Month: June 2021

Kansilan Guringawa, Muslihu Yusuf ya tallafa wa yara sama da 50 da kuɗin JAMB

Kansilan Guringawa, Muslihu Yusuf ya tallafa wa yara sama da 50 da kuɗin JAMB

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kansilan Guringawa a cikin Ƙaramar Hukumar Kumbotson Jihar Kano ya gabatar wa Babbar Sakatariyar Ilimi ta ƙaramar hukumar Kumbotso da ƙudurin sa na tallafa wa harkar ilimi daga tushe, kana ya gabatar mata da kwamitin da ya kafa na bunƙasa harkar ilimi a mazaɓar sa, wato 'Guringawa Ward Education Promotion Committee', inda kwamitin ya ƙunshi ƙwararrun malaman makarantun firamare, sakandare har zuwa jami'a, sannan da masu hannu da shuni da masu unguwanni da sauran jagororin al'umma har 11 a matsayin mambobin kwamitin. A Alhamis da ta gabata, kwana guda da kai ziyarar kansilan ofishin…
Read More
2023: Sai da haɗin kai APC za ta ƙwaci mulki a hannun PDP a Taraba, cewar Ɗan Atiku

2023: Sai da haɗin kai APC za ta ƙwaci mulki a hannun PDP a Taraba, cewar Ɗan Atiku

Daga ABUBAKAR A. BOLARI, a Gombe An bayyana cewa muddin aka samu haɗin kan da ya kamata, cikin ruwan sanyi APC za ta karɓe mulkin Taraba daga hannun PDP a 2023. Bayanin haka ya fito ne daga bakin jigo a APC a jihar Taraba kuma mai neman shugabancin APC na jihar, Muhammad Ɗan Atiku Jalingo, yayin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai kwanan nan a Gombe domin nuna sha'awarsa ta neman jagorancin APC ta Taraba. Ya ce rashin shugabanci nagari da rashin mutunta jama'a ne yasa APC ta faɗi zaɓe, amma tun da yanzu al'ummar Jalingo sun gane…
Read More
Haramta Tiwita, Gwamnati ta bada odar hukunta duk wanda aka kama da laifin take doka

Haramta Tiwita, Gwamnati ta bada odar hukunta duk wanda aka kama da laifin take doka

Daga AISHA ASAS Babban Lauyan Nijeriya kuma Ministan Shari'a, Justice Abubakar Malami, SAN ya bada umarnin zartar da hukunci cikin gaggawa a kan duk wanɗanda aka samu da laifin take dokar haramta Tiwita a Nijeriya. Umarnin ministan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da aka fitar ta hannun hadimin ministan kan sha'anin hulɗa da jama'a, Dr. Umar Jibrilu Gwandu a ranar Asabar. A cewar sanarwar, "Malami ya bai wa Daraktan Sashen Gabatar da Ƙararraki (DPPF) na ofishinsa, da ya dukufa aiki tare da shirye-shiryen gurfanar da duk waɗanda aka samu sun yi wa dokar Gwamnatin Taryya na dakatar da…
Read More
Labari da ɗuminsa: Kamfanonin sadarwa a Nijeriya sun soma daƙile hanyoyin shiga Tiwita

Labari da ɗuminsa: Kamfanonin sadarwa a Nijeriya sun soma daƙile hanyoyin shiga Tiwita

Da alama dai matakin dakatar da harkokin Tiwita a Nijeriya da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka a Juma'ar da ta gabata ya soma aiki. Domin kuwa 'yan Nijeriya sun wayi gari Asabar sun kasa samun zarafin yin mu'amala da shafukan Tiwita kamar yadda suka saba sakamakon kamfanonin sadarwa a ƙasar, da suka haɗa da MTN, Airtel, Glo da kuma 9Mobile, sun soma daƙile hanyar shiga masarrafin Tiwita. Kodayake dai kamfanonin sadarwar ƙarƙashin ƙungiyarsu, sun fito sun bayyana cewa sun soma daƙile hanyar shiga Tiwita ga masu amfani da layukansu kamar yadda yake ƙunshe cikin wata sanarwa da suka bayar a ranar…
Read More
Gwamnati ta dakatar da harkokin Tiwita a Nijeriya

