Labarai

Keyamo ya yi ƙarar EFCC da ICPC a kotu, ya nemi su tuhumi Atiku

Keyamo ya yi ƙarar EFCC da ICPC a kotu, ya nemi su tuhumi Atiku

Daga AMINA YUSUF ALI Festus Keyamo, mai magana da yawun majalisar kamfe ta jam'iyyar APC, ya shigar da ƙara a kan hukumar hana cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC), yana neman kotu ta kama Atiku Abubakar, ɗan takarar jam'iyyar PDP na shugabancin Nijeriya. A cikin ƙarar, Festus Keyamo wanda lauya ne mai muƙamin SAN ya haɗa da dokar Hukumar daƙile laifukan cin hanci da makamantansu (ICPC) Hukumar kula da dokar ɗa'ar aiki (CCB) a cikin ƙarar, bayan wa'adin awoyi 72 da ya bayar sun cika. Keyamo, lauya mai muƙamin SAN, ya ba da…
Read More
‘Yan bindiga sun sace ɗaliban firame a Nasarawa

‘Yan bindiga sun sace ɗaliban firame a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun kai hari tare da yin awon gaba da ɗaliban da ba a tantance yawansu ba a wata makarantar firamare da ke ƙauyen Alwaza cikin Ƙaramar Hukumar Doma, Jihar Nasarawa. Jaridar Intelrigion ta rawaito maharan sun yi wa makarantar kwanton ɓauna ne a lokacin da yaran ke ƙoƙarin haɗuwa da safiyar Juma'a. Ya zuwa haɗa wannan rahoto, ba a kai ga sanin su wane ne maharan da kuma adadin yaran da suka sace ɗin ba. Da aka nemi jin ta bakinsa kan lamarin, mai magana da yawun 'yan sandan jihar,…
Read More
An kuɓutar da basaraken da aka yi garkuwa da shi a Filato

An kuɓutar da basaraken da aka yi garkuwa da shi a Filato

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Filato sun ce an kuɓutar da Sarkin Agwan Izere, Dr. Isaac Azi Waziri, wanda aka yi garkuwa da shi da sanyin safiyar Juma'a. Blueprint ta rawaito maharan sun yi garkuwa da basaraken ne a fadarsa da ke gundumar Shere a shiyyar Jos ta Gabas. Kakakin 'yan sandan Jihar Filato, DSP Alfred Alabo, ya tabbatar da kuɓutar da Sarkin. Haka nan, ya ce an cafke wasu mutum biyu da ake zargin masu garkuwa ne da mutane a yankin.
Read More
Jami’ar Kimiyyar Kiwon Lafiya ta Azare ta ɗauki ɗaliban farko guda 760

Jami’ar Kimiyyar Kiwon Lafiya ta Azare ta ɗauki ɗaliban farko guda 760

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Sabuwar Jami’ar Kimiyyar Ilimin Kiwon Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da take da mazauni a garin Azare cikin Jihar Bauchi ta ƙaddamar da ɗalibanta na farko guda 760 na zagon karatu na shekarun 2021/2022 da 2022/2023. Da yake yin matsakaicin jawabin fara karatun ɗaliban a garin Azare, muƙaddashin shugaban jami’ar, Farfesa Bala Mohammed Audu ya ce Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ne ya kafa jami’ar a watan Yuni na shekara ta 2021, kazalika an naɗa shugabanninta ne bada wani ɓata lokaci ba a ranar 27 ga watan Janairu na shekara ta 2022. “Yau muna yin jawabin fara…
Read More
Kotu ta yanke wa matashi sharar masallaci kan bai wa ɓarayi masauki

Kotu ta yanke wa matashi sharar masallaci kan bai wa ɓarayi masauki

Dag WAKILINMU Wata kotu mai zamanta a Dei-Dei, Abuja, ta yanke wa wani matashi mai suna Anas Ibrahim, hukuncin sharar masallaci na tsawon wata shida bayan kama shi da laifin bai wa ɓarayi masauki. Wani mai suna Ibrahim da ke kasuwar kayan gwari a Zuɓa ya amsa tuhumar cewa yana ɗaya daga wani gungun ɓarayi tare da roƙon kotu ta yi masa sassauci. Alƙalin kotun, Saminu Suleiman, ya bai wa mai laifin umarnin ya share Babban Masallacin Zuɓa na wata shida ko kuma ya biya tarar N20,000. Tun da farko, lauyan mai gabatar da ƙara, Chinedu Ogada, ya faɗa wa…
Read More
Zargin miliyan N99: Kotu ta ɗaure alƙali da mataimakansa a Kano

