Labarai

Buhari ya yi Allah wadai da kisan lauya Omobolanle Raheem a Legas

Buhari ya yi Allah wadai da kisan lauya Omobolanle Raheem a Legas

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya yi Allah wadai da kashe wata lauya da ’yan sanda suka yi a ranar Kirsimeti a Jihar Legas. Buhari ya ce, ya yi matuƙar kaɗuwa da kisan Omobolanle Raheem, tare da bai wa hukumaomin ‘yan sanda umarni kan ɗaukar matakin da ya dace a kan waɗanda suka yi aika-aikar. Shugaban ya ce, wannan manuniya ce kan yadda ake mu'amala da bindigogi ba yadda ya dace ba. Ya ƙara da cewa, faruwar al’amarin fargarwa ce ga hukumomi ciki har da hukumar ‘yan sanda kan aiwatar da tsare-tsaren da ake da su dangane da…
Read More
An sayar da tsohon wandon kan Naira miliyan 50

An sayar da tsohon wandon kan Naira miliyan 50

Wani mutumi ya lale maƙuden kuɗaɗe har Naira miliyan 50.78 ya saya wani wandon jins ɗin da aka zaƙulo a ƙasan teku. Wani wandon maza wanda aka gano ya kasance mafi tsufa da daɗewa kuma an yi gwanjonsa kan Dala 114,000 wanda ya yi daidai da Naira miliyan 50.7. Farin wandon an tsamo shi ne daga wani jirgin ruwa da ya nitse tun a shekarar 1857 a Arewacin Carolina. A yayin jawabi kan nasarar da aka samu wurin sayar da shi, Dake Dwight Manley, Manajan California Gold Marketing Group ya ce, “haƙo wannan wando da masu haƙo ma’adanai suka samu…
Read More
2023: Mutanen kirki kaɗai za ku zaɓa, Sarkin Musulmi ga ‘yan Nijeriya

2023: Mutanen kirki kaɗai za ku zaɓa, Sarkin Musulmi ga ‘yan Nijeriya

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su zaɓi mutane nagari masu kishin ƙasa a matsayin shugabanni a zaɓe mai zuwa. Ya bayyana haka ne a wajen bikin Saukar Karatun Alƙur'ani na mahadata 825 da Makarantar Hizburrahim gudanar cikin Ƙaramar Hukumar Funtuwa, Jihar Katsina. Basaraken ya ce, zaɓen 2023 ya ƙarto don haka akwai buƙatar jama'a su fito don su zaɓi nagartattun shugabanni waɗanda za su jagoranci ƙasa wajen ficewa daga halin da tale ciki. A cewarsa, "Yau ƙasarmu na neman wanda zai ceto ta daga mawuyacin halin…
Read More
Buhari ya taya Ganduje murnar cika shekara 73 da haihuwa

Buhari ya taya Ganduje murnar cika shekara 73 da haihuwa

Daga WAKILINMU Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya taya Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje murnar cika shekara 73 da haihuwa. Buhari ya yi hakan ne cikin sanarwar da ya fitar ta bakin mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu, ranar Asabar a Abuja. Ya kuma yaba wa Gwamnan bisa salon shugabancinsa da kuma ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi a Kano, tare da taya shi murnar zagayowar ranar haihuwarsa. Daga nan, ya yi kira ga Gandujen da ya ci gaba da bai wa walwalar talakawan jihar muhimmanci da bunƙasa jihar.
Read More
Kasafin 2023 ya samu tazgaro a Majalisar Dokoki

Kasafin 2023 ya samu tazgaro a Majalisar Dokoki

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A ranar Alhamis, Majalisar Dokoki ta Nijeriya ta gaza amincewa da kasafin kuɗi na 2023, kamar yadda ta tsara tun asali, sakamakon yadda ta ce, Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa mata kasafin cike da tazgaro. A jawabinsa yayin zaman majalisar, Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya ce, an tsara Majalisar Dattawan za ta amshi rahoton Kwamitin Majalisar Kan Ƙudirin Kasafin Kuɗi na 2023, amma hakan ya gagara. A cewarsa, “sakamakon wasu manyan ƙalubale da ake fuskanta, ba mu iya karvar rahoton kasafin na 2023 ba, kuma ba komai ya janyo hakan ba…
Read More
Nijeriya ta tafka asarar tiriliyan N64.3 a shekara huɗu – Bankin Duniya

