Editor

9513 Posts
Na gaji tarin basussuka daga gwamnatin El-Rufai, cewar Gwamnan Kaduna

Na gaji tarin basussuka daga gwamnatin El-Rufai, cewar Gwamnan Kaduna

Daga BASHIR ISAH Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya bayyana cewa, ya gaji ɗimbin basussuka daga gwamnatin da ya gada, lamarin da ya ce taliƙe kaso mai tsoka daga kason wata-wata da jihar ke samu a wajen Gwamnatin Tarayya. Basussukan da ya ce ya gada faga gwamnatin Nasir El-Rufai sun haɗa da Dala Miliyan 587 da Naira Biliyan 85 sai kuma kwangiloli guda 115. Gwamna Sani ya bayyana haka ne a wajen taron jin ra'ayoyin jama'ar gari dangane da shugabancinsa da aka shirya ranar Asabar. Ya ce, ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen yin amfani da ɗan…
Read More
Ko ƙuri’ar kwamitin sulhu za ta taimaki Gaza?

Ko ƙuri’ar kwamitin sulhu za ta taimaki Gaza?

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Wannan mako na so yin rubutu ne kan ɗan karen tsada da kujerar aikin hajji ta yi a nan Nijeriya da kai tsaye ta doshi Naira miliyan 8.5 amma nasarar ƙuri'ar neman dakatar da buɗe wuta nan take a Gaza da ta gudana a kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya sa sawun giwa ya take na rakumi. A gaskiya wannan babban labari ne da ya dau hankalin duniya kuma hatta mummunan hari kan gidan rawa a Rasha bai sha gaban wannan labarin ba. Duk kokarin tsagaita wutar musamman don Gazawa su huta a cikin…
Read More
Farashi zai ci gaba da tashi muddin gwamnatoci suka dinga biris da ‘yan kasuwa – Sardaunan Gwaram

Farashi zai ci gaba da tashi muddin gwamnatoci suka dinga biris da ‘yan kasuwa – Sardaunan Gwaram

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Saboda yadda farashin kayyakin abinci da na masarufi har ma da kusan komai a faɗin ƙasar yake ta ƙara wahal da 'yan Nijeriya, baban ɗan kasuwan nan na Jihar Gombe, Alhaji Ahmed Abdullahi (Sardaunan Gwaram), ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da na jihohi baki ɗaya, da su tashi tsaye yanzun nan su ga sun bunƙasa kasuwanci a ƙasa. Har illa yau, Sardaunan Gwaram ɗin wanda shi ne Mataimakin Sakataren Ƙungiyar Haɗin Kan “Yan Kasuwan Jihar Gombe, ya ce muhimman mafitar dai kenan wato gaggauta bunƙasa kasuwanci sannan tallafi ga “yan kasuwa musamman kamar waɗanda…
Read More
Shugaban Kamfanin Binance ya maka EFCC da mashawarcin Tinubu a kotu

Shugaban Kamfanin Binance ya maka EFCC da mashawarcin Tinubu a kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban kamfanin Binance dake tsare a hannun hukumomin Nijeriya, Tigran Gambaryan ya maka Mashawarcin Shugaban Ƙasa Akan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu da Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa a kotu bisa zarginsu da tauye masa haƙƙoƙinsa na bil adama. A ƙarar da ya shigar, Gambaryan ya nemi kotu ta ayyana tsare shi da qwace masa takardun tafiye-tafiyen a matsayin laifin da ya sava sashe na 35 ƙaramin sashe (1) da na (4) na kundin tsarin mulkin na shekarar 1999. Ya buƙaci kotun da ta umarci ofishin mashawarcin…
Read More
Gwamnan Kaduna ya ɗauki nauyin karatun ɗaliban Kuriga

