Editor

9513 Posts
Gwamnan Zamfara ya biya haƙƙin tsoffin ma’aikata N4.3bn

Gwamnan Zamfara ya biya haƙƙin tsoffin ma’aikata N4.3bn

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya biya tsoffin ma'aikatan jihar bashin giraduti sama da Naira biliyan 4.3 da suke bin gwamnatin jihar tun daga shigar 2011. Mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, an fara biyan waɗanda lamarin ya shafa haƙƙoƙinsu ne tun a watan Fabrairu bayan kammala tantance su. Sanarwar da ya fitar ta ce, gwamnatin Zamfara ta biya biliyan N4,337,087,492.06 ga tsafin ma'aikatan jihar da na ƙananan hukumomi da suka yi ritaya. “A watan Fabrt Gwamna Dauda Lawal ya kafa kwamitin tantance bayanan waɗanda lamarin ya shafa sannan aka biya su bashin giraduti…
Read More
HortiNigeria ta shirya wa ‘yan jarida taro kan yaƙi da tsutsar tumatin

HortiNigeria ta shirya wa ‘yan jarida taro kan yaƙi da tsutsar tumatin

Daga WAKILINMU HortiNigeria ta ƙaddamar da gangami ga ‘yan jaridu kan yaƙi da tsutsar tumatir wacce ake kira Tuta absaluta a gidan Kwari, da ke ƙaramar hukumar Bunkure ta Jihar Kano. A sakamakon mummunar illa da tsutsar Tuta absaluta take yiwa tumatir, HortiNigeria, wacce take samun tallafi daga ƙasar Neitherlands, ta ƙaddamar da wani gangami ga manema labarai kan yadda za a magance cutar Sharon wacce aka fi sani da Tuta absaluta. A yayin gudanar da gangamin an nuna yadda aka tsara hanyoyi na yaƙar Tsutsar musamman kasancewar aikin ba na mutum ɗaya ba ne kan ɗaki ne sai an…
Read More
Gwamna Bago ya zo da tsarin da ya dace sauran gwamnoni su yi koyi da shi – Bello Rahaji

Gwamna Bago ya zo da tsarin da ya dace sauran gwamnoni su yi koyi da shi – Bello Rahaji

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Shugaba kuma wanda ya kafa Ƙungiyar RED, Alhaji Bello Giɗaɗo Rahaji, ya bayyana cewa yadda ya ga gwamnan su na Jihar Neja Alhaji Mohammed Umar Bago yake tafi da mulki bisa taka-tsantsan da bin diddigi a kan duk wani aiki ko amana da ya bayar da ci gaban al'ummar jihar Neja, wannan abun koyi ne ga gwamnoni da shugabanni da sauran al'ummar Nijeriya. Domin a cewarsa wannan shi ne zai kawo kyakkyawan cigaba a kowacce jiha da kuma kowane mataki ko na mulki ko da kuwa a cikin gidanka ne kuma wannan ce tasa yanzu…
Read More
Gwamna Abba ya sauya wa shugaban hukumar tattara kuɗin shiga na Jihar Kano wurin aiki

Gwamna Abba ya sauya wa shugaban hukumar tattara kuɗin shiga na Jihar Kano wurin aiki

Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin Dr. Zaid Abubakar a matsayin sabon shugaban hukumar tattaara haraji ta jihar Kano (KIRS). Gwamnan ya kuma amince da naɗin Kassim Ibrahim a matsayin Daraktan zartarwa na hukumar tara kuɗaɗen shiga. Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da babban daraktan yaɗa Labarai na gwamnan jihar Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a daren ranar Talata. Gwamnan ya ce sabon tsarin gudanarwar zai fara aiki nan bada daɗewa ba yayin da tsohon shugaban hukumar tattara kuɗaɗen shiga na jihar Kano Alh. Sani Abdulkadir…
Read More
Haɓaka noman auduga zai farfaɗo da masaƙun da suka durƙushe a Nijeriya – Shugaban ‘yan kasuwar auduga

Haɓaka noman auduga zai farfaɗo da masaƙun da suka durƙushe a Nijeriya – Shugaban ‘yan kasuwar auduga

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Manoma da masu Kasuwnacin Auduga na shiyyar Arewa maso gabashin Nijeriya Alhaji Sadiq Ado, ya bayyana cewa haɓaka noman auduga da kasuwancin ta zai farfaɗo da durƙusassun masaƙun Nijeriya da suka daina aiki. Alhaji Sadiq Ado wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar a jihar Gombe ya ce dawo da noman auduga da tallafawa manoman zai haɓaka tattalin arzikin 'yyan Nijeriya da yawa. Ado ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa inda taɓarɓarewar da harkar ta yi idan gwamnatoci suka shigo wajen taimakawa manoman harkar…
Read More
Masarautar Gaya ta naɗa Munzir Yusuf Ali muƙamin Sarkin Malamai

