifin take wannan doka, tarar N100,000 lakadan ta hau kansa. Darakta a Hukumar, Hajiya Riskatu Abdulazeez ce ta bayyana hakan a Abuja a ƙarshen mako. A cewarta, da zarar bishiyoyin da aka daddasa a gidaje suka girma, shi kenan sun zama mallakar gwmamnati wanda dole sai da izinin gwamnatin kafin a sare ko a kada su. Ta ce ɗaukar…
Read More
‘Yan takarar ciyaman 38 sun faɗi gwajin auna fahimta a Kaduna

‘Yan takarar ciyaman 38 sun faɗi gwajin auna fahimta a Kaduna

Daga UMAR M. GOMBE Jam'iyyar APC ta jihar Kaduna ta bayyana rashin cancantar tsayawa takara na wasu mutum 38 daga cikin mutum 115 da suka nuna sha'awarsu ta tsayawa takarar shugabancin ƙananan hukumomin jihar. Uwar jam'iyyar APC ta jihar ta ce, waɗanda lamarin ya shafa an same su da dalilan da suka hana canantarsu shiga takara kama daga dalili na mutum na da wani tabo na laifi da ya taɓa aikatawa ko kuma ya faɗi a gwajin auna fahimtar da aka ba su su rubuta. Manhaja ta kalato cewa wannan shi ne karo na farko a tarihin Nijeriya da aka…
Read More
Yaƙi da Boko Haram: Buhari ya kunyata Afirka – inji ɗan jairida a Ghana

Yaƙi da Boko Haram: Buhari ya kunyata Afirka – inji ɗan jairida a Ghana

Daga FATUHU MUSTAPHA Ɗan jaridar Ƙasar Ghana, Kwesi Pratt Jr, ya ce ya ji kunya matuƙa da ya ji cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda tsohon soja ne, ya nemi ƙasar Amurka da tallafa wa Nijeriya kan batun yaƙi da matsalolin da suka addabi ƙasar. Ɗan jaridar ya ce Shugaba Buhari ya tattara ya bar ofishinsa tun da ya gaza cika alƙawarin da ya ɗaukar wa 'yan Nijeriya. Shugaba Buhari yayin wata ganawa da Ƙaramin Sakataren Amurka, Anthony Blunkrn, a Talatar da ta gabata ya ce ya kamata ya yi a maida AFRICOM zuwa Afirka don ƙarfafa ƙoƙarin da ake…
Read More
‘Yan bindiga sun hallaka kwamishina a Kogi

‘Yan bindiga sun hallaka kwamishina a Kogi

Daga AISHA ASAS 'Yan bindiga a jihar Kogi, sun kashe Kwamishinan Fansho na jihar, Solomon Adebayo, a kan babbar hanyar Kabba zuwa Ilori da ke jihar. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna lamarin ya auku ne cikin daren Asabar da ta gabata sa'ilin da Marigayin ke kan hanyarsa ta zuwa yankin Kabba daga Ilori. Majiyar Manhaja ta ce 'yan bindigar sun buɗe wa motar kwamishinan wuta ne wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwarsa nan take, tare da raunata direbansa. Tuni dai rundunar 'yan sandan jihar ta tabbatar da aukuwar lamarin. Da yake magana a kan batun, mai magana da…
Read More
Buhari ya taya Mohammed Idris murnar cika shekara 55 da haihuwa

Buhari ya taya Mohammed Idris murnar cika shekara 55 da haihuwa

Daga BASHIR ISAH A yau ne fitaccen nan a harkar yaɗa labarai, wato Alhaji Mohammed Idris, ya cika shekara 55 da haihuwa. Tuni dai dangi, 'yan'uwa da abokan arziki suka shiga zazzaga wa jigon fatan alheri dangane da zagayowar wannan rana mai muhimmanci a rayuwar Kakakin Nupe. Shi ma Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bai bari an baro shi baya ba, domin kuwa ya aike da saƙonsa na taya murna ga Babban Sakataren Ƙungiyar Masu Jaridu na Nijeriya (NPAN), Alhaji Mohammed Idris, bisa cikarsa shekara 55 da haihuwa. A cewar Mai Magana da Yawun Shugaban Ƙasa, Garba Shehu, "Shugaba Buhari ya…
Read More
Ma’aikata a kama sana’a, cewar Gwamna Matawalle

Ma’aikata a kama sana’a, cewar Gwamna Matawalle

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi kira ga ma'aikatan gwamnatin jihar cewa baya ga albashi da suke karɓa duk wata, akwai buƙatar su duba su haɗa da sana'a domin samun ƙarin kuɗaden shiga saboda a cewarsa, gwamnati ba ta da halin biyan  sabon mafi ƙarancin albashi. Gwamnan ya ce a halin da ake ciki, gwamnati na fama da biyan basussukan da ta gada daga gwamnatin da ta gabace ta na biyan albashi da gudanar da harkokin gwamnati. Matawalle ya bayyana hakan ne a Juma'ar da ta gabata sa'ilin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Ƙungiyar Ƙwadago (NLC)…
Read More