Editor

9513 Posts
Yan Nijeriya za zu yi murna idan aka rushe zaɓen Tinubu – PDP

Yan Nijeriya za zu yi murna idan aka rushe zaɓen Tinubu – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar PDP ta ce 'yan Nijeriya za su fito kan tituna suna murna idan har aka soke ayyana Bola Tinubu a matsayin Shugaban Ƙasa. Sai dai a martanin da ta mayar cikin gaggawa, jam’iyyar mai mulkin ƙasar ta ce PDP na rugujewa ne kawai, inda ta dage cewa Shugaba Tinubu na da hurumin ‘yan Nijeriya kuma zai yi aiki a kan haka kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada. Pedro Obaseki, Daraktan Dabaru da Bincike na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na PDP (PCC) wanda ya yi wa manema labarai jawabi gabanin…
Read More
An tashi baram-baram a zaman sulhu kan rigimar kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

An tashi baram-baram a zaman sulhu kan rigimar kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Idan ba a manta ba jaridar Blueprint Manhaja a kwanan nan ne ta kawo muku labarin rigimar da ta ɓarke akan zaɓen sabon shugabancin majalisar dokokin jihar ta Nasarawa karo na 7, inda a ƙarshe aka samu ɓangarori 2 wato ɓangaren Honorabul Oga Ogazi da na shugaban majalisar dokokin dake neman zarcewa wato Honorabul Balarabe Ibrahim Abdullahi. Kasancewa rigimar ya ƙi ci ya kuma qi cinyewa ne sai wasu masu ruwa da tsakin jihar dake faɗa aji da sarakunan gargajiyan jihar da sauran su ciki har da gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule suka ɗauki…
Read More
An gaza biyan ’yan wasa mata kuɗaɗensu gabanin fara gasar kofin duniya

An gaza biyan ’yan wasa mata kuɗaɗensu gabanin fara gasar kofin duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Hukumar Kula da Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) Gianni Infantino, ya ce babu tabbacin hukumomin ƙwallon ƙafar ƙasashe da suka sami gurbi a gasar lashe kofin duniya ta mata da aka fara a ranar Alhamis, da ƙasashen Australia da New Zealand za su ɗauki nauyi, za su iya kammala rabawa ’yan wasansu kuɗaɗen da ya kamata a ba su. Kowace 'yar wasa da za ta fafata a gasar za ta samu dala dubu 30, wanda a baya hukumar ta ce za ta tura musu kuɗinsu kai tsaye, ba sai ya bi ta hannun hukumomin ƙasashensu…
Read More
Nijeriya ta samu tallafin Dala miliyan 9.3 don ƙarfafa allurar rigakafin Covid-19

Nijeriya ta samu tallafin Dala miliyan 9.3 don ƙarfafa allurar rigakafin Covid-19

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ma'aikatan lafiya suna shirya rigakafin Moderna Coronavirus (COVID-19) da za a gudanar a sabuwar cibiyar rigakafin jama'a da aka buɗe a Tokyo, Japan, Mayu 24, 2021. Gwamnatin Tarayya ta samu tallafin Dalar Amurka miliyan 9.3 daga Ƙungiyar Global Initiative for Vaccine Equity, CanGIVE, don bunƙasa isar da allurar rigakafin COVID-19 da ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a ƙasar. Babban Kwamishinan Kanada, Amb. Jamie Christoff, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, yayin ƙaddamar da CanGIVE a Nijeriya. Ma’aikatar lafiya ta tarayya, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Ƙasa…
Read More
Cibiyar Kannywood Foundation ta taya jarumi El-Mustapha murna

Cibiyar Kannywood Foundation ta taya jarumi El-Mustapha murna

Daga WAKILINMU Cibiyar Kannywood Foundation ta yi taya murna ga jarumi Abba El-Mustapha naɗin da Gwamnan Kano ya yi masa kwanan nan. Gwamna Abba Kabira ya naɗa Abba El-Mustapha ne a matsayin Babban Sakataren Hukumar Tace Fina-finai da Ɗab'i ta Jihar Kano, wato KSCB. Cikin sanarwar da ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami'in hulɗa da jama'a na cibiyar, M.K Maikaba, cibiyar ta ce "Gaba ɗayanmu shugabani da 'ya'yan wannan cibiya na matuƙar farin cikin samun tabbacin wannan muhimmin labari. "Don haka muke yi wa Allah Mai Girma godiya, sannan muna son mu nuna wa Mai girma zaɓaɓɓen Gwamnan…
Read More
Jarumi Abba El-Mustapha ya zama Shugaban Hukumar Tace Finafinai

