Labarai

PDP a Jihar Benue ta dakatar da Shugaban jam’iyyar na Ƙasa, Ayu saboda zagon ƙasa

PDP a Jihar Benue ta dakatar da Shugaban jam’iyyar na Ƙasa, Ayu saboda zagon ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA Rikicin cikin gidan jam'iyyar adawa ta PDP na cigaba da zafafa, yayin da Kwamitin Zartarwa na Jam’iyyar PDP a gundumar Igyorov da ke ƙaramar hukumar Gboko ta Jihar Benue ya dakatar da Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa Iyorchia Ayu nan take. Jaridar News Point Nigeria ta rawaito cewa sun dakatar da Ayu ne saboda nuna adawa da jam'iyyar bayan sun kaɗa masa ƙuri'a. A lokacin da yake karanta wani ƙudiri, Sakataren jam’iyyar a gundumar Igyorov, Banger Dooyum, ya ce zagon ƙasa da Ayu tare da abokansa suka yi wa jam'iyyar ya taimaka wajen rashin yin nasarar Jam’iyyar…
Read More
PDP da LP suna shirya manaƙisa don hana rantsar da ni a matsayin shugaban ƙasa – Tinubu

PDP da LP suna shirya manaƙisa don hana rantsar da ni a matsayin shugaban ƙasa – Tinubu

Daga AMINA YUSUF ALI Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya kwarmata irin makircin da ya ce wasu fusatattun 'yan siyasa suke shirya masa don kawo cikas ga rantsar da shi a matsayin sabon shugaban Nijeriya a ranar 29 ga Mayun 2023. Tinubu ya yi wannan ikirarin ne a wani jawabi da Daraktansa na hulɗa da jama'a kuma Ministan ƙwadago da ba da aiki Mista Festus Keyamo SAN ya wallafa ranar Asabar 25 ga watan Maris, 2023, a Abuja. Jawabin ya yi gargaɗi ga 'yan takarar shugabancin Nijeriya na jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, da na jam'iyyar LP,…
Read More
DSS ta gargaɗi masu neman dagula zaman lafiya a ƙasa

DSS ta gargaɗi masu neman dagula zaman lafiya a ƙasa

Daga BASHIR ISAH Hukumar tsaro ta DSS ta yi zargin cewar akwai wasu da ke ƙoƙarin haddasa fitina don wargaza zaman lafiya a faɗin ƙasa. Da wannan DSS ta hanzarta gargaɗin masu hannu cikin wannan mummunan ƙuduri da su janye ƙudurin nasu ko kuma su fuskanci fushin dokokin Nijeriya. Gargaɗin na DSS na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da ta fitar ta ofishin Jami'in Yaɗa Labarai na DSS, Dr Peter Afunanya. A cewar sanarwar, “Hukumar na gargaɗin waɗanda suka zaƙu don tada zaune tsaye a ƙasa da su janye aniyarsu. “Ya isa shaida ganin yadda wasu fusatattun 'yan siyasa da…
Read More
Marafan Kaiama, Idris Muhammad ya rasu

Marafan Kaiama, Idris Muhammad ya rasu

Daga WANILINMU Allah Ya yi wa Marafan Kaiama a Jihar Kwara, Alhaji Idris Muhammad Madugu, rasuwa. Ya rasu ne a ranar Lahadi bayan fama da rashin lafiya. Salihu Ɗantata shi ne ya ba da sanarwar rasuwar a shafinsa na Facebook. A halin rayuwarsa, marigayin tsohon ma'aikaci ne ƙarƙashin Gwamnatin Jihar Kwara, kafin daga baya ya yi titaya.
Read More
Batun zubar da ciki: Babban Hafsan sojoji ya ƙaryata jaridar Reuters, ya ƙalubalance ta ta kawo hujja

Batun zubar da ciki: Babban Hafsan sojoji ya ƙaryata jaridar Reuters, ya ƙalubalance ta ta kawo hujja

