Editor

9513 Posts
Amurka ta ƙi amince wa Falasɗinu zama mamba a Kwamitin Sulhun MƊD — Shawesh

Amurka ta ƙi amince wa Falasɗinu zama mamba a Kwamitin Sulhun MƊD — Shawesh

Daga BASHIR ISAH Ƙasar Falasɗinu ta bayyana cewa Amurka ta ƙi amince mata ta zama cikakkiyar mamba a Kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya. Jakadan Falasɗinu a Nijeriya, Abdullah M. Abu Shawesh, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar manema labarai da ya fitar mai ɗauke bayyanada kwanan wata 25 ga Afrilun 2024. Sanarwar ta ce sama da kwanaki 200 ke nan da fara kisan ƙare dangin da ake yi wa Falasɗinawa. A cewar Shawesh, "A ranar 19 ga Afrilu, Amurka ta ƙi amincewa da buƙatar Falasdinawa ga kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya na samun cikakken mamba da zama…
Read More
Ƙarancin Ruwan Sha: Gwamna Buni ya raba wa gidajen sayar da ruwa gas Kyauta

Ƙarancin Ruwan Sha: Gwamna Buni ya raba wa gidajen sayar da ruwa gas Kyauta

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu A ƙoƙarin nemo mafita dangane da matsalar ruwan sha a Damaturu, babban birnin jihar Yobe, da kewaye, Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya baiwa Ma'aikatar Albarkatun Ruwa ta jihar rabawa masu gidajen sayar da ruwa kyautar man gas, mako-mako, a Damaturu da kewaye. Da yake sanya ido dangane da aikin rarraba man gas din a ranar Litinin, Shugaban Hukumar kula da ruwa ta jihar (GM), Engr. Mahdi Zarma ya bayyana cewa wannan yunƙurin ya taimaka wajen rage wahalhalun ruwan tare da tsadar ruwan ga al'umma. “A kwanakin nan Gwamnati ta ƙara yawan man…
Read More
Yadda ruftawar bene ta kashe mutum uku a Kano

Yadda ruftawar bene ta kashe mutum uku a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Wani bene mai hawa biyu ya ruguje ana tsaka da aikinsa a Unguwar Kuntau daura da Kantin M D light, Kano. Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a ranar Juma'a inda ya rutsa da masu aikin ginin mutum 12. Muhammad Usman da aka fi sani da Sharu Mahi yana cikin leburorin da lamarin ya shafa, ya bayyana cewa yana hawa na biyu yana aiki sai ya fito sayayya kafin ya dawo ginin ya rubto. Ya ce, "Ni ina cikin ma'aikatan rake, kawai na fito saya ina sakkowa ina sakkowa ginin ya…
Read More
RSF ta tsananta hare-hare kan birnin al-Fashir na Arewacin Darfur

RSF ta tsananta hare-hare kan birnin al-Fashir na Arewacin Darfur

Sabbin hare-haren dakarun RSF kan birnin al-Fashir na arewacin Darfur ya sanya fargabar sake fantsamar yaƙin Sudan na fiye da shekara guda zuwa yankin wanda ke ɗauke da iyalai aƙalla miliyan 1600 da suka tserewa matsugunansu. Al-Fashir shi ke matsayin birni mafi girma da baya ƙarƙashin ikon RSF a yankin na yammacin Darfur, duk da yadda mayaƙan na RSF suka mamaye tare da ƙwace iko da dukkanin sauran sassan Darfur wanda ya kai ga zarginsu da aikataa kisan ƙabilanci kan tsirarun ƙabilun da ba Larabawa ba musamman a yammacin yankin. Dubban fararen hula ne da rikicin na fiye da shekara…
Read More
‘Yan bindiga sun hallaka kwamandan soji a Katsina

‘Yan bindiga sun hallaka kwamandan soji a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina 'Yan bindiga sun harbe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Ɗan Ali dake ƙaramar hukumar Ɗanmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan-ɓauna da aka kai musu. Majiyarmu ta bayyana cewa, ɓarayin sun yi wa babban jami'in sojin kwanton-ɓauna ne a ƙauyen Malali dake cikin ƙaramar hukumar Ƙanƙara, lokacin da yake tafiya cikin mota ƙirar Hilux don kai wa wasu sojoji ɗauki dake ƙoƙarin fatattakar 'yan bindigar da suka kawo hari a ƙauyen. "Kamar yadda ku ka sani Malali na kan hanyar Zangon Pawwa, kuma 'yan bindiga sun mamaye wannan wuri,…
Read More
Mutane da dama sun mutu, sama da motoci 70 sun ƙone sakamakon gobarar tankar mai a Ribas

