Month: February 2021

Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Daga BASHIR ISAH An gudanar da jana'izar jami'an sojin saman nan su 7 da suka rasu a haɗarin jirgin sama da ya auku a Abuja a Lahadin da ta gabata. Jami'an da lamarin ya shafa sun cim ma ajalinsu ne bayan da jirginsu, ƙirar Beechcraft King Air 350, ya faɗo a ƙauyen Bassa daura da Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe, bayan da suka tashi da nufin zuwa aiki a jihar Neja. Mai Magana da Yawun Rundunar Sojin Sama na Nijeriya, Air Vice Marshal Ibikunle Daramola ya ce jirgin ya fuskanci matsalar inji kafin aukuwar haɗarin. Cikin waɗanda suka…
Read More
An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

Daga WAKILIN MU An sako direban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Adamawa United wanda aka yi garkuwa da shi a ranar Asabar da ta gabata. An yi garkuwa da direban ƙungiyar ne a lokacin da suka faɗa hannun wasu 'yan fashi da makami a kan hanyarsu ta zuwa birnin Legas don buga wasan da aka tsara musu a can. Yazu haɗa wannan labari, babu wani cikakken bayani a kan ko sai da aka biya diyya kafin aka saki direban. Tun farko, 'yan fashin sun buƙaci a biya diyyar naira milyan N50 kafin su saki direban da suka yi garkuwa da shi,…
Read More
Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Daga FATUHU MUSTAPHA Allah Ya yi wa fitaccen tsohon Ministan Harkokin Mai na Saudiyya, Ahmed Zaki Yamani, rasuwa. Yamani ya rasu ne a wata asibitin Landa a Litinin da ta gabata. Wata 'yar marigayin mai suna Mai Yamani, ta ce matsalar zuciya ce ta yi ajalin mahaifin nata, inda ya rasu yana da shekara 90. Yamani na ɗaya daga cikin mutanen da ƙasar Larabawa ba za ta mancewa da su ba saboda irin rawar da ya taka wajen cigabanta. A halin rayuwarsa, marigayin ya yi tsayin daka wajen bunƙasa harkokin mai na ƙasar Saudiyya. A matsayinsa na ministan albarkatun mai…
Read More
Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Daga WAKILIN MU Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin tsoffin Shugabannin Tsaron Nijeriya a matsayin jakadu. Wanna ya faru ne a Talatar da ta gabata. Idan ba a manta ba, a Janairun da ya gabata Shugaba Buhari ya zaɓi General Abayomi G. Olonisakin da Lt. General Tukur Y. Buratai da Vice Admiral Ibok-Ete E. Ibas da kuma Air Marshal Sadique B. Abubakar don zama jakadun Nijeriya bayan murabus da suka yi daga aiki ba da jimawa ba. Amincewa da naɗin ya zo ne bayan gamsuwa da majalisar ta yi da rahoton kwamitin majalisar kan harkokin ƙasashen waje ƙarƙashin jagorancin Adamu…
Read More
Kuɗin intanet: Majalisa ta gayyaci shugaban CBN don ya yi ƙarin haske

Kuɗin intanet: Majalisa ta gayyaci shugaban CBN don ya yi ƙarin haske

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya bayyana a gaban Majalisar Dattawa domin kare batun haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet (crypto currencies) da gwamnati ta yi. Majalisar ta gayyaci Emefiele ne domin ya yi mata ƙarin haske kan irin damarmaki da kuma haɗarin da ke tattare da harkar kuɗaɗen intanet ga tattalin arzikin ƙasa. A can baya, Babban Bankin, ta hannun Daraktan Sashen Sanya wa Bankuna Ido Bello Hassan, ya bayyana cewa waɗannan kuɗaɗe na intanet wasu da ba a san ko su wane ne ba suke bada su kuma ba tare da wasu sanannun dokoki ba.…
Read More
EFCC ta yi sabon shugaba

EFCC ta yi sabon shugaba

Daga AISHA ASAS Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin sabon Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Sanatocin sun shafe sa'o'i biyu suna tantance Bawa kafin daga bisani suka tabbatar da shi a sabon matsayin nasa. Yayin da ake tantance shi, Bawa ya bai wa majalisar tabbacin cewa zai yi aiki tukuru don gyara wa hukumar zama ta hanyar inganta harkokinta kafin ƙarewar wa'adin jagorancinsa. Bawa ya ce zai yi aiki tare da waɗanda suka dace a sassan duniya domin tabbatar da Nijeriya ta amfana da dukiyoyinta da aka…
Read More
Makinde ya sake buɗe kasuwar Shasha

Makinde ya sake buɗe kasuwar Shasha

Daga AISHA ASAS Bayan shafe kimanin makonni biyu da rufe kasuwar Shasha a jihar Oyo sakamakon ɓarkewar rikici a tsakanin 'yan kasuwan kasuwar, Gwamna Seyi Makinde ya bada umarnin sake buɗe kasuwar ba tare da wani jinkiri ba. Makinde ya buƙaci sake buɗe kasuwar ne yayin wata ganawa da ya yi da shugabannin Hausawa da Yarabawan yankin a fadar gwamnatin jihar da ke Ibadan. Gwamnan ya ce an ɗauki matakin sake buɗe kasuwar ne duba da yadda rufe kasuwar ya yi tasiri kan tattalin arzikin yankin da ma jihar baki ɗaya. Ya ce yayin da ya ziyarci Sarkin Sasa da…
Read More
An yi garkuwa da sirikar Mangal a Katsina

An yi garkuwa da sirikar Mangal a Katsina

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotannin da Manhaja ta samu daga jihar Katsina, sun nuna 'yan bindiga sun sace sirikar hamshaƙin ɗan kasuwar nan Alhaji Dahiru Barau Mangal, a Katsina. Majiyar Manhaja ta ce lamarin ya faru ne a daren Talata a yankin ƙaramar hukumar Matazu, inda 'yan bindigar suka je suka ɗauki Hajiya Rabi. Majiyar wadda ta buƙaci a sakaya sunanta, ta ce da misalin karfe 1 na daren Talata 'yan bindigar suka shiga gari suka tafi kai tsaye zuwa gidan Hajiya Rabi suka ɗauke ta suka yi gaba ba tare da an san inda suka nufa ba. Da ma dai…
Read More
EFCC ta kama ‘yan fashin intanet 9 a Minna

EFCC ta kama ‘yan fashin intanet 9 a Minna

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC), ta cafke wasu 'yan fashin intanet su tara a Minna, babban birnin jihar Neja. EFCC ta cafke waɗanda lamarin ya shafa ne a ranar Litinin biyo bayan bayanan sirri da ta ce ta samu a kansu dangane da ayyukan zambatar mutane da suke aikatawa. Kayayyakin da EFCC ta ce ta ƙwace a hannu matasan sun haɗa da ƙananan kwamfutoci da wayoyin salula da kuma motoci. Hukumar ta ce, za ta gurfanar da 'yan fashin a kotu da zarar ta kammala bincikenta.
Read More