Siyasa

Neja: PDP ta dakatar da Babangida Aliyu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Neja: PDP ta dakatar da Babangida Aliyu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Daga AISHA ASAS Jam'iyar PDP a Jihar Neja ta bayyana dakatar da Tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dakta Mu'azu Babangida Aliyu. PDP ta Ƙaramar Hukumar Chanchaga ta dagatar da Aliyu ne bisa wasu zarge-zarge a kansa ciki har da haifar da rashin jituwa a tsakanin shugabannin jam'iyyar. Kazalika, an zargi Tsohon Gwamnan da yi wa jam'iyya zagon-ƙasa, sai batun rashin martaba faɗar Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai, wanda ya buƙaci a haɗu a gudanar da babban taron jam'iyya na jiha. Haka nan, akwai zargin cewa Dr Mu'azu Babangida Aliyu ya tallafa wa APC da kuɗi Naira milyan N450 yayin zaɓen…
Read More
Ihejirika ya zama ɗan APC

Ihejirika ya zama ɗan APC

Daga WAKILINMU Shugaban Kwamitin Riƙo na APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya karɓi tsohon Shugaban Rundunar Sojoji Lt.Gen. Oyeabo Azubike Ihejirika (mai murabus) a jam'iyyarsu ta APC. Manhaja ta gano cewa, tun bayo na Ihejirika ya soma raɓar APC inda sai a wannan lokaci ya tsunduma cikinta a bayyane. Sanarwa da ta fito ta hannu Daraktan Yaɗa Labarai ga Buni, Mamman Mohammed, ta nuna an gabatar da Gen. Ihejirika a hukumance ga shugaban riƙo na jam'iyyar APC a Juma'ar da ta gabata a bisa jagorancin Gwamnan Jigawa, Alhaji Abubakar Badaru da Hon. Farouk Adamu Aliyu. Buniya ce,…
Read More
Kotu ta ɗaure Farfesa kan maguɗin zaɓe a Akwa-Ibom

Kotu ta ɗaure Farfesa kan maguɗin zaɓe a Akwa-Ibom

Daga UMAR M. GOMBE Wata babbar kotu a jihar Akwa-Ibom ta yanke wa Farfesa Peter Ogban hukuncin zaman kaso na shekara uku bayan da ta kama shi da laifin tafka maguɗin zaɓe. Kotu ta kama malamin da laifin shirya sakamakon zaɓe na ƙarya tare da sanar da sakamakon yayin babban zaɓen 2019 a matsayinsa na shugaban zaɓe a shiyyar Akwa-Ibom ta Arewa maso-yamma. Farfesan wanda malami ne a Jami'ar Calabar a Sashen Nazarin Harkokin Noma, ya tafka maguɗi wajen haɗa sakamon wasu ƙananan hukumomi guda biyu a wancan lokaci, wato ƙaramar hukumar Oruk Anam da Etim Ekpo. A can baya,…
Read More
Alaƙar Buhari da Tinubu tana ƙara armashi – Fadar Shugaban Kasa

Alaƙar Buhari da Tinubu tana ƙara armashi – Fadar Shugaban Kasa

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya musunta zargin da ake yaɗawa kan cewa ruwa ya yi tsami tsakaninsa da tsohon Gwamnan Jihar Legas kuma jigo a jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu. Buhari ya musunta zargin hakan ne ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu ya fitar inda ya bayyana cewa hakan ba gaskiya ba ne. Sanarwar ta nuna cewa, hasali ma alaƙar da ke tsakanin dattawan biyi sai armashi da ƙarƙo take ƙarawa. A cewar Shehu Garba, “Fadar Shugaban Ƙasa na faɗa da babbar murya cewa babu wani rashin jituwa a tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari…
Read More
APC za ta shafe shekara 32 riƙe da mulkin ƙasa, cewar Buni

