Siyasa

Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa za ta shirya wata bita ta musamman domin wayar da kan ma'aikatan ta na sashen faɗakar da masu zaɓe da ke hedikwatar ta da kuma jihohi. Wata sanarwa da ta fito daga hukumar a ranar Asabar ta ce bitar, mai taken "Faɗakar da Mai Faɗakarwa", wato "Train-the- Trainers (ToT)", an kasa ta zuwa gida biyu saboda matsalar annobar korona (COVID-19) da ake fama da ita. Kashin farko za a yi bitar ga shugabannin sashen faɗakar da masu zaɓe (HODs VEP) da ke jihohin Kudu da kuma waɗanda su ke…
Read More
IMO: An buƙaci Buhari da shugabannin APC su shiga tsakanin Uzodima da Okorocha

IMO: An buƙaci Buhari da shugabannin APC su shiga tsakanin Uzodima da Okorocha

Daga AISHA ASAS Wani gungun magoya bayan dimukraɗiyya sun gudanar da zanga-zangar lumana a Abuja inda suka nuna rashin jin daɗinsu dangane da kama tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okoroca, da 'yan sanda suka yi tare da yin kira ga Shugaba Buhari da sauran shugabannin APC a kan su gaggauta shiga tsakani. An ga masu zanga-zangar ɗauke da kwalaye waɗanda aka rubuta saƙonni daban-daban a jikinsu masu nuna rashin kyautatuwar abin da Gwamnan Imo, Hope Uzodima ya yi da kuma nuna goyon baya ga Rochas. Masu zanga-zangar sun ra'ayin cewa kama Okorocha da aka yi take-take ne na neman…
Read More
Zaɓen ƙananan hukumomin Oyo ɓata kuɗi da lokaci ne, inji APC

Zaɓen ƙananan hukumomin Oyo ɓata kuɗi da lokaci ne, inji APC

Daga FATUHU MUSTAPHA Jam’iyyar APC a jihar Oyo, ta ce zaɓen ƙananan hukumomi da aka shirya sake gudanarwa a ranar 15 ga Mayu mai zuwa a jihar, tamkar ɓata kuɗi da kuma lokaci ne. Shugaban riƙo na APC a jihar, Chief Akin Oke, ya bayyana zaɓen a matsayin lamarin da ba zai yi armashi ba balle ya ja hankalin ‘yan siyasa na gaskiya. Yana mai cewa, an ga faruwar irin haka a baya, inda gwamnan jihar kan haifar da tsaiko ga sha’anin ƙananan hukumomin jihar waɗanda su ne mataki na uku a matakan gwamnati. Oke, ya ce zai kasance abu…
Read More

Tawagar PDP ta ziyarci Gwamna Bello

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Neja Abubakar Sani Bello, ya karɓi baƙuncin tawagar kwamitin sulhu na jam'iyyar PDP a yammacin Alhamis. Tawagar ta ƙunshi Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Bukola Saraki, da Tsohon Gwamnan Neja, Dr Mu'azu Babangida Aliyu, da Tsohon Gwamnan Gombe, Ibrahin Hassan Dankwambo, da Tsohon Gwamnan Katsina, Ibrahim Shema da fai sauransu. Tawagar ta ziyarci Gwamna Bello ne domin jajanta masa game da sace ɗaliban sakandare da 'yan bindiga suka yi kwanan nan. Gwamna Bello ya wallafa bayanin ziyarar a shafinsa na twita a yammacin Alhamis.
Read More
Zamfara: Wani jigon APC ya musanta zancen yana da matsala da EFCC

Zamfara: Wani jigon APC ya musanta zancen yana da matsala da EFCC

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wani  mai ruwa da tsaki kuma tsohon ɗan takarar gwamna a Zamfara yayin zaɓen 2019, Hon. Aminu Sani Jaji ya ce bai san da wata shari’a da ta haɗa shi da hukumar Hana Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ba har ta kai ga sanya masa alama a gidansa da ke Gusau ranar Juma’a. Ɗan siyasar wanda ya yi magana da ’yan jaridu a wayar tarho ya ce, babu wanda ya gayyace shi ko ya kusanta shi ko dai a EFCC ko kuma a ko wace hukuma, kuma saboda haka ya zama abin mamaki a gare…
Read More
Majalisa ta buƙaci Buhari ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalolin tsaro

