Labarai

Buhari ya sake naɗa Bashir Ahmad hadiminsa

Buhari ya sake naɗa Bashir Ahmad hadiminsa

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa Bashir Ahmad matsayin Hadimi na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Sadarwa na Zamani. Sanarwar naɗin na ƙunshe ne cikin wasiƙar da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha, ya aikawa Bashir ɗin mai ɗauke da kwanan watan 20 ga Yulin 2022. Kafin wannan lokaci, Bashir Ahmad shi ne hadimin Shugaba Buhari kan sabbin kafafen yaɗa labari inda ya ajiye muƙamisan don yi takarar ɗan Majalisar Wakilai. Cikin wasiƙar da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya gani, sabon muƙamin da Buhari ya bai wa Bashir zai fara aiki ne daga ranar 19 ga watan Yulin…
Read More
Ƙidayar shekarar 2023 hanyar magance talauci da rashin tsaro ce a Nijeriya

Ƙidayar shekarar 2023 hanyar magance talauci da rashin tsaro ce a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Shugaban Ƙasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, ƙidayar al'ummar ƙasa da za a yi a shekara mai zuwa a Nijeriya za ta taimaka wa gwamnati wajen yaƙi da talauci da kuma rashin tsaro. Shugaban ƙasar ya yi wannan bayani ne a ranar Alhamis ɗin da ta gabata a taron masu ruwa da tsaki a kan ƙididdigar al'umma da ta gidaje na ƙasa gabaɗaya wanda aka gudanar a Abuja. Wannan bayani yana ƙunshe ne a cikin wani jawabi wanda kakakin fadar shugaban ƙasar mai suna Femi Adesina ya sanya wa hannu. Buhari ya ƙara da cewa,…
Read More
Ɗan takarar sanata na APC a Jigawa ya rasu

Ɗan takarar sanata na APC a Jigawa ya rasu

Daga ABUBAKAR MUHAMMAD TAHIR Ɗan takarar sanata na Jam'iyyar APC a Jihar Jigawa, Alhaji Tijjani Ibrahim Gaya, wanda ke neman wakilcin mazaɓar Jigawa ta Tsakiya a zaɓe ami zuwa ya rasu. Alhaji Tijjani Ibrahim Gaya ya rasu ne bayan fama da doguwar jinya da ya yi wanda aka kwantar da shi a Asibitin Nizamiye da ke Abuja. Cikin sanarwar da Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru ya fitar ya aike da saƙon ta'aziya ga 'yan uwa da iyalan mamacin inda ya bayyana marigayin a matsayin ɗan kishin ƙasa abun koyi ga matasa masu tasowa. Gwamna Badaru ya ƙara da cewa,…
Read More
Ku daina ziyarar alƙalai cikin dare, inji Alƙalin Kotun Ƙoli

Ku daina ziyarar alƙalai cikin dare, inji Alƙalin Kotun Ƙoli

Daga AMINA YUSUF ALI Alƙalin Kotun Ƙolin Nijeriya, Mai Shari'a Inyang Okoro, ya bayyana cewa, Sashen Shari'a na ƙasar nan ba za ta taɓa yin aikinta yadda ya kamata ba har sai ta tsira daga matsalar tauye haƙƙi daga gwamnatocin jihohi. Wanda ya haɗa da kai ziyara zuwa gidajen alƙalai domin ƙara wa miyarsu gishiri.  Okoro ya bayyana haka ranar Juma'a a garin Abuja yayin taron laccar da ƙungiyar ma'aikatan Shari'a ta Nijeriya (NBA) ta shirya mai taken: 'Tauye ikon sashen Shari'a a mulkin demokraɗiyya: Dalilansa, sakamakonsa, da kuma mafita'. Mai Shari'ar ya ƙara da cewa, in dai wannan ta'adar…
Read More
Ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun tsaya cak sakamakon rashin sakin kasafin 2022

Ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun tsaya cak sakamakon rashin sakin kasafin 2022

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai ma'aikatu, sassa da kuma hukumomin gwamnati (MDA) da kuma kamfanonin gine-gine da sauransu sun shiga matsanancin ƙarancin kuɗi a sakamakon jinkirin sakin kasafin kuɗi na shekarar 2022 da ya sa maiakatun suka tsaya cak suka kasa gudanar da manyan ayyukan raya ƙasa.  A yanzu haka Ma'aikatun da sassa da kuma hukumomin gwamnati (MDA) waɗanda su ne suka fi buƙatuwa da a saki waɗancan kuɗaɗe na kasafin wanda aka ware domin ayyukan raya ƙasa sayen kayan aiki, da sauransu, sun shiga guna-guni a kan jinkirin da aka samu na qin sakin kuɗaɗen bayan…
Read More
Badaƙalar kuɗi: Gwamna Atiku na fafutukar sasantawa da Amurka a bayan fage