Jarumi Abba El-Mustapha ya zama Shugaban Hukumar Tace Finafinai

Daga AISHA ASAS Tun bayan sauya gwamnatin Jihar Kano, ake muhawara kan wanda za a ba wa ragamar shugabantar Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, lamarin da ya zama abin tattaunawa a shafukan sada zumunta. Duk da mutane da dama sun faɗi ra'ayinsu kan waɗanda suke hasashen za su iya ɗarewa kujerar shugabancin hukumar, kamar Sunusi Oscar 442, Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama, Salisu Muhammad Officer, sai dai da yawa sun aminta da cewa, a dukka mutanen da ake zayyanowa ba wanda ake hasashen zai iya danne fitaccen jarumi Abba El-Mustapha sakamakon irin rawar da ya taka a siyasar Kwankwasiyya da kuma…
Read More
Man fetur (1800-1950)

Man fetur (1800-1950)

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Masu hikima wajen sarrafa harshe da masu falsafar rayuwa sun fassara, kuma sun yi tambihin ma’anar kalmar tarihi daga dukkan abubuwan da suka faru a wannan doro na duniya na zahiri ga shi kan sa bil’adama tare da yanayin da yake ciki, aka kuma tattara shi aka adana, gudun kada ya salwanta, domin amfanin al'umami masu zuwa nan gaba. Tambayar a nan, mene ne man fetur? ’Yan kimiyya suka bayyana a matsayin man fetur ya zama gama gari kamar jamfa a Jos, waɗanne dalilai ne suka kai shi wannan matsayi? Domin sauƙaƙa bayani man fetur,…
Read More
Sojojin Isra’ila sun kai farmaki a yammacin gaɓar kogin Jordan

Sojojin Isra’ila sun kai farmaki a yammacin gaɓar kogin Jordan

Sojojin Isra'ila sun harbe wani Bafalasɗine har lahira tare da raunata aƙalla wasu mutum huɗu, biyu kuma na cikin mummunan hali a birnin Nablus da ke yammacin gavar kogin Jordan, kamar yadda ma'aikatar lafiya ta Falasɗinu da ƙungiyar agaji ta Red Crescent ta sanar. Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, ma'aikatar lafiya ta Falasɗinu ta ce an harbe wani mutum kafin wayewar garin jiya Alhamis, yayin da mayaƙan Falasɗinawa suka ce suna artabu da sojojin Isra'ila da mazauna yankin Nablus. Aƙalla Falasɗinawa huɗu ne suka samu raunuka sakamakon harbin bindiga, biyu kuma na cikin mawuyacin hali, inji…
Read More
Riyad Mahraz na daf da komawa Al Ahli ta Saudiyya

Riyad Mahraz na daf da komawa Al Ahli ta Saudiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Manchester city ta amince da tayin fan milyan 30 a kan ɗan wasanta Riyad Mahrez da ƙungiyar Al Ahli ta saudiyya ta yi. Ɗan wasan mai shekara 32 tuni city ta ba shi izinin ya zauna karya shiga tawagar ’yan wasan ƙungiyar da suke atisaye a nahiyar Asia. Yanzu haka ya rage ga Mahrez ya tattauna da Al Ahli akan batun albashin sa. Rahotanni sun kwarmata cewa tuni ya amince da kwantaragin shekaru uku a ƙungiyar dake birnin Jeddah. Shekaru biyu suka rage kwantaragin ɗan wasan ya ƙare a Etihad, sai dai…
Read More
Ban ci bashin Naira biliyan 10 na CCTV ba – Ganduje

Ban ci bashin Naira biliyan 10 na CCTV ba – Ganduje

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Tsohon Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya musanta zargin cin bashin N10 biliyan domin saka kyamarorin tsaro na CCTV a Birnin Kano da kewaye. Wani gungun 'yan gwagwarmaya ƙarƙashin inuwar Coalition of Political Analysts Forum and Good Governane ya nemi gwamantin Abba Kabir Yusuf ta binciki tsohon gwamna bisa abin da ya yi da kuɗin. Sai dai a martanin da ya fitar a Abuja, Dr Ganduje ya bayyana cewa bai samu zarafin karvo bashin ba saboda wata Kotun Tarayya dake Kano ta dakatar da shi bayan da Majalisar Dokoki ta amince masa. A…
Read More