Mutane da dama sun mutu, sama da motoci 70 sun ƙone sakamakon gobarar tankar mai a Ribas

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Ribas sun ce, mutane a dama sun ƙone ƙurmus kana motoci sama da 70 sun ƙone sakamakon fashewar wata tankar mai wadda ta kama da wuta na nan take a yankin Eleme, Jihar Ribas. MANHAJA ta kalato cewar lamarin ya auku ne a ranar Juma'a da daddare. Rahotanni sun ce motar ta kama da wuta ne alhali tana ɗauke da mai, lamarin da ya yi sanadiyar ƙonewar motoci masu yawan gaske da ke kusa da kuma haifar da tsaiko a kan hanyar da iftila'in ya auku. Duk da dai ba a tantance adadin mutanen…
Read More
Rundunar sojojin Isra’ila ta amince da murabus ɗin shugaban hukumar leƙen asirinta

Rundunar sojojin Isra’ila ta amince da murabus ɗin shugaban hukumar leƙen asirinta

Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Isra’ila Aharon Haliva ya yi murabus, sakamakon harin da ba a taɓa ganin irinsa ba da ƙungiyar Hamas ta kai wa ƙasar a ranar 7 ga watan Oktoba. Haliva ya kasance babban jami’in gwamnatin Isra’ila na farko da ya aje muƙaminsa tun bayan harin Hamas da ya hallaka mutane 120o, sannan ta yi garkuwa da wasu kusan 250 da har yanzu ba a kammala kuɓutar da su ba. Jim kadan bayan harin, tsohon shugaban hukumar leƙen asirin ya ce a ɗora masa laifin rashin daƙile harin da Hamas ta kai cikin ƙasar, don haka ya…
Read More
Zamfara: ‘Yan bindiga sun kai hari mahaifar ministan tsaro, sun yi awon gaba da mutane sama da 50

Zamfara: ‘Yan bindiga sun kai hari mahaifar ministan tsaro, sun yi awon gaba da mutane sama da 50

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu gungun 'yan ta'adda sun mamaye garin Maradun, hedikwatar ƙaramar hukumar Maradun kuma mahaifar ƙaramin ministan tsaro, Hon. Bello Muhammad Matawalle, inda suka yi garkuwa da mutane fiye da 50 galibinsu mata, a jihar Zamfara Wani mazaunin yankin, Malam Sulaiman Maradun, a wata tattaunawa ta wayar tarho ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin. A cewarsa, ‘yan bindigar sun yi wa garin ƙawanya da misalin ƙarfe 12:00 na tsakar daren ran Alhamis inda suka gudanar da harin nasu gida-gida. "Abin takaici ne yadda suka mamaye garinmu saboda sun zo da wasu manyan makamai masu kisa, suka…
Read More
Gwamna Abba Kabir ya ƙaddamar da aikin gadar sama da ƙasa ta Tal’udu

Gwamna Abba Kabir ya ƙaddamar da aikin gadar sama da ƙasa ta Tal’udu

Nan gaba kaɗan gadar Ɗan'agundi za ta biyo baya, inji gwamnan Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya ƙaddamar da aikin gadar ƙasa da sama da aka fara aikinta a ranar Asabar. Gwamnan ya bayyana cewa wannan aiki na da nasada da alqawarin da aka ɗaukar wa al'umma yayin da suke yawon yaƙin neman zaɓen shekarar 2023 da ya gabata. Maigirma gwamna Abba ya ƙara da cewa wannan aiki da zai gudana yana da nufin kawo sauƙi ga al'ummar ciki da wajen jihar musamman masu shigowa don gudanar da harkokin kasuwanci. "Kamar yadda muka…
Read More
Nijeriya ba ta shirya kafa ‘yan sandan jiha ba – Sufeto Janar

Nijeriya ba ta shirya kafa ‘yan sandan jiha ba – Sufeto Janar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sufeto Janar ɗin 'yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun ya bayyana cewa Nijeriya ba ta kai ga ta kafa 'yan sanda jiha ba wanda gwamnoni a jihohi ke da iko da. Egbetokun ya bayyana haka ne a ranar Litinin a taron tattaunawa kan kafa ‘yan sandan jiha wanda kwamitin majalisar wakilai kan duba kundin tsarin mulkin ƙasa ya shirya. Ya ce rundunar 'yan sandan ƙasa ba ta amince da hakan ba, amma kuma ta na rokon Majalisar Ƙasa ta duba yiwuwar ƙara kason 'yan sanda a kasafin kuɗin ƙasa. Ya kuma ce kafa ‘yan sandan…
Read More