Editor

9513 Posts
Ɗalibai 1,680 aka sace a shekaru 10 a Nijeriya — UNICEF

Ɗalibai 1,680 aka sace a shekaru 10 a Nijeriya — UNICEF

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ya ce hare-hare da sace-sacen da ake kai wa 'yan makaranta a Nijeriya ya karu tun bayan sace ‘yan matan makarantar Chibok a jihar Borno shekaru 10 da suka gabata. UNICEF, a cikin wani rahoto da ta fitar a jiya Litinin, ta ce kashi 37 na makarantu a jihohi 10 ne kawai ke da tsarin gargaɗin farko na gano barazanar irin waɗannan hare-hare. Rahoton ya yi la’akari da alƙaluma masu ban tsoro na tashe-tashen hankula da suka shafi yara. A cikin shekaru 10 da…
Read More
Ba mu wanke Betta Edu, Sadiya Farouq da wasu daga zargin harƙallar kuɗaɗe ba – EFCC

Ba mu wanke Betta Edu, Sadiya Farouq da wasu daga zargin harƙallar kuɗaɗe ba – EFCC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar EFCC ta bayyana cewa har yau ba ta wanke ko da mutum ɗaya da ake zargin handama, harƙalla da karkatar da kuɗaɗen Ma’aikatar Ayyukan Jinqai da Inganta Rayuwar Marasa Galihu ba. EFCC ta kara da cewa, “har yanzu dai ana ci gaba da bincike, kuma sai ƙarin haske ake samu. Saboda haka muna kira ga jama’a su yi watsi da duk wasu surutai da ba su ji daga bakin EFCC ɗin ba.” Haka sanarwar ta ƙunsa, wadda aka fitar da ita a ranar Asabar, mai ɗauke da sa hannun Kakakin EFCC, Dele Oyewale…
Read More
Duk wanda ba zai kare gwamnatin Tinubu ba ya ƙara gaba – Gargaɗin Matawalle

Duk wanda ba zai kare gwamnatin Tinubu ba ya ƙara gaba – Gargaɗin Matawalle

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya yi kakkausan gargaɗi ga ‘yan Arewa da ke cikin gwamnatin Bola Tinubu cewa duk wanda ba zai kare gwamnati ba, to ya sauka ya ƙara gaba. “Yanzu fa ba lokacin da za a yi shiru ba ne.Tilas mu tashi tsaye a san muna cikin wannan gwamnati, ko kuma mu fice kowa ya ƙara gaba. Matawalle ya yi wannan kakkausan furuci ne a matsayin raddi ga ɗaya daga cikin ‘yan Arewa da ke cikin gwamnatin Tinubu, wato Hakeem Baba-Ahmed. Mashawarcin Musamman ne ga Tinubu a Harkokin Siyasa, ya shiga…
Read More
Gwamnan Abba ya rantsar da ƙarin kwamishinoni da mashawarta

Gwamnan Abba ya rantsar da ƙarin kwamishinoni da mashawarta

Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya rantsar da ƙarin sababin kwamishinoni guda huɗu da wasu ƙarin manyan masu ba shi shawara kan harkokin gwamnatinsa a ranar Alhamis. Kwamishinonin da rantsarwar ta shafa sun haɗa da Hon Adamu Aliyu Kibiya da zai jagoranci Ma'aikatar Kasuwanci, sai Hon Abduljabbar Umar Garko wanda aka danƙa wa Ma'aikatar Filaye da Safiyo. Sai kuma Hon. Shehu Aliyu Yanmedi, wanda zai kula da Ma'aikatar Ayyuka na Musamman, sannan Hon Mustapha Rabiu Kwankwaso, Ma'aikatar Matasa da Wasanni. A ɓangare masu bai wa Gwamna shawara kuwa, su takwas ne aka rantsar…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo kan almundahanar N80.2bn

Da Ɗumi-ɗumi: EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo kan almundahanar N80.2bn

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da Rashawa (EFCC) ta ce tana neman tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin tafka almundahanar Naira biliyan N80.2. Hukumar ta bayyana hakan ne a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na soshiyal midiya da yammacin ranar Alhamis. Sanarwar ta ce, “EFCC na neman tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ruwa a jallo bisa laifuka masu alaƙa da almundahar kuɗi da ya biliyan N80.2. "Duk wanda ke da masaniyar inda yake ya hanzarta sanar da hukumar ko kuma ofishin 'yan sanda mafi kusa." Wannan na zuwa ne sa'o'i bayan da Babban Lauyan Ƙasa…
Read More
Akwai ƙalubale sosai a cikin aikin jarida – Hajiya Larai Baba

