Labarai

An kori sojojin da suka kashe Sheikh Goni Aisami a Yobe

An kori sojojin da suka kashe Sheikh Goni Aisami a Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana ɗaukar matakin korar wasu sojojinta biyu bisa samun su da laifin kashe malamin addinin Musulunci, Sheikh Goni Aisami Gashuwa, a jihar Yobe. Sojojin da lamarin ya shafa su ne Lance Kofur John Gabriel da Lance Kofur Adamu Gideon. Sanarwar korar ta fito ne daga muƙaddashin kwamandan da ke kula da Bataliya ta 241 dake Nguru a jihar Yobe, Laftanar Kanar Ibrahim Osabo, inda ya shaida wa manema labarai cewa kwamitin binciken haɗin gwiwa da aka kafa tare da haɗin gwiwar 'yan sanda ya same su da laifi. Ya ƙara da…
Read More
Makarantar ST.Lous ta yi walimar ɗalibai 29 da suka yi saukar karatun Alƙur’ani Maigirma

Makarantar ST.Lous ta yi walimar ɗalibai 29 da suka yi saukar karatun Alƙur’ani Maigirma

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Makarantar ST Lous mai tsohon tarihi da ke Unguwar Bamfai a birnin Kano, ta yi bikin walimar taya ɗalibanta 29 murna da suka samu falalar rabauta da sauke karatun Alƙur'ani maigirma, a walimar da hukumar makarantar ta shirya musu wadda aka yi a harabar makarantar a ranar Larabar da ta gabata, kamar yadda Malama Halima Baba Yaro, mataimakiyar shugabar makarantar kuma wacce ta jagoranci bikin walimar ɗaliban 29, ta bayyana a lokacin walimar. Har ila yau, Malama Halima Baba Yaro, ta ce wannan ranar ba ƙaramar rana ba ce ga hukumar makarantar da malamai, da…
Read More
Gwamnatina za ta mayar da hankali wajen haɗin kan ƙasa – Atiku

Gwamnatina za ta mayar da hankali wajen haɗin kan ƙasa – Atiku

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ɗan takarar shugabancin Nijeriya na Jam'iyyar PDP a zaɓen 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bada shawarar kafa gwamnatin haɗin kan ƙasa domin tunkara da kuma magance matsalolin da suke addabar ƙasar nan. Hakan na a ƙunshe ne a cikin bayanin da mataimaki na musamman ga Atiku Abubakar kan kafafen yaɗa labarai Abdulrasheed Shehu ya fitar. Da yake jawabinsa, akan maudu'in miƙa mulki a Nijeriya cikin ƙarni na 21 a taron na Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa NBA karo na 62 a Birnin Ikko, wanda babban lauya Olisa Agbakoba ya jagoranta, Wazirin Adamawa ya koka game da…
Read More
A gaggauta hukunta waɗanda suka kashe Sheikh Aisami – JIBWIS

A gaggauta hukunta waɗanda suka kashe Sheikh Aisami – JIBWIS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Jama’atul Izalatul Bid’ah wa Ikamatis Sunna a Nijeriya JIBWIS, ta yi kira ga mahukuntan ƙasar da su “gaggauta” yin hukunci ga wasu sojojin ƙasar biyu da ake zargi da kisan Sheikh Goni Gasua Aisami. Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe da ke Arewa maso gabashin Nijeriya, ta sanar da kama wasu sojoji biyu, waɗanda ake tuhuma da kashe Aisami a ranar Juma’ar da ta gabata. Shugaban ƙungiyar ta ƙasa Sheikh Abdullahi Bala Lau ne ya yi kira ga mahukuntan kamar yadda wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a shafinta na Facebook a ranar Litinin…
Read More
Ba zan miƙa jami’o’in Gwamnatin Tarayya ga jihohi ba – Atiku

Ba zan miƙa jami’o’in Gwamnatin Tarayya ga jihohi ba – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗan takarar Shugaba Nijeriya a Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce ba zai miƙa wa gwamnatocin jihohin ƙasar ragamar tafiyar da jami'o'in gwamnatin tarayya ba. Cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Paul Ibe, ya fitar ya ce sun lura cewa an juya maganar da ɗan takarar shugaban ƙasar na PDP ya yi a wajen wani babban taro na ƙungiyar lauyoyin Nijeriya da ya gudana a Legas a kan batun da ya shafi ɓangaren ilimi da hanyoyin da zai bi wajen warware matsalolin da ɓangaren ke fuskanta. Ya ce a cikin bayanan Atiku,…
Read More
Mun danƙara wa jami’an tsaro isassun kuɗaɗe – Hon. Alhassan Doguwa

