Labarai

Kafafen yaɗa labaran Nijeriya sun ƙaddamar da cibiyar ƙorafe-ƙorafe

Kafafen yaɗa labaran Nijeriya sun ƙaddamar da cibiyar ƙorafe-ƙorafe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Litinin ne kafafen yaɗa labaran Nijeriya su ka ƙaddamar da kwamitin mutane tara na hukumar sauraron ƙorafe-ƙorafen Kafafen Yaɗa Labaran Ƙasa (NMCC), wadda aka fi sani da ‘National Ombudsman’. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Kabiru Yusuf, shugaban ƙungiyar ’yan jaridu ta ƙasa NPAN, kuma shugaban ƙungiyar ’yan jaridu ta Nijeriya NPO ya fitar. Yusuf ya ce, a cikin sanarwar da aka fitar ranar Juma’a a Legas, an zaɓo mambobin hukumar ne daga kafafen yaɗa labarai, malamai da ƙungiyoyin farar hula. Ya ce, matakin ya zama wajibi a yunƙurin da ake…
Read More
Ganduje ya naɗa Farfesa Jega a matsayin Shugaban Gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi

Ganduje ya naɗa Farfesa Jega a matsayin Shugaban Gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa tsohon shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zamanta ta Ƙasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, a matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwar Sa’adatu Rimi dake Kano. Hakan na cikin wata sanarwa ce da Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Kwamared Muhammad Garba ya fitar. Sanarwa ta ce Gwamna Ganduje ya kuma amince da naɗin Oba Dakta Sanata Moshood Olalekan Ishola Balogun na Aliiwo a matsayin Babban uba kuma shugaban Kwamitin Gudanarwar Jami’ar ta Sa’adatu Rimi. A cewar Muhammed Garba, sauran mambobin kwamitin gudanarwar Jami’ar sun haɗa da: Dakta Muhammad Adamu Kwankwaso,…
Read More
’Yan bindiga sun yi awon gaba da ɗalibai mata a Zamfara

’Yan bindiga sun yi awon gaba da ɗalibai mata a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu gungun ’yan ta'adda sun sace ɗalibai mata biyu na Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS) a Jihar Zamfara. An ruwaito cewa, lamarin ya faru ne da safiyar ranar Lahadi 2 Afirilu, 2023 lokacin da ’yan ta’addan suka farmaki ɗakin kwanan ɗaliban da ke Sabon-Gida. Rahotanni sun ce, ’yan matan da aka sacen sun haɗa da wata mai suna Maryam da kuma Zainab. ’Yan sanda sun tabbatar da faruwar lamarin, inda Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Mohammed Shehu ya tabbatar da faruwar lamarin, kuma ya bayyana yadda ya faru. A cewarsa, ’yan ta’addan sun mamaye ɗakin…
Read More
Gwamna Ganduje ya kafa kwamitin miƙa mulki mai mambobi 17

Gwamna Ganduje ya kafa kwamitin miƙa mulki mai mambobi 17

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano ta amince da kafa kwamitin miƙa mulki na mambobi 17 ga gwamnati mai jiran gado a jihar. Majalisar ta kuma amince da wani ƙaramin kwamiti mai mutum 100 wanda za a fitar da Kundin Tsarin Mulkin daga ma’aikatu da hukumomi daban-daban na jihar. Wannan na cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Malam Muhammad Garba ya sanar da hakan a ranar Lahadi a kano Ya ce kwamitin wanda ke ƙarƙashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Usman Alhaji, yana da mambobi da suka haɗa da…
Read More
NBC ta yanke wa Tashar Channels tarar N5m kan saɓa ƙa’idar aiki

NBC ta yanke wa Tashar Channels tarar N5m kan saɓa ƙa’idar aiki

Daga BASHIR ISAH Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabiji (NBC) ta ci Tshar Channels tarar Naira miliyan 5 saboda saɓa ƙa'idar aiki. NBS ta kama tashar da laifi ne yayin wani shirin da ta yi tare da ɗan takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa na Jam'iyyar Labour, Dr Datti Baba-Ahmed a ranar Karaba, 22 ga Maris. Tarar na ƙunshe ne cikin wasiƙar da hukumar ta aike wa Shugaban tashar ta Channels mai ɗauke da kwanan wata 27 ha Maris wadda Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya samu leƙawa a ranar Juma'a a Abuja. Darakta Janar na NBC, Balarabe Ilelah, shi…
Read More
Abba Kabir ya kafa Kwamitin Karɓar Mulki

