Editor

9513 Posts
An tsinci gawar jami’in ɗan sanda a gidansa a Maiduguri

An tsinci gawar jami’in ɗan sanda a gidansa a Maiduguri

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Al'ummar Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, sun samu kansu a cikin wani yanayi yayin da aka tsinci gawar wani sifeton ’yan sandan a gidansa. Marigayi jami’in (da aka sakaya sunansa) da ke aiki a sashin Gwange na rundunar ’yan sandan jihar Borno an gansa ne kwanaki uku da suka wuce kafin a gano gawarsa a gidansa da safiyar Asabar. Maqwabtansa a Layin Bayan, unguwar Wulari Jerusalem a Maiduguri, sun ɗaga murya wajen kiransa a lokacin da suka lura ya kulle ƙofarsa ta baya, amma wani ɗoyi na fitowa daga gidan. Nan take aka kai rahoton lamarin…
Read More
Yadda tuhume-tuhume suka kaure tsakanin Abba da Ganduje

Yadda tuhume-tuhume suka kaure tsakanin Abba da Ganduje

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Tataɓurza, musayar yawu da kuma tayar da ƙura irin na siyasa sun kunno kai a Jihar Kano tsakanin  zaɓaɓɓen gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-gida) da kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Shugaban Jam'iyyar APC ta Ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Gumurzun ya fara ne daidai lokacin da Jam’iyyar APC reshen mazavlɓar Ganduje da ke Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano ta dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.  Mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a a mazaɓar Ganduje, Haladu Gwanjo, ne ya sanar da dakatar da…
Read More
Ɗan Nijeriya ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis na duniya

Ɗan Nijeriya ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis na duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani rahoto da Hukumar Shirya Gasar Tennis ta Duniya, ITTF, ta fitar ya nuna cewa ɗan Nijeriya Quadri Aruna ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis 20 na duniya. A cikin jadawalin da hukumar ta fitar, ɗan Nijeriyar ya samu matsayi na 19. A jadawali 2 na baya-bayan nan da hukumar ta fitar, Aruna na matsayi na 22 bayan da ya yi rashin nasara a gasar kofin Tennis ta duniya wadda ta gudana a ƙasar Koriya. Yayin da zakaran gasar a Nahiyar Africa Ɗan Ƙasar Masar Omar Assar, shima ya samu matsawa gaba zuwa matsayi na…
Read More
Ƙaramar Sallah: Sarkin Fataskum, Umar Bubaram, ya hori masu hali kan taimako

Ƙaramar Sallah: Sarkin Fataskum, Umar Bubaram, ya hori masu hali kan taimako

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mai Martaba Sarkin Fataskum, Alhaji Umar Bubaram ya hori masu hali da su ci gaba da taimakon mabuƙata duba da halin da ake ciki na tsadar rayuwa a ƙasar. Sarkin ya bayyana haka ne cikin makon da ya gabata a lokacin da yake miƙa saƙon barka da Sallah ga al'ummar Fataskum da Musulmin duniya bakiɗaya. Alhaji Umar Bubaram ya ce a halin da ake ciki yanzu na taɓarɓarewar tattalin arziki, akwai buƙatar attajirai su dinga taimakon na ƙasa "domin ɗorewar zumunci da ƙaunar juna". Haka kuma mai martaba Sarkin Alhaji Umar Bubaram Ibn Wuriwa…
Read More
Atiku da Wike sun halarci babban taron jam’iyyar PDP a Abuja

Atiku da Wike sun halarci babban taron jam’iyyar PDP a Abuja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Laraba ne ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Alhaji Atiku Abubakar da ministan babban birnin tarayya, Nyesome Wike, suka halarci taron jam’iyyar PDP na ƙasa a Abuja gabanin kwamitin zartarwa na jam’iyyar na ƙasa. Wannan dai shi ne karon farko da tsohon gwamnan jihar Ribas zai halarci taron jam'iyyar PDP tun bayan zaɓen shugaban ƙasa a bara. Wike dai ya samu saɓani da shugabannin jam’iyyar PDP kuma bai goyi bayan zaɓen Abubakar da jam’iyyar ta yi ba a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaven bara. Baya ga…
Read More
Ɗan gidan El-Rufai na yi wa ‘yan Majalisar Dokokin Kaduna barazana kan binciken da ake yi wa mahaifinsa