Mun danƙara wa jami’an tsaro isassun kuɗaɗe – Hon. Alhassan Doguwa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Tarayya, Alasan Ado Doguwa, ya bayyana cewa Majalisar Tarayya ta danqara wa jami’an tsaron Nijeriya musamman sojoji wadatattun kuɗaɗen da duk ta ke buƙata wajen daƙile matsalar tsaro. Doguwa ya yi wannan iƙirarin ne a ranar Lahadi, lokacin da ya ke kaɓar kyautar karramawa daga ƙungiyar Kano Citizens Forum. Ya ce harkar tsaro abu ne mai muhimmanci sosai wanda majalisa kwata-kwata ba ta wasa da shi. Sauran waɗanda aka karrama a wurin sun haɗa da tsohon Kwamandan Burget ta 3 da ke Kano, Sinyinah Nicodemus da kuma Kamshinan ‘Yan…
Read More
Ana daf da buɗe Jami’ar KHARAN ta Khalifa Ishaqa Rabi’u a Kano

Ana daf da buɗe Jami’ar KHARAN ta Khalifa Ishaqa Rabi’u a Kano

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano An bayyana cewa ana daf da buɗe Jami'ar KHARAN ta Khalifa Sheikh Ishaqa Rabi'u a Jihar Kano. Jami'ar dai ita ce ta farko a Nijeriya da aka assasa ta da nufin bunƙasa karatun Alƙur'ani Maigirma da nazarinsa da kimiyyarsa wacce aka yi wa laƙabi da Jami'ar KHARAN wacce Marigayi Kadimul Ƙur`an Khalifa Sheikh Ishaqa Rabiu ya gina ta kuma ana daf da fara karatu a cikinta tsakanin ƙarshen shekarar nan zuwa farkon shekarar 2023. Kamar dai yadda Malam Anwar Sheik Ishaqa Rabiu ya bayyana a lokacin taron saukan kammala saukan karatun Alƙur'ani Maigirma na shekara,…
Read More
Kamfanin Boska ya gudanar da aikin jinya kyauta a Jihar Sakkwato

Kamfanin Boska ya gudanar da aikin jinya kyauta a Jihar Sakkwato

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe A ƙoƙarin da kamfanin Dexa Medical masu yin Boska ke yi na duba lafiyar mutane a ranar Asabar ɗin da ta gabata, 20 ga watan nan na Agusta, kamfanin ya gudanar da aikin jinya kyauta ga al'ummar Kwannawa dake ƙaramar hukumar Denge Shuni a Jihar Sakkwato. A jawabinsa ga jama'ar da suka ci gajiyar shirin kamfanin na Dexa, shugaban shiyya na kamfanin na yankin Sakkwato Adeyemi Afeez Ola, cewa ya yi kamfanin ya ware wannan ranar ce don taimakawa jama'a masu larurar gani da masu fama da wasu ƙananan cututtuka da za a yi…
Read More
‘Yan sanda sun kama mutum 18 da ake zargi da satar mutane a Benuwai

‘Yan sanda sun kama mutum 18 da ake zargi da satar mutane a Benuwai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar 'yan sanda a jihar Benuwai ta ce jami'anta sun kama wasu mutum 18 da ake zargi da satar mutane tare da ƙwace makamai daga wajensu. Mai magana da yawun rundunar, Catherine Anene Sewuese, cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin da maraice, ta ce mutanen da ake zargin sun yi ƙoƙarin tserewa jami'an 'yan sanda a wani wajen binciken ababen hawa a kan hanyar ƙaramar hukumar Utonkon inda aka kama su. Ta ce an samu makamai a wajen mutanen ciki har da bindiga ɗaya samfurin AK-47, da ƙananan bindigogi biyu da kuma…
Read More
Wayar salula ta yi sanadin ƙonewar gidan mai qurmus a Jihar Legas

Wayar salula ta yi sanadin ƙonewar gidan mai qurmus a Jihar Legas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar 'yan kwana-kwana ta Jihar Legas ta ce a ranar Litinin, wani mutum ya sami raunuka bayan da wani abu ya fashe a wani gidan mai mai zaman kansa da ke garin Badagry na jihar. Babban jami'i da ke kula da reshen hukumar ta Badagry Abel Husu ne ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN aukuwar wannan iftila'in. Ya ce hukumar tasu ta sami labarin abin da ke aukuwa ne a gidan man Yemoral Oil and Gas Petrol Station da ke kan hanyar Ajara a Badagry da misalin ƙarfe 8:55 na ranar…
Read More