ukarofi

11000 Posts
Gwamnatin Tinubu ta amsa tana biyan tallafin fetur

Gwamnatin Tinubu ta amsa tana biyan tallafin fetur

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bayan kwashe tsawon watanni ana musantawa, a ƙarshe Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta amince da cewa ƙasar da ta fi kowacce ƙasa haqo mai a nahiyar Afirka za ta ware har naira tiriliyan 5.4 domin tallafin man fetur a shekarar 2024.Wannan adadi ya qaru sosai daga Naira tiriliyan 3.6 da aka kashe a shekarar 2023 da kuma Naira tiriliyan 2.0 a shekarar 2022.An bayyana hakan ne a lokacin da Wala Edun, ministan kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin ƙasa ya gabatar da wani shiri na inganta zaman lafiya da cigaba…
Read More
Muna matuƙar godiya da goyon bayan da Gwamnatin Nijeriya ke bai wa Falasɗinawa – Falasɗinu

Muna matuƙar godiya da goyon bayan da Gwamnatin Nijeriya ke bai wa Falasɗinawa – Falasɗinu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jakadan Falasɗinu a Nijeriya, Abdul Abu Shawesh ya ce, a rana ta 243 da Isra'ila ta fara wa al'ummar Falasdinu kisan ƙare dangi, ina nuna matuƙar godiya da irin ɗimbin goyon bayan da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ke bai wa Falasɗinawa.Abu Shawesh ya bayyana hakan ne a ciki wata sanarwar da ya fitar a ranar Laraba.Ya ce; "A yau, zan fara da miƙa godiyata ga Tarayyar Nijeriya bisa tsayuwar daka wajen nuna goyon ƙudurin saka Falasɗinawa a Hukumar Lafiya ta Duniya da aka amince da shi a ranar Juma’ar da ta gabata.""Muna sa ran Nijeriya za…
Read More
Ma’aikaciyar jinya ta ɓace a Abuja bayan zuwa tashar Zuba

Ma’aikaciyar jinya ta ɓace a Abuja bayan zuwa tashar Zuba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata ma’aikaciyar jinya mai suna Lucy Likeh ta ɓace bayan zuwa tashar mota a babban birnin tarayya domin aika wa ƙawarta saƙo.’Yar shekaru 28 da haihuwa, an ce tana aiki da wata ƙungiya mai zaman kanta a MKK Plaza da ke Jabi, Abuja, an ce ta je wurin tashar na Zuba don aika wa ƙawarta saƙo zuwa Minna, Jihar Neja, ranar Juma’a.Bayan ta ziyarci tashar, ba a san inda ma’aikaciyar jinyar take ba, kuma wayarta a kashe.An ce tana sanye da baƙar wando da baƙar riga da hular feskaf lokacin da aka ganta na ƙarshe.Da yake…
Read More
An zargi Ministan Kimiyya da jabun takardun NYSC

An zargi Ministan Kimiyya da jabun takardun NYSC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ana zargin ministan Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Geoffrey Nnaji da laifin yin takardar bautar ƙasa (NYSC) ta jabu.Rahoton da Peoples Gazette ta fitar wanda ya bankaɗo wani aikin damfara da ministan ya yi ya kuma sanya hukumar tsaro ta farin kaya ta DSS cikin wani rufa-rufa mai ban mamaki.Ku tuna cewa an tabbatar da Geoffrey Nnaji a matsayin minista daga jihar Enugu a ranar 7 ga watan Agusta, 2023, tare da wasu mambobin majalisar ministoci 44, bayan naɗin da majalisar dattawa ta gabatar a ranar 7 ga Yuli, 2023.Daga nan aka naɗa shi…
Read More
Cire tallafin fetur: Gwamnatocin jihohi za su iya biyan mafi ƙarancin albashi, inji Falana

Cire tallafin fetur: Gwamnatocin jihohi za su iya biyan mafi ƙarancin albashi, inji Falana

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A yawan shiga yajin aikin ƙungiyoyin qwadago, Femi Falana (SAN) ya ce babu wata jiha da za ta ce ba za ta iya biyan mafi ƙarancin albashi ba biyo bayan cire tallafin da Gwamnatin Tarayya ta yi.Ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan Talabijin na Channels TV Brief, inda ya ƙara da cewa gwamnati ba za ta iya hana 'yan ƙwadago shiga yajin aiki ba."Babu wata jiha a Nijeriya a yau da ba za ta iya biyan fiye da mafi qarancin albashi ba saboda gwamnati ta cire tallafin man fetur a shekarar da ta…
Read More
CBN ya soke lasisin bankin Heritage

