Labarai

Zaɓen gwamnoni: Sarkin Keffi ya yaba da isowar kayan zaɓe a kan kari

Zaɓen gwamnoni: Sarkin Keffi ya yaba da isowar kayan zaɓe a kan kari

Daga BASHIR ISAH Mai Martaba Sarkin Keffi, Dr Shehu Chindo Yamusa II, ya yaba da yadda tsarin zaɓen wannan karon ya kankama a kan kari. Basaraken ya nuna gamsuwarsa da yadda kayan zaɓen suka iso da wuri aka kuma tantance masu zaɓe a kan kari a zaɓen gwamnoni da majalisun jihohi a ranar Asabar. Sarkin ya bayyana gamsuwarsa ne yayin da yake zantawa da manema labarai a fadarsa jim kaɗan bayna kaɗa ƙuri’arsa a rumfar zaɓe mai lamba 009, Tudun Ƙofa Ward da ke Ƙaramar Hukumar Keffi, Jihar Nasarawa. Ya kaɗa ƙuri’ar tasa ce da misalin ƙarfe 8:42am, tare da…
Read More
Zaɓen gwamnoni: Shugaban Ƙasa mai jiran gado ya kaɗa ƙuri’arsa

Zaɓen gwamnoni: Shugaban Ƙasa mai jiran gado ya kaɗa ƙuri’arsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa mai jiran gado, Bola Tinubu, ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi da ke gudana a wannan Asabar. Kamfanin Dillancin Labarai, NAN, ya rawaito cewar Tinubu ya kaɗa ƙuri'arsa ne da misalin ƙarfe 9:35 na safe a Rumfar Zaɓe 085 a Gunduma 03, da ke Alausa, Ikeja, Jihar Legas. Bayanai sun ce ya yi zaɓen nasa ne cikin yanayi mai tsatssauran tsaro. Matarsa, Oluremi da Sarkin Kasuwa Legas, Cif Folashade Ojo, na daga cikin waɗanda suka take wa Tinubu baya zuwa rumfar zaɓe.
Read More
Rikici ya ɓarke a wurin zaɓe a Bayelsa

Rikici ya ɓarke a wurin zaɓe a Bayelsa

An samu aukuwar rikici a wasu mazaɓu a yankin Ogbia, Jihar Bayelsa a wannan Aasabar da ake gudanar da zaɓen gwamnoni da na'yan majalisun jihohi. Manhaja ta tattaro cewar kayan zaɓen da aka tanada wa gundumar Ogbia ta 2, 3, 4 da ta 5 a Ƙaramar Hukumar Ogbia ta jihar, an lalata su sannan aka yi awon gaba da su. Tuni Gwamnan Jihar, Douye Diri, ya yi tir da wannan ɗanyen aiki. Gwmnan ya yi kira ga Sufeto-Janar na 'Yan Sanda nmda ma Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar da su maido da zaman lumana a yankin.
Read More
‘Yan daba sun lalata kayan zaɓe a Taraba

‘Yan daba sun lalata kayan zaɓe a Taraba

Da safiyar Aasabar wasu 'yan daba suka tarwatsa kayan zaɓe a Gundumar Akati cikin Ƙaramar Hukumar Donga, Jihar Taraba. Bayanai daga yankin sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da jami'an INEC ke ƙoƙarin raba kayan zaɓe zuwa rumfunan zaɓen yankin. Wakilinmu ya ce tada ƙayar bayan ya yi sanadiyar jama'ar yankin kowa ya tsere don neman mafaka. Wani ganau, Jame Chimi, ya ce zuwan sojoji ne ya taimaka wajen lafar da ƙurar da 'yan dabar suka tayar.
Read More
‘Yan sanda sun cafke waɗanda ake zargi da kai wa tawagar Gwamnan Kaduna hari

‘Yan sanda sun cafke waɗanda ake zargi da kai wa tawagar Gwamnan Kaduna hari

Daga WAKILINMU Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta cafke wasu da ake zargin mabiya Shi’a ne da ake zargi da kai wa tawagar Gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, hari. Sanarwar da Kakin rundunar, DSP Mohammed Jalige, ya fitar ta ce jami’an da ke bai wa tawagar Gwamnan kariya ne suka tsaftace yankin Bakin Ruwa da ke Rigasa, Babban Hanyar Nnamdi Azikiwe bayan da mabiya Shi’a suka kai hari tare da hana wa jama’a zirga-zirga a yankin. Ya ce an kama ‘yan dabar ne yayin da suke takura wa mazauna yankin a daidai lokacin da tawagar gwamna ta isa yankin da misalin…
Read More
EFCC ta tura jam’ianta jihohi don sanya ido kan zaɓen gwamnoni