Majalisa ta buƙaci Buhari ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalolin tsaro

Daga WAKILIN MU Majalisar dattijan Najeriya ta buƙaci Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalolin tsaron da suka addabi sassan Nijeriya. Majalisar ta buƙaci haka ne bayan da ‘yan bindiga suka sace ɗalibai sama da 20 a Kwalejin Kimiyya ta Kagara, Jihar Nejs'a, a Larabar da ta gabata. Sanata Sani Musa da ke wakiltar gabashin Jihar Neja, wanda shi ne ya gabatar da ƙudirin neman shelar dokar ta-ɓacin, ya ce ‘yan bindigar da suka sace ɗaliban na sanye ne da kayan sojoji. Haka nan, Majalisar ta bumaci hukumomin tsaron Nijeriya da su kafa rundunar haɗin gwiwa sojoji…
Read More
Yadda na sayar da kadarorina don bada tallafin karatu ga ɗaliban Kano 370 – Kwankwaso

Yadda na sayar da kadarorina don bada tallafin karatu ga ɗaliban Kano 370 – Kwankwaso

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Kano na dauri, Rabiu Kwankwaso, ya bayyana yadda ya sayar da wasu kadarorinsa domin ɗaukar nauyin ɗalibai 'yan asalin Kano su 370 zuwa karatu a ƙasashen ƙetare a ƙarƙarshin Gidauniyar Kwankwasiyya. Kwankwaso ya bayyana haka ne a lokacin da ya je tarbar ɗaliban da suka ci gajiyar shirin da suka dawo daga Indiya da Dubai a babban filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, inda ya bayyana gamsuwarsa dangane da ayyukan gidauniyar. Tsohon Ministan Tsaron ya ce a lokacin da ya yanke shawara kan batun ɗaukar nauyin ɗaliban sai ya ji ya gamsu da ya…
Read More
Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya sabunta rajistarsa a APC

Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya sabunta rajistarsa a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A Juma'ar da ta gabata Shugaban Jaridun Manhaja da Blueprint, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya sabunta rajistarsa ta zama ɗan jam'iyyar APC a rumfar zaɓensa da ke Malagi, a ƙaramar hukumar Gbako da ke jihar Neja. Bayan kammala rajistarsa, Alhaji Idris ya yaba da yadda aikin yin rajistar ke guna cikin lumana a rumfar zaɓensu, tare da kira ga 'yan jam'iyyarsu ta APC a faɗin jihar kan kowa ya tabbatar da ya yi rajista ko sabunta rajistarsa. Yana mai cewa, "Na yi matuƙar farin ciki da yadda aikin yin rajistar ke gudana. Wannan wata alama ce mai…
Read More
Ganduje ya rantsar da sabbin ciyamomi a Kano

Ganduje ya rantsar da sabbin ciyamomi a Kano

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Jihar Kano ta rantsar da sabbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin jihar su 44 a Juma'ar da ta gabata. Sa'ilin da yake jawabi yayin bikin rantsarwar, Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya ce cika aiki shi ne babban abin da gwamnatinsa ta fi maida hankali a kai. Tare da kira a gare su da su kasance masu ƙwazo da kuma yin aiki da gaskiya. A cewar gwamnan, ƙanan hukumomi a matsayin mataki na uku na tsarin gwamnati na buƙatar jajirtattun shugabanni da za su yi aiki tukuru. Yana mai cewa sadaukarwa da kuma cika aiki su ne…
Read More
Gwamna Bello ya naɗa sabon shugaban ma’aikata

Gwamna Bello ya naɗa sabon shugaban ma’aikata

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya naɗa Mrs. Hannah Odiyo a matsayin sabuwar Shugaban Ma'aikata na Gwamnatin Jihar. Sakataren Gwamnatin Jihar, Dr. Folashade Arike Ayoade ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis. Kafin naɗin nata, Mrs. Odiyouta ta kasance riƙe da matsayin sakatariyar Ma'aikatar Harkokin Noma na Jihar Kogi. Gwamna Bello ya yi yabo na musamman ga shugabar ma'aikata mai barin gado, Deborah Ogunmola dangane da irin gudunmawar da ta bayar ga cigaban sha'anin aikin gwamanti a jihar. Kana ya taya sabuwar shugabar murnar samun sabon muƙami tare da…
Read More