23
Apr
Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta ce tana shirin haramta wa ɗalibai 'yan ƙasa da shekara 18 nan gurbin karatu a jami'o'i da sauran manyan makarantu da ke faɗin Nijeriya. Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske a lokacin da yake zagayen duba yadda jarrabawar UTME ta 2024 ke gudana a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar ranar Litinin a Abuja. Ministan ya bayyana rashin jin daɗinsa bisa ƙarancin shekarun wasu daga cikin ɗaliban da ya gani suna rubuta jarrabawar, yana mai cewa shekarunsa…