Gwamnati ta dakatar da harkokin Tiwita a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harkokin kamfanin Tiwita a Nijeriya har sai baba-ta-gani. Ministan Yaɗa Labarai da Al'adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a. Ministan ya nuna yadda ake amfani da shafukan Tiwita wajen aiwatar da harkokin da ke haifar wa Nijeriya cikas. Kazalika, ya ce Gwamnatin Tarayya ta umarci Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Kasa (NBC) da ta hanzarta shirya shirin bada lasisi ga ɗaukacin OTT da kuma harkokin soshiyal midiya a cikin ƙasa. Sanarwar ta fito ne ta hannun hadimi na musamman ga…
Read More
An kama kayayyakin fasaƙwauri na sama da milyan N100 a Katsina

An kama kayayyakin fasaƙwauri na sama da milyan N100 a Katsina

Daga UMAR M. GOMBE Jami'an Hukumar Yaƙi da Fasaƙwauri ta Nijeriya, sun yi nasarar kama kayayyakin fasaƙwauri da harajinsu ya kai milyan N101,027,350 wanɗanda aka shigo da su cikin ƙasa ta ɓarauniyar hanya a jihar Kastina. Daga cikin kayayyakin da jami'an suka kama a ranar Alhamis da ta gabata har da motoci guda 14 da harajinsu ya kai milyan N91,592,500, haɗa da kayan abinci da sauransu waɗanda harajinsu ya kai N9,434,850. Da yake bayani yayin taron manema labarai a babban ofishin hukumar na yankin Katsina, Shugaban Riƙo na Kwastam na Katsina, DC Dalha Wada Chedi, ya jaddada aniyar Hukumar Kwastam…
Read More
Har mai sayayya a yanar gizo na da damar kai ƙorafi hukumar kula da haƙƙin kwastoma a Kano – Hon. Nasiru Na’ibawa

Har mai sayayya a yanar gizo na da damar kai ƙorafi hukumar kula da haƙƙin kwastoma a Kano – Hon. Nasiru Na’ibawa

Hon. Nasiru Usman Na’ibawa shi ne Mai Taimaka wa Gwamnan Jihar Kano na Musamman kan yadda hukumar Karota da Kwanzuma ke ciki a fagen yin ceto rayuwar al’umma daga halaka tun daga abin da za su ci ko su yi mu’amala zuwa titinan da suke zirga-zirgar yau da kullum. Ga yadda tattaunawarsa da Wakiliyar Manhaja, Bilkisu Yusuf Ali, ta kasance: Me za ka fara da shi game da Hukumar Karota ta Jihar Kano?Ita wannan hukumar ta Karota hukuma ce da aka kafa ta bisa doka tun a tsohuwar gwamnatin Kano, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso wadda aka kafa ta kan raguwar…
Read More
Murza gashin baki da Buhari ya yi

Murza gashin baki da Buhari ya yi

A yamma ranar 1 ga Yuni, 2021, Shugaban Ƙasar Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya yi wani furuci ma jan hankalin da ya dace da buƙatar Nijeriya da ’yan Nijeriya, wanda kuma ba kasafai ake samun sa aikata irin waɗannan kalamai ba. A taƙaice ma dai, gwamnatinsa ba ta cika yin irinsu ko da da yawunsa ne tun bayan kafuwarta a watan Mayu na shekara ta 2015 zuwa yanzu a watan Yuni na shekara ta 2021. Da yawa suna alaƙanta hakan da kasancewar Shugaban Ƙasar dattijo, Hausa-Fulani, ɗan Arewa, gogagge da sauran ɗabi’u makamantan hakan, waɗanda su ne suke sanya ake kallon…
Read More
Baƙin kishi: Anya kuwa ciwon ‘ya macen na ‘ya macen ne?

Baƙin kishi: Anya kuwa ciwon ‘ya macen na ‘ya macen ne?

Daga AMINA YUSUF ALI Assalamu alaikum. Masu karatu sannunku da jimirin karanta wannan fili namu na Zamantakewa. Wanda yake zuwa muku kowanne mako a jaridarku mai farin jini ta Manhaja. A wannan makon za mu tattauna a kan zafin kishin mata da abinda ya je kawo shi, da kuma yadda za a magance shi. A sha karatu lafiya. Kafin na shiga rubutun gadan-gadan. Ya kamata na tuna wa 'yan'uwana mata cewa, mu ne jinsin da muka fi nuna muna da haɗin kai yayin da wata yar uwarmu ta shiga wani hali fiye da maza. Kuma mu ne kullum muke iƙirarin…
Read More