CBN ya soke lasisin bankin Heritage

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya, CBN, ya ce ya ƙwace lasisin gudanar da aiki na bankin Heritage da ke ƙasar.A cikin wata sanarwa da bankin ya fitar, ya ce ya ɗauki matakin ne "domin tabbatar da ingantaccen tsarin kuɗi a ƙasar, kuma ya yi hakan ne a ƙarqashin sashe na 12 na dokar bankuna da sauran harkokin kuɗi (BOFIA) ta 2020". Babban Bankin ya ce, soke lasisin ya zama wajibi bayan da bankin na Heritage ya cigaba da saɓawa sashe na 12 (1) na BOFIA 2020 da gazawarsa wajen inganta ayyukansa na kuɗi inda yake haifar da babbar…
Read More
Ya manin Kirifto Karansi yake aiki?

Ya manin Kirifto Karansi yake aiki?

Daga ALIYU ƊAHIRU ALIYU Idan zan turo maka kuɗi ta banki zuwa asusun ajiyarka na banki ai bankin zai ɗauki ladan aiki ko? A ladan aikin nan za a ba wa ma'aikata albashi waɗanda su ne suka buga stamfi/tambari kuma suka danna kwamfuta har kuɗin ya isa. To kamar haka manin yake aiki a Kirifto Karansi amma ba sak ba.Asali shi manin yana nufin yadda mutane suke amfani da kwamfuta don tabbatar da duk wata "hada-hadar kuɗi" (cinikayya ko tafiyar sakonni) da yake "blockchain", wanda shi bulokcan (block da chain) na nufin gamayyar ma'adanai (decentralized databases) da suke haɗe da…
Read More
Alaƙar jinin al’ada da zamantakewar aure

Alaƙar jinin al’ada da zamantakewar aure

Daga AISHA ASAS Allah S.W.A ya faɗa a cikin littafi mai tsarki “Su na tambayar ka game da haila {al’ada} ka ce masu ƙazanta ne, su nisance mata har sai sun yi tsarki.” A wannan ayar mata suke fakewa su na haramta ko sumbatar mazajensu. A cewar su ko hannu ya haramta miji ya riƙe na matar sa har sai tayi tsarki. Uwar gida ki sani a lokacin da ki ke al’ada saduwa kawai aka haramta maku. Da yawa mazaje masu mata ɗaya sukan shiga mawuyacin hali a lokacin da matansu ke al’ada wanda kaɗan ne daga cikinsu ke iya…
Read More
Kotunan shari’ar Masarautar Kano za su zauna rana guda

Kotunan shari’ar Masarautar Kano za su zauna rana guda

Daga NASIR S. GWANGWAZO Daga dukkan alamu kotunan da ke sauraron taƙaddama kan gadon kagarar Masarautar Kano za su zauna a rana guda ne bayan da a jiya Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman ta sanya ranar 13 ga Yuni, 2024, a matsayin ranar da za ta yanke hukunci game da taƙaddama kan huruminta na sauraron shari’a kan masarautar. Wannan rana da Babbar Kotun Tarayya ta sanya ya zo daidai da ranar Babbar Kotun Jihar Kano a ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu ne a ranar 28 ga Mayu, 2024.Idan za a…
Read More
Babban Sakataren Ma’aikatar ƙasashen wajen ya musanta zargin cin zarafi

Babban Sakataren Ma’aikatar ƙasashen wajen ya musanta zargin cin zarafi

Babban Sakataren Ma'aikatar Ƙasashen waje ya musanta zargin cin zarafi da minista yayi masa a wata takarda da ministan ya aikewa shugabar ma'aikatan Najeriya ta hanyar lauyoyinsa. Wasu waɗanda suka nemi a ɓoye sunayensu sun shaida cewa wannan tuhumar kawai faɗa ne tsakanin Ministan da Babban sakataren. Kuma sun shaidawa jaridar PR Nigeria cewa zargin cin zarafin ba zai yiyu ya zama gaskiya ba. Wani cikin wanda ya nemi a sakaya sunan shi ya ce mataimakiyar Ministan ta nemi wasu alfarma ne wanda shi Babban sakataren ya hana wanda yake tunani shine sanadin yi masa wannan bita da ƙullin. Kamar…
Read More