Ɗan gidan El-Rufai na yi wa ‘yan Majalisar Dokokin Kaduna barazana kan binciken da ake yi wa mahaifinsa

Daga BASHIR ISAH Kakakin Majalisar Jihar Kaduna, Yusuf Liman, ya zargi ɗan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bello El-Rufai, kan tura masa rubutaccen saƙo yana yi masa baraza kan batun binciken tsohuwar gwamnatin mahaifinsa. MANHAJA ta kalato a ranar Talatar da ta bagabata Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin na musamman domin bincikar hada-hadar ƙuɗaɗe da kwangiloli da sauransu, wanda tsohuwar gwamnatin Nasir El-Rufai ta yi daga 2015 zuwa 2023. Kakain Majalisar ya gargaɗi Bello kan ya daina yi wa majalisar barazana kan batun bibciken. Liman ya ƙara da cewa, Bello ya aike masa da saƙon zagi da barazana ta…
Read More
Ƙarancin kayan aiki ya addabi makarantun Jihar Jigawa

Ƙarancin kayan aiki ya addabi makarantun Jihar Jigawa

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Ƙaran cin kayan koyarwa ya addabi makarantu da malamai a Jihar Jigawa, lamarin da ya sa wasu daga cikin malaman makarantun Jihar gabatar da ƙorafin su ga manema labarai. Kaɗan daga cikin ƙorafin ya haɗa da ƙarancin alli da rijistar ɗalibai da tsarin karantawar, wato scheme of work da kuma ƙarancin littatafan karatu. A hannu guda malaman sun yi ƙorafin rashin kulawa a kansu wajan ƙarin girma da gazawar gwamnati wajen biyansu haƙƙinsu na ƙarin girma a kan lokaci. Masu ƙorafin waɗanda suka buƙaci a sakaya sunansu, sun ce ce da yawa daga cikinsu…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe basarake a Taraba

‘Yan bindiga sun kashe basarake a Taraba

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga a Jihar Taraba sun kai hari tare da kashe sarkin masarautar Sansani, Alhaji Abdulmutalib Jankada, da ke cikin Ƙaramar Hukumar Gassol a jihar. Majiyoyi sun ce maharan sun shiga ƙauyen Sensani ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 9 na dare inda suka tafi kai tsaye zuwa fadar masarautar ƙauyen sannan suka kashe Nuhu a gidansa da ke kusa da Ibbi. Majiyarmu ta ce za a yi jana'izar marigayin bayan an sauka daga Sallar Juma'a daidai da karantarwar Musulunci. Ya zuwa haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa daga ɓangaren hukuma kan batun.
Read More
Jami’an tsaro sun hana ’yan majalisar dokoki shiga fadar Sarkin Dutse wajen naɗin Sardauna

Jami’an tsaro sun hana ’yan majalisar dokoki shiga fadar Sarkin Dutse wajen naɗin Sardauna

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Jami'an tsaron farin kaya sun hana Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Alhaji Lawan Muhd Dansure, shiga fadar Mai Martabar Sarkin Dutse a lokacin bikin naɗin Sardaunan Dutse, Alhaji Nasiru Haladu Dano, wanda ya gaji kujerar Marigayi Alhaji Bello Maitama Yusuf, tsohon Sardaunan Dutse, wanda ya rasu a shekarar da ta gabata.  Jami'an tsaron sanye da baƙaƙen gilasai sun samu damar korar Shugaban Masu Rinjaye da tawagarsa ne a lokacin da su ka halarci fadar ta Mai martaba Sarkin na Dutse, Alhaji Hamim Muhd Sunusi, a lokacin da ya ƙaddamar da naxin…
Read More
Gwamnatin Nijeriya na biyan tallafin mai a yanzu fiye da a baya – El Rufa’i

Gwamnatin Nijeriya na biyan tallafin mai a yanzu fiye da a baya – El Rufa’i

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufai ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya na ci gaba da biyan tallafin mai wani abu da ya ce an Nijeriya da dama ba su sani ba. Da yake amsa tambayoyin manema labarai a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, El Rufai ya ce a yanzu gwamnati na biyan fiye da abin da take biya a matsayin tallafin mai a baya. Ya bayyana cewa matakai da dama da aka tanada na rage raɗaɗin janye tallafin mai ba sa tasiri abin da a cewarsa ya sa aka maido da…
Read More