Gwamnan Kaduna ya ɗauki nauyin karatun ɗaliban Kuriga

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi alƙawarin bai wa ɗaliban Kuriga 137 da aka kuvutar daga hannun ’yan bindiga tallafin karatu. Gwamnan ya ce gidauniyarsa ta Uba Sani za ta gyara makarantun Kuriga domin bai wa yara a garin damar samun ingantaccen ilimi. Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga ɗaliban da suka kuvuta daga hannun ‘yan bindiga a gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis. Sani, ya ce bayan sako ɗaliban, gwamnatin jihar ta ɗauki masana ilimin halayyar ɗan adam aiki waɗanda suka shafe lokaci suna tattaunawa da ɗaliban…
Read More
Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hedikwatar Tsaron Nijeriya ta ci alwashin cewa, ba za ta gajiya ba har sai an kama waxanda suka kashe sojoji 17 a Okuama da ke jihar Delta tare da gurfanar da su a gaban shari’a bisa ga dokar Nijeriya. Daraktan yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai qarin haske kan ayyukan soji da ke gudana a sassan ƙasar nan a Abuja, babban birnin Nijeriya. Janar Buba ya ce "an saki sunayen mutane takwas da ake nema ruwa a jallo ciki har…
Read More
Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Daga BASHIR ISAH Bayabnan da Manhaja ta tattaron sun ce, a jimilIance wasu sabbin gwamnoni su 13 sun ci bashi da ya kai Naira Biliyan 226.8 a cikin watanni shida da suka yi a ofis. Wannan bashin kuwa ya shafi wanda gwamnonin suka ci a gida da kuma ƙetare. Binciken News Point Nigeria ya gano cewa, wasu gwamnonin jihohi 16 kuma, basussukan da suka ciyo ya ƙaruwa da Naira Biliyan 509.3. An yi lissafin basussukan ƙetaren ne kan lissafin N889 kan $1 kamar yadda Ofishin Kula da Basussuka (DMO) ya nuna. Rahoton DMO ya ce an tattaro bayanan basussukan ne…
Read More
An karrama Janar Gusau da lambar NIPR

An karrama Janar Gusau da lambar NIPR

Daga BASHIR ISAH A ranar Larabar da ta gabata aka karrama Muƙaddashin Darakta na Sashen Labarai na Tsaro, Brigadier General Ismaila Gusau, Ph.D. mni, da lambar yabo ta NIPR. Cibiyar Hulɗa da Jama'a ta Ƙasa ita ce ta karrama jami'in da wannan lamba ta yabo. An karrama Gusau ne saboda hazaƙarsa wajen ƙoƙarin sauke nauyin aiki da ya rataya a wuyansa. Kuma an karrama shi ne tare da wasu a wajen taron wanda cibiyar da ta ɗauki nauyin shiryawa ta saba shiryawa duk shekara. 'Yan jaridu da jami'an hulɗa da jama'a daga sassa daban-daban na daga cikin waɗanda cibiyar ta…
Read More
Za a ɗage dakatarwar da aka yi wa Ningi ba da daɗewa ba – Akpabio

Za a ɗage dakatarwar da aka yi wa Ningi ba da daɗewa ba – Akpabio

Daga BASHIR ISAH Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa, nan ba da daɗewa ba za a ɗage dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi (PDP, Bauchi ta Tsakiya) a Majalisar Dattawa. Ya bayyana hakan sa'ilin da yake amsa wa manema labarai tambayoyi a wajen wani taro da aka shirya ranar Juma'a a Geneva, Switzerland. Wannan na zuwa ne sa'o'i 24 bayan da Ningi ya yi wa Akpabio kan cewa zai ƙalubalanci dakatar da shi da aka yi a kotu muddin ba a janye dakatarwar ba a cikin kwana 7. An dakatar da Ningi daga majalisar ne biyo…
Read More
Tsohon Mataimakin Gwamnan Kwara, Peter Kisira ya rasu yana da shekara 74

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kwara, Peter Kisira ya rasu yana da shekara 74

Daga BASHIR ISAH An bayyana rasuwar tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Kwara Peter Kisira. Gwamnatin jihar ce ta tabbatar da rasuwar marigayin cikin rasanarwar da ta fitar da safiyar Asabar ta bakin Babban Sakataren Yaɗa Labarai, Rafiu Ajakaye. Marigayin ya bar duniya yana da shekara 74. Kisira ya yi mataimakin Gwamnan Jihar ne a zamanin Gwamna Alhaji Abdulfattah Ahmed, daga watan Mayun 2011 zuwa Mayun 2019. Tuni dai Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana alhininsa kan rasuwar tare da miƙa ta'aziyya ga 'yan uwan mamacin.
Read More