Abba Kabir ya kafa Kwamitin Karɓar Mulki

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya kafa Kwamitin karɓar mulki daga Gwamna Ganduje. Hakan na cikin wata sanarwar da Kakakinsa Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar da yammacin ranar Jumu'a. Ga sunayen 'yan Kwamitin kamar haka: Sen. AB Baffa Bichi, PhDChairman Prof. Hafiz AbubakarMember Hon. Shehu Wada SagagiMember Hon. Umar Haruna DoguwaMember Hon. Ahmad Garba BichiMember Dr Ali Haruna MakodaMember Barr Maliki KuliyaMember Barr. Haruna Isa DederiMember Dr. Danyaro Ali YakasaiMember Engr. Muhammad DiggolMember Dr Ibrahim Jibrin ProvostMember Sheikh Aminu DaurawaMember Dr. Labaran Abubakar YusufMember Prof Sani Lawan MFashiMember Alh. Umar S. MinjibirMember Dr Danjuma MahmudMember Engr.…
Read More
Shugabancin Kano: Ba zan biya bashin da ban ci ba, cewar Gwamna mai jiran gado ga Gwamna mai barin gado

Shugabancin Kano: Ba zan biya bashin da ban ci ba, cewar Gwamna mai jiran gado ga Gwamna mai barin gado

Daga RABI'U SANUSI a Kano Zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana ƙin amincewarsa wajen biyan bashin da gwamnati Gwamna Abdullahi Ganduje ta ciyo bayan bayyana shi a matsayin wanda ya samu nasarar lashe zaɓen da aka gudanar a kwanan baya wnda Hukumar Zaɓe, INEC, ta tabbatar masa. Manhaja Blueprint ta rawaito cewar Abba Kabir, ya yi zargin gwamnatni mai barin gado ta ciyo basussuka da dama domin gadar wa gwamnati mai jiran gado. Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran zababben gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya miƙa wa…
Read More
Kotu ta haramta wa Ganduje kusantar Filin Wasan Golf na Kano

Kotu ta haramta wa Ganduje kusantar Filin Wasan Golf na Kano

Daga RABI'U SANUSI a Kano Wata Babbar Kotu da ke zamanta a Jihar Kano ta nuna wa Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje yatsa bisa yunƙurin da gwamnatinsa ke yi na ganin ta tsaga tare da cefanar da Filin Wasan Golf mallakar jihar. Manhaja Blueprint ta ruwaito cewa, Kotun ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Zuwaira Yusuf, ta buƙaci kada wani mai ruwa da tsakin da ya kusanci wannan fili har sai lokacin da Kotun ta ayyana a matsayin ranar da za a dawo don ci gaba da sauraron ƙarar, wato ranar 5 ga Yuni bayan kuma an rantsar da sabon gwamnan jihar.…
Read More
An kashe mata biyu a cibiyar addinin Musulunci a Lisbon

An kashe mata biyu a cibiyar addinin Musulunci a Lisbon

'Yan sanda sun ce wani mahari ya kashe wasu mata biyu, bayan da ya daɓa musu wuƙa a wata cibiyar addinin Musuluci a Birnin Lisbon na Ƙasar Portugal. An kai harin ne a cibiyar addinin Musulunci ta 'Ismaili Centre' da ke birnin. 'Yan sanda sun samu nasarar harbe maharin, wanda ke riqe da sharveviyar wuƙa a ƙafa, bayan da ya yi yunqurin guduwa. Kawo yanzu dai ba a san dalilin maharin na kashe matan ba. 'Yan sanda sun ce sun samu kiran waye inda aka shaida musu cewa, an ga maharin ya shiga cibiyar da misalin ƙarfe 11 na safe…
Read More
Mun gamsu da jagorancin shugabannin Kasuwar Mile-12 a Legas

Mun gamsu da jagorancin shugabannin Kasuwar Mile-12 a Legas

Daga DAUDA USMAN a Legas Wani ɗan kasuwar gwari dake Kasuwar Mile-12 a cikin garin Legas, Alhaji Auwalu na Ubanliba kuma mai bai wa shugaban kulawa da cigaban kasuwanci ɓangaren tumatiri shawara ta musamman, Alhaji Abdulgiyasu Sani Rano, ya bayyana cewar shi da sauran al'ummar kasuwar suna cigaba da gamsuwa tare da amincewa da jagorancin shuwagabanni kasuwar gaba ɗaya. Alhaji Auwalu na Ubanliba ya yi wannan tsokacin ne a kasuwar Mile-12 a lokacin da yake zantawa da Jaridar Manhaja a Legas dangane da harkokin kasuwancin tumatiri a kasuwar, inda na Ubanliba ya cigaba da cewa haqiqa Abdulgiyasu Sani Rano yana…
Read More