Zargin miliyan N99: Kotu ta ɗaure alƙali da mataimakansa a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kotun Majistare mai lamba 14 ta aike da wani alƙali da ma’aikatansa na Hukumar Shari’a kurkuku saboda zargin su da wawure Naira miliyan 99. Mai Shari’a Mustapha Sa’ad Datti ya aike da mutanen ne bisa zargin su da yin sama da faɗi da kuɗaɗen wasu marayu. Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano ce ta gurfanar da waɗanda ake zargin gaban kotun. Sani Ali, Sani Uba Ali, Bashir Baffa, Gazzali Wada na daga cikin waɗanda ake tuhuma. Sauran sun haɗa da Hadi Tijjani Mu’azu, Alkasim Abdullahi tare da Yusuf…
Read More
Yau Emefiele zai bayyana gaban kotu kan badaƙalar Dala miliyan 53

Yau Emefiele zai bayyana gaban kotu kan badaƙalar Dala miliyan 53

Daga WAKILINMU A wannan Larabar ake sa ran Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, zai bayyana a gaban Babbar Kotun Abuja dangane da shari'ar sama da Dalar Amurka miliyan 53 na kudaden ‘Paris Club’. A wata ƙara da aka shigar gaban kotun ranar 20 ga watan Oktoban 2022, Alkalin kotun, Mai Shari'a Inyang Ekwo ya bai wa Emefiele odar ya bayyana a gaban kotun ran 18 ga Janairu don sauraron shari'ar. Umarnin kotun ya biyo bayan ƙarar da lauya Joe Agi, ya shigar ne kan kamfanin Linas International Ltd da Ministar Kudi da CBN ta hannun lauyoyinsa, Isaac Ekpa…
Read More
Akwai masu fakewa da addini wajen cimma manufofinsu na siyasa – Buhari

Akwai masu fakewa da addini wajen cimma manufofinsu na siyasa – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya faɗa ranar Talata cewa, akwai masu fakewa da addini domin cimma manufofinsu a ɓangaren tattalin arziki da siyasa. Buhari ya ce akwai buƙatar ci gaba da bai wa fannin ilimi muhimmanci domin tafiya da galibin jama'a. Shugaban ya yi waɗannan kalaman ne a birnin Nouakchott, Mauritania, yayin da suke ganawa da Rashad Hussain, Jakadan Amurka kan 'yancin harkokin addini. Yayin tattaunawar tasu, Buhari ya tuno ganawarsa da tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump a fadar White House inda ya ce Trump ɗin ya tambaye shi kan cewa: “Me ya sa kake kashe Kiristoci…
Read More
CBN ya samar da katin ATM na bai ɗaya

CBN ya samar da katin ATM na bai ɗaya

Daga BASHIR ISAH A matsayin ɓangaren na ƙoƙarin da yake yi na inganta sha'anin hada-hadar kuɗi a ƙasar nan, Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya samar da katin cire kuɗi (ATM) na bai ɗaya. CBN ya ce da wannan sabon katin na ATM, za a sadar da ko asusuwa nawa mutum ke da su da katin ta yadda za a iya amfani da katin wajen cire kuɗi a na'urorin ATM a bankuna daban-daban da sauransu. Katin mai taken '1 BVN = 1 ATM CARD' in ji CBN, zai yi aiki ne a tsakanin bankunan da ke mabobi a tsarin mu'amalar bankuna,…
Read More
Emefiele ya koma bakin aiki bayan kammala hutu

Emefiele ya koma bakin aiki bayan kammala hutu

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya koma bakin aiki bayan kammala hutun da ya ɗauka. Sanarwar da CBN ya fitar ranar Litinin mai ɗauke da sa hannun Daraktan sadarwa na bankin, Osita Nwanisobi, ta ce a Disamban da ya shuɗe Emefiele ya ɗauki hutu. Kuma ya dawo bakin aiki da sabbin dabaru kafin taron farko na Kwamitin Dokar Kuɗi (MPC) wanda zai gudana ran 23 zuwa 24 ga Janairun 2023. Sanarwar ta ƙara da cewa, Emefiele na jaddada ƙoƙarinsa wajen aiwatar da ayyukan da suka rataya a kansa daidai da doka da kuma umarnin Shugaban…
Read More