APC za ta shafe shekara 32 riƙe da mulkin ƙasa, cewar Buni

Daga WAKILINMU Shugaban Kwamitin Riƙo na Ƙasa na Jam'iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce jam'iyyarsu na da niyar yin mulkin ƙasa nan da shekaru 32 masu zuwa. Buni ya bayyana haka ne a wajen taron ƙaddamar da wani kwamitin APC na musamman mai mambobi 61, ƙarƙashin shugabancin Gwamnan Jigawa Badaru Abubakar, tare da ɗora wa kwamitin nauyin fito da hanyoyin da za a bi wajen gyara zaman jam'iyyar tasu. Kazalika, Buni ya ce ana buƙatar kwamitin ya gudanar bincike a tsakanin mambobin jam'iyya da ma al'umma baki ɗaya sannan ya fitar da manufa da burin…
Read More
Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya karɓi bakuncin tsohon Shugaban Majalisar Wakilai, Mr Dimeji Bankole da tsohonn Gwamnan Jihar Ogun, Mr Gbenga Daniel a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja bayan da suka sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC. Tawagar ta ziyarci Fadar Shugaban ƙasar ne ƙarƙashin jagoranci Shugaban Kwamitin Riƙo na APC kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni tare da Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi da kuma Gwamna Mohammed Badaru na Jigawa. Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kaɗan bayan kammala ganawarsu, Mai Mala Buni ya ce Shugaba Buhari ya yi matuƙar farin ciki…
Read More
Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ita jam'iyyun siyasa 18 kaɗai ta sani kuma su ne za ta yi aiki da su har sai Kotun Ƙoli ta gama yanke hukunci kan jam'iyyun da aka soke rajistar su. Babban Kwamishina kuma shugaban Kwamitin Wayar da kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai na hukumar, MistaFestus Okoye, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai. A sanarwar, ya yi kira ga jam'iyyu 74 waɗanda hukumar ta soke rajistar su da su jira hukuncin na Kotun Ƙoli. Okoye ya ce, “Hukumar Zaɓe…
Read More
Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu a Abuja, ta umurci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta bayyana Chief Ifeanyi Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi na mazaɓar Imo ta Arewa wanda aka gudanar ran 5, Disamb, 2020 a jihar Imo. Alƙali Taiwo Oladipupo Taiwo shi ne wanda ya yanke wannan hukunci inda ya ce kotu ta hanzarta ta tabbatar da Ararume na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar. Kazalika, alƙalin ya bai wa INEC odar ta miƙa wa Ararume takardar shaidar lashe zaɓe cikin sa'o'i 72 daga lokacin da…
Read More
Jam’iyyar AAC ta fatattaki Sowore a ofishin INEC

Jam’iyyar AAC ta fatattaki Sowore a ofishin INEC

Daga FATUHU MUSTAPHA 'Ya'yan jam'iyyar African Alliance Congress (AAC) sun ce suna kan bakansu na korar da suka ce an yi wa Omoyele Sowore daga jam'iyyarsu har ma da neman 'yan sanda su kama shi saboda shigan burtun da suka ce ya yi musu. A wannan Litinin ne wani gungun mutane ƙarkashin jagorancin Sowore suka yi yinƙuri mamaye hedikwatar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a Abuja amma sai 'yan jam'yyar AAC ƙarƙashin jagorancin shugabansu na ƙasa, Dr. Leonard Nzenwa, suka fatattake su. Binciken Manhaja ya gano cewa, Sowore da mutanensa sun ziyarci ofishin INEC ne da nufin…
Read More
2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

Daga WAKILINMU Mambobin Ƙungiyar Matasa Magoya Bayan Tinubu (NYMT), sun yi kira ga jigon jam’iyyar APC, Asiwaju Ahmed Tinubu, da ya fito takarar neman shugabancin ƙasa a 2023. Matasan sun yi ra’ayin cewa babu wanda ya fi cancanta ya gaji Shugaba Muhammadu Buhari kamar Tinubu domin ci gaba ƙarfafa nasararorin da gwamnatin APC ta samu. A cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a Abuja, Darakta Janar na ƙungiyar, Mukhtar Husseini ya jigon ya yi sadaukarwa sosai wajen ɗorewar dimukraɗiyyar da ake cin moriyarta a yau. Ya ce buƙatar mara wa Tinubu baya ta taso ne bisa la’akari da…
Read More