Akwai ƙalubale sosai a cikin aikin jarida – Hajiya Larai Baba

"Ni ce mace ta farko da ta shugabanci gidan talabijin da rediyo a Jos" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Samun mace kamar Hajiya Larai Baba, wacce ta shafe tsawon shekaru tana aikin jarida, tana gwagwarmayar kawo sauyi al'umma, ba abu ne mai sauƙi ba. Saboda irin yadda ta samu gogewa tun da ƙananan shekaru, kuma ta yi aiki da ƙwararrun ýan jarida da suka kwanta dama, waɗanda suka riƙa sa ta a hanya har ta kai matsayin da a yanzu sunanta ya zama ruwan dare, musamman a cikin garin Jos da kewaye, sakamakon ayyukan da ta rika gudanarwa a tashar Unity…
Read More
Gwamnatin Jigawa za ta gudanar da shirin karantarwa na musamman makarantu 198

Gwamnatin Jigawa za ta gudanar da shirin karantarwa na musamman makarantu 198

By Umar Akilu Majeri Dutse Gwamnatin Jihar Jigawa tare da haɗin gwiwar kamfanin Mukaranta wanda ke samun tallafi daga kamfanin Bono Energy sun ware ƙananan hukumomi 12 daga 27 da jihar ke da su domin aiwatar da shirin kiyarwa na musamman a makarantun 198 da ke yankunan. A halin da ake ciki, an kwashi malamai 240 waɗanda da su ne za a fara ɗabbaƙa wanna shiri na Mukaranta domin koya wa ɗalibai rubutu da karatu a matsayin gwaji a ɗaukacin ƙananan hukumomi 12 da za a fara shirin da su. Ƙananan hukumomin da za su fara cin gajiyar shirin sun…
Read More
JAMB ta ba da umarnin tsare duk iyayen da aka gani kusa da cibiyoyin CBT yayin rubuta jarrabawar UTME

JAMB ta ba da umarnin tsare duk iyayen da aka gani kusa da cibiyoyin CBT yayin rubuta jarrabawar UTME

Daga BASHIR ISAH Hikumar Shirya Jarrabawar Neman Gurbin Karatu a Manyan Makarantu (JAMB) ta bai wa ɗaukacin cibiyoyin CBT umarni kan cewa, su sa a kama duk iyayen da suka gani kusa da cibiyarsu yayin rubuta jarrabawar UTME ta 2024 Hukumar ta ba da wannan umarnin ne yayin taron ƙarshe da ta yi da masu cibiyoyin CBT a ranar Laraba. Mai magana fa yawun JAMB, Fabian Benjamin, ya ce umarnin ya zama wajibi duba da yadda wasu iyayen yara kan mamaye cibiyoyin CBT yayin rubuta jarrabawar kamar yadda aka shaida a baya. Benjamin ya naƙalto Shugaban JAMB, Farfesa Is-haq Oloyede…
Read More
‘Yan bindiga sun sace mutane da dama a Kaduna

‘Yan bindiga sun sace mutane da dama a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Bayanan da MANHAJA ta samu na nuni da cewa, 'yan bindiga sun sace mutanen da ba a tantace adadinsu ba a ƙauyen Angwar Danko da ke mazaɓar Kakangicikin Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari, Jihar Kaduna. Majiyarmu ta ce maharan masu yawan gaske sun dira ƙauyen da misalin ƙarfe 6 na yamma a ranar Laraba. A cewar wani mazaunin yankin, 'yan bindigar sun kaɗa kan mutanen ne zuwa dajin da ke kusa. Ɗan majalisar juhar mai wakiltar Gundumar Kakangi, Yahaya Musa Dan Salio, ya tabbatar da faruwar lamarin. Sai dai ya ce bai kai ga samun cikakken bayani kan…
Read More
Bikin Easter: Rabaran Dakuru ya shawarci ma’aurata su mutunta juna

Bikin Easter: Rabaran Dakuru ya shawarci ma’aurata su mutunta juna

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Babban Rabaran na Cocin ECWA na 1 dake Uke a jihar Nasarawa, Rabaran Dokta Joshua Bulus Dakuru, ya bayyana wasu munanan ɗabi'u dake yin sanadin mutuwar aure da rashin zaman lafiya a auratayya da sauran su inda ya shawarci ma'aurata baki ɗaya musamman kiristoci, su riƙa guje wa waɗannan ɗabi'un. Rabaran Dakuru ya bayyana haka ne a jawabin sa a lokacin wani taro na musamman don tunawa da mutuwa da kuma tashin Isa Almasihu daga matattu wadda aka gudanar a Cocin na ECWA na 1a Uke. Rabaran Dakuru ya ce, waɗannan munanan ɗabi'u dake…
Read More