Daga AMINA YUSUF ALI Babban Hafsan Rundunar Sojin Nijeriya (COAS) Laftana Janar Farouk Yahaya ya ƙalubalanci jaridar Reuters ta ba da hujja a kan rahoton da ta take yaɗawa wanda a ciki take ikirarin cewa, an gudanar da zubar da ciki har guda 10,000, an yi kisan kiyashi na yara da dama da yake da alaƙa da cin zarafin jinsi ta hanyar jima'i da suka danganta shi da hukumar sojin Nijeriya. Rahotanni sun bayyana cewa, COAS ya zo da ƙalubalen ne a yayin da yake ba da bayanin a gaban wani Kwamiti na musamman na Hukumar hana cin zarafin ɗan'adam…
Read More
INEC ta saka ranar bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni da ‘yan majalisun jiha takardar shaidar cin zaɓe

INEC ta saka ranar bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni da ‘yan majalisun jiha takardar shaidar cin zaɓe

Daga SANI AHMAD GIWA Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Nijeriya, INEC, ta ce ta saka ranakun da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun gwamnoni a jihohin ƙasar da aka gudanar da zaɓen gwamna. A wata sanarwar da hukumar INEC ɗin ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa ƙuri'a na hukumar, Festus Okoye, ta ce sashe na 72 (1) na Dokar Zaɓen ƙasar ta 2022, ya ɗora wa hukumar alhakin bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun 'yan takara a cikin kwana 14 da yin zaɓen.…
Read More
Oladipo Diya ya rasu yana da shekara 79

Oladipo Diya ya rasu yana da shekara 79

Daga BASHIR ISAH Tsohon Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa a gwamnatin marigayi Sani Abacha, Lt-General Donaldson Oladipo Diya, ya riga mu gidan gaskiya yana da shekara 79. Ɗan marigayin, Prince Oyesinmilola Diya, shi ne ya ba da sanarwar rassuwar mahaifin nasa cikin sanarwar da ya fitar da safiyar ranar Lahadi. Sanarwar ta ce, “A madadin ahalin Diya na gida da waje, muna sanar da rasuwar maigidanmu, mahaifinmu, kakanmu, ɗan uwanmu, wato Lt- General Donaldson Oladipo Oyeyinka Diya (mai murabus) GCON, LLB, BL, PSC, FSS, mni." Marigayi Oladipo diya Sanarwar ta nuna marigayin ya cika ne ranar Lahadi, inda iyalansa suka…
Read More
Duniya na fuskantar barazanar ƙarancin ruwa – MƊD

Duniya na fuskantar barazanar ƙarancin ruwa – MƊD

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi gargaɗin cewa duniya na cikin barazanar fuskantar ƙarancin ruwan sha saboda amfani da buƙatar ruwa sosai da ake da ita ga kuma matsalar sauyin yanayi. "Duniya na cikin matsalar faɗa wa mawuyacin hali saboda yawan amfani da ruwa,'' inji rahoton. Wallafa rahoton na zuwa ne gabanin taron MƊD na farko kan ruwa tun 1977. Dubban wakilai ne daga sassan duniya za su halarci taron ƙolin na kwanaki uku da za a yi a birnin New York daga ranar Laraba. Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya ce…
Read More
Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari

Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari

Daga BAKURA MOHAMMED a Bauchi Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da buƙatar da tsohon shugaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar 'yan sandan Nijeriya Abba Kyari ya gabatar a gabanta, yana neman kotun ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi masa. Yayin zaman kotuna a ranar Laraba alƙalin kotun mai shari'a Emeka Nwite ya yi watsi da buƙatar Abba Kyari, yana mai cewa kotun na da hurumin sauraron ƙararrakin da suke da alaƙa da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi kamar yadda kundin tsarin mulki da dokar da ta kafa hukumar NDLEA suka ba ta dama. Abba…
Read More
Emefiele ya roƙi gafarar ‘yan Nijeriya kan matsalar hada-hadar kuɗi ta intanet

Emefiele ya roƙi gafarar ‘yan Nijeriya kan matsalar hada-hadar kuɗi ta intanet

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya nemi gafara kan 'yan Nijeriya kan qalubalen da aka fuskanta kan tsarin hada-hadar kuɗi ta intanet. Emefiele ya nemi gafarar ne a taron kwamitin tsarin kuɗi na MPC da aka gudanar a ranar Talata a Abuja, inda gwamnan ya aminta da cewa, an samu ƙalubalen wanda a yanzu an warware ƙalubalen. Da yake amsa tambayoyi akan abin da ya shafi bankuna ganin yadda wasu bankuna a ƙasar Amurka ke durƙushewa, gwamnan ya ce bankuna a ƙasar nan ba za su durƙushe ba kamar yadda aka samu…
Read More