EFCC ta tura jam’ianta jihohi don sanya ido kan zaɓen gwamnoni

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa, EFCC, ta tura jami’anta zuwa jihohin da za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi domin sanya ido kan zaɓen ranar Asabar. Mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar ranar Juma’a. Ya ce, jami’an hukumar sun isa wuraren da aka tura su don sauke nauyin da aka ɗora musu. Majiyarmu ta ce jami’an da aka tura Jihar Neja ƙarƙashin jagorancin ACEII Mustapha Abubakar, sun isa jihar inda suka gana da Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, J.A Ogundele. Haka nan,…
Read More
APC na alfahari da ƙoƙarin Hon. Bamalum – Bukardima Lawan

APC na alfahari da ƙoƙarin Hon. Bamalum – Bukardima Lawan

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Bade a Jihar Yobe, Hon. Bukardima Lawan, ya ce jam'iyyar ta na alfahari da irin ƙwazon tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi da matashin ɗan siyasa kuma Mashawarci na Musamman ga Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, kan ilimi a matakin farko da na sakandire, Hon. Isa Bamalum Bashir. Shugaban jam'iyyar ya yi wannan furucin ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron ƙaddamar da tallafin atamfofi kyauta ga mata masu ƙaramin karfi, wanda Hon. Isa Bamalum Bashir ya gabatar a cikin Makaranar Sakandiren Jeka-ka-dawo dake Gashu'a a…
Read More
Zaɓe: Sojoji sun fara sintirin inganta tsaro a Jihar Borno

Zaɓe: Sojoji sun fara sintirin inganta tsaro a Jihar Borno

Daga SANI AHMAD GIWA Gabanin zaɓen gwamnoni da na 'yan majalisun jihohi, Dakarun Sashen na 1 na Operation Haɗin Kai sun fara sintiri na karfafa gwiwa a Jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Nijeriya. Dakarun tare da jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Borno da sauran jami’an tsaro sun gudanar da wani gagarumin bajekoli a kewayen babban birnin Maiduguri, domin kawar da fargaba, da ƙarfafa ƙwarin gwiwar ‘yan ƙasar da kuma nuna shirin sojoji domin zaɓen ranar Asabar. Babban kwamandan runduna ta 7 (GOC) da kuma Kwamanda ta 1 na Operation Haɗin Kai, Manjo Janar Waidi Shaibu ya umurci kwamandojin…
Read More
Zaɓen Gwamnoni: A jihohi 28 kaɗai za a fafata

Zaɓen Gwamnoni: A jihohi 28 kaɗai za a fafata

Daga BASHIR ISAH Jihohi 28 daga cikin 36 da Nijeriya ke da su ne za a gudanar da zaɓen gwamnoni ran Asabar, 18 ga Maris, 2023. Yayin da zaɓen gwamnonin ba zai gudana ba a wasu jihohi guda takwas da suka haɗa da Anambra, Bayelsa, Edo, Ekiti, Imo, Kogi, Osun da kuma Ondo, waɗanda sukan gudanar da nasu a lokuta na daban saboda hukuncin kotu da ya gitta. Jihohin da za su shaida zaɓen gwamnonin a wannan Asabar, sun haɗa da: Abia, Adamawa, Akwa Ibom, Bauchi, Binueai, Borno, Kuros Riba, Delta, Ebonyi, Enugu, Gombe, Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Kwara,…
Read More
Zan kafa gwamnatin nagarta da dacewa ba ta haɗin kan ƙasa ba – Tinubu

Zan kafa gwamnatin nagarta da dacewa ba ta haɗin kan ƙasa ba – Tinubu

Daga AMINA YUSUF ALI Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da suke a dukkan faɗin jam'iyyu mabanbanta da su ba da goyon baya ga gwamnatin da yake shirin kafawa a Nijeriya, yayin da ya bayyana cewa, ba zai yi kafa gwamnatin haɗin kan ƙasa ba idan aka rantsar da shi, sai dai ya amince zai tafiyar da gwamnati mai nagarta. Tinubu ya ƙara da cewa, a yayin da zai zaɓi masu taimaka masa a fadarsa ta shugabancin ƙasa, zai zaɓa ne bisa la'akari da cancanta da dacewa. Wannan jawabi yana ƙunshe ne a…
Read More