Masarautar Gaya ta naɗa Munzir Yusuf Ali muƙamin Sarkin Malamai

Mai Martaba Sarkin Masarautar Gaya a Jihar Kano, Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya, ya amince da naɗin Alhaji Munzir Yusuf Ali a matsayin Sarkin Malaman Gaya. Sanarwar naɗin na ƙunshe ne cikin wasiƙar da masarautar ta fitar mai ɗauke da sa hannun Wamban Gaya, Alhaji Mansur Ibrahim Gaya, da kuma kwanan wata 8 ga Mayun 2024. Sanarwar ta ce bikin naɗin zai gudana ne a ranar Juma'a, 17 ga Mayu, 2024, da misalin ƙarfe 10 na safe a Fadar Sarkin Gaya. "Saboda haka ana ba ka shawarar ka ci gaba da shirye-shirye don tabbatar da nasarar wannan naɗin," in ji sanarwar.
Read More
ECOWAS za ta kafa dakarun ko-ta-kwana don yaƙi da ta’addanci a Yammacin Afirka

ECOWAS za ta kafa dakarun ko-ta-kwana don yaƙi da ta’addanci a Yammacin Afirka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta ce za ta kafa dakarun ko-ta-kwana domin tunkarar matsalar 'yan ta'adda masu iƙirarin jihadi da ke tayar da zaune tsaye a ƙasashe daban-daban, kamar yadda shafin intanet na The Nation mai zaman kansa a Nijeriya ya rawaito. Kwamishinan ECOWAS Abdel-Fatau Musah ya faɗi hakan ne a ranar Talata a Abuja cewa ƙungiyar na buƙatar tara dala biliyan 2.4 ga dakarun, inda ƙasashe mambobin ƙungiyar suka bayar da rabin adadin. "A yau, Burkina Faso ta zarce Afganistan a matsayin ƙasa mafi fama da ta'addanci a duniya kuma…
Read More
Ɗan Majalisar Tarayya, Isa Dogonyaro ya kwanta dama

Ɗan Majalisar Tarayya, Isa Dogonyaro ya kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa ɗan Majalisar Tarayya, Isa Dogonyaro, mai wakiltar mazaɓar Garki/Babura a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, rasuwa. Sanarwar rasuwar marigayin ta fito ne ta hannun abokin aikinsa, Mohammed Bello El-Rufa’i, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook da safiyar Juma'a “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Da safiyar yau muka rasa abokin aiki a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, mutumin kirki da ƙwazo. "Da fatan Allah SWT Ya gafarta masa, Ya kuma sanya shi cikin Aljannatul Firdaus," in ji sanarwar.
Read More
Hukumar Alhazan Kano ta biya Naira biliyan 18 ga NAHCON

Hukumar Alhazan Kano ta biya Naira biliyan 18 ga NAHCON

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Darakta-Janar na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, Lamin Rabi’u Ɗanbappa, ya bayyana cewa hukumar ta aikawa Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) sama da Naira biliyan 18 domin shirye-shiryen aikin hajjin shekarar 2024. Sanarwar da kakakin hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya fitar ta ce, duk da cewa mutane 3,110 sun biya kuɗin aikin hajjinsu, yawancinsu suna jiran bizarsu daga Hukumar NAHCON. Ɗanbappa ya kuma buƙaci hukumar da ta hanzarta bayar da bizar kafin ranar da za a rufe yin bizar. Ya jaddada ƙudirin Gwamnatin Kano na kammala gyara sansanin alhazai kafin a…
Read More
CBN ya bai wa masu POS watanni biyu su yi rajista da CAC

CBN ya bai wa masu POS watanni biyu su yi rajista da CAC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umurci duk masu sana’ar POS a ƙasar nan da su yi rajistar kasuwancinsu da hukumar kula da harkokin kamfanoni (CAC) nan da watanni biyu. An bayyana hakan ne bayan wata ganawa tsakanin Fintechs da Shugaban CAC na Ƙasa, Hussaini Magaji (SAN) a Abuja a ranar Litinin. Shugaban na CAC ya ce wa’adin watanni biyu na yin rajistar wanda zai ƙare a ranar 7 ga watan Yuli, ba an yi ba ne don muzgunawa wata ƙungiya ko ɗaiɗaikun mutane ba, amma “ya yi daidai da ƙa’idojin doka da kuma umarnin…
Read More