21
Apr
Daga WAKILINMU A gobe Litinin, 22 ga watan Afrilu idan Allah y'Ya kai mu, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai buɗe taron yaƙi da ta’addanci a Afirka wanda za a yi a Abuja. Nijeriya tare da goyon bayan ofishin yaƙi da ta'addanci na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNOCT) ce ta shirya wannan taro wanda aka yi masa laƙabi da "Ƙarfafa Dangantakar Nahiyar Afirka Don Gina Cibiyoyin Taron Dangin Magance Barazanar Ta'addanci''. Maƙasudin taron na kwana ɗaya shi ne inganta haɗin gwiwar yaƙi da ta'addanci a ɓangarori daban-daban tsakanin ƙasashen yankin, tare da sake fasalin rawar da ƙasashen duniya ke takawa kan batun…
