14
Jun
Daga NASIR S. GWANGWAZO Daga dukkan yanayin babu alamun lalubo warware rikicin da ke addabar Masarautar Kano a nan kusa bisa la’akari yadda har yanzu kotu da jami’an tsaro ke cigaba da taka rawa a cikin lamarin.A jiya Alhamis ne Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ƙarƙashin jagorancin Alƙali Muhammad Liman ta yanke hukuncin cewa, ta na da hurumin sauraron ƙarar da aka kai gabanta kan tuɓaɓɓen Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, tsigaggen Sarkin Dawaki Babba, Alhaji Aminu Babban ɗan Agundi, ke ƙalubalantar sauke su.Jim kaɗan bayan hakan kuma, sai Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta sanar…