Badaƙalar kuɗi: Gwamna Atiku na fafutukar sasantawa da Amurka a bayan fage

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Atiku Bagudu ya roƙi Gwamnatin Ƙasar Amurka da ta yi wa Allah ta bari a sasanta zargin badaƙalar Dalar Amurka milliyan ɗari da arba'in ($140,000,000:00), wanda ya yi daidai da Naira Billiyan Hamsin da Takwas da ɗigo Uku (#58.3b), waɗanda tsohon Shugaban Nijeriya, Marigayi Janar Sani Abacha, ya ƙetare da su zuwa ƙasashen waje, waɗansu masu bincike suka gano da hannun Gwamna Atikun dumu-dumu a ciki. Kamar yadda Jaridar Premium Times ta ruwaito a shafinta ta ce, shari'ar, wacce ke gudana tsakanin sashen shari'a na Ƙasar Amurka, (US Department of Justice, USDOJ)…
Read More
’Yan bindiga sun fasa Jihar Jigawa, sun kashe jami’in tsaro

’Yan bindiga sun fasa Jihar Jigawa, sun kashe jami’in tsaro

*Mun fatattake su zuwa cikin daji, inji ACG Abba Daga Abubakar Muhammad Tahir  ’Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun halaka jami'in shige da fice tare da raunata guda biyu daga cikin jami'an hukumar. Cikin wata ganawa da manema labarai da Shugaban Hukumar na Jihar Jigawa, ACG Ismail Abba, ya yi da manema labarai a ranar Laraba a Dutse, Babban Birnin Jihar ta Jigawa, ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne da misali qarfe 11:20 na dare lokacin da ’yan bindigar suka nufo shingen bincike na hukumar da ke yankin Birniwa-Galadi. Ya ƙara da cewa, 'yan bindigar sun zo a babura…
Read More
Ɗan majalisa ya tallafa wa al’ummarsa don rage fatara

Ɗan majalisa ya tallafa wa al’ummarsa don rage fatara

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato A wani mataki na ƙarfafa wa da kuma tallaffa wa al'ummar ƙananan hukumomin Gwadabawa da Illela dake a Jihar Sakkwato, ɗan majalisa mai wakiltar ƙananan hukumomin Gwadabawa da Illela a Majalisar Tarayya, Abdullahi Balarabe Salame ya raba kayayyaki ga al'ummar da yake wakilta na maƙudan nairori. A cewar ɗan majalisar wannan ya zama wajibi domin rage wa al'umma raɗaɗin talauci da suke fama da shi. Salame ya ƙara da cewa tallafi ba shakka ya zama tilas kasancewar matsalar talauci da kuma rashin aikin yi ya jefa al'umma cikin ayukkan assha. Shi ma da yake magantawa…
Read More
Addu’a ce takobin dukkan ayyukan ta’addanci – Falakin Ƙaraye

Addu’a ce takobin dukkan ayyukan ta’addanci – Falakin Ƙaraye

Daga DAUDA USMAN a Legas An bayyana cewar gudanar da addu'o'i na musamman kan zaman lafiya ita ce takobin kowane irin ƙalubale da ke addabar Nijeriya. Alhaji Bature Ƙaraye kuma Falaƙin Ƙaraye, mazaunin Legas shi ne ya bayyana haka bayan kammala ɗaurin aurensa a Kano, inda aka yi addu'ar nema wa Nijeriya zaman lafiya da yalwar arziki mai amfani. Taron ɗaurin auren dai ya gudana ne a Masallacin Sheikh Jaafar da ke Unguwar Ɗorayi a cikin birnin Kano, inda ya samu halarta manyan baƙi da nesa da na kusa, haɗi da shuwagabannin majalisar Kasuwar Mile 12 da ke Legas irinsu…
Read More
Uba da ɗansa sun rasa ransu bayan sun faɗa rijiya a Kano

Uba da ɗansa sun rasa ransu bayan sun faɗa rijiya a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Wani magidanci ɗan shekara 60, Malam Bala tare ɗan sa Sunusi Bala, mai shekaru 33 sun faɗa wata tsohowar rijiya da ke Sabon Garin Bauchi, a ƙaramar hukumar Wudil, da ke cikin garin Kano, inda suka rasa rayukansu kafin a kai ga cetosu. Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Alhaji Saminu Abdullahi, ya tabbatar da mutuwar su ranar Laraba da ta gabata a Kano, inda ya ce uba da ɗan nasa sun rasu ne yayin da suke  ɗibar ruwa a rijiya. Sanarwar ta ce lamarin ya faru ne ranar Talata da…
Read More