Nijeriya ta tafka asarar tiriliyan N64.3 a shekara huɗu – Bankin Duniya

Daga WAKILINMU Bankin Duniya ya ce, Nijeriya ta tafka asarar kuɗi Dalar Amurka biliyan 144.1, kwatankwacin Naira tiriliyan 64.3. Bankin ya ce rashin iya tattalin harkar canji daga bagaren Babban Bankin Najeriya (CBN) ne ya janyo wa ƙasar wannan asara daga 2017 zuwa 2021. Ya ce yadda CBN ke tafiyar da harkokin canjinsa ya haifar da rarrabuwar ra’ayoyin masana tattalin arziki da masu sharhi kan lamurra. Bayanan da Bankin Duniyar ya wallafa a shafinsa na intanet sun rashin iya tafiyar da sha’nin canjin daga ɓangaren CBN hakan ya sa kasar ta tafka asarar Dalar Amurka biliyan 144.1 daga 2017 daga…
Read More
Kirsimeti: FRSC ta tura jami’ai 1,769 da motocin sintiri 35 a Kaduna

Kirsimeti: FRSC ta tura jami’ai 1,769 da motocin sintiri 35 a Kaduna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa FRSC, reshen Jihar Kaduna ta tura jami’ai aƙalla 1,769 da motoci 35 domin tabbatar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara ba tare da cikas ba a jihar. Muƙaddashin kwamandan sashin, Garba Lawal ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Kaduna. Lawal ya ce ma’aikata 1,769 da aka tura sun haɗa da jami’ai 290, da Marshals 979 da kuma jami'a na musamman guda 500. A cewarsa, an ɗauki matakin ne domin tabbatar da kiyaye doka a manyan titunan Kaduna, musamman a wannan bikin…
Read More
Kirsimeti: Gwamnati ta sake ayyana ranakun hutu

Kirsimeti: Gwamnati ta sake ayyana ranakun hutu

Daga WAKILINMU A karo na biyu, Gwamnatin Taraya ta sake sanar da ranakun hutun gama-gari albarkacin bukukuwan Kirsimeti da na Sabuwar Shekara. Gwamnatin ta ayyana ranar 26 da 27 ga Disamban 2022, da kuma 2 ga Janairun 2023 a matsayin ranakun hutu don bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara. Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ne ya sanar da hakan a madadin Gwamnati cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis. Ministan ya yi amfani da wannan dama wajen taya Kiristoci ’yan Nijeriya da sauran ‘yan kasa murnar wadannan bukukuwa. Haka nan, ya yi kira ga Kiristoci da su yi…
Read More
Ƙarshen maha’inta ya zo – Saƙon Buhari na Kirsimetinsa na ƙarshe a matsayin Shugaban Ƙasa

Ƙarshen maha’inta ya zo – Saƙon Buhari na Kirsimetinsa na ƙarshe a matsayin Shugaban Ƙasa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya bai wa 'yan Nijeriya tabbacin ƙarshen maha'intar ƙasa ya zo, sannan 'yan ƙasa za su ga alheri a 2023 da ma bayan nan. Buhari ya bayyana haka ne cikin saƙon taya murnar Kirsimetin 2022 da ya isar wa 'yan ƙasa. Ya ce, “Saƙona na ƙarshe ke nan game da Kirsimeti a matsayin Shugaban Ƙasa. Nan da makonni 22 wannan gwamnatin za ta miƙa wa ta gaba ragamar mulki. “Wannan wata dama ce da ya kamata mu nuna wa duniya cewa a shirye Nijeriya take ta ƙarfafa dimokuraɗiyyarta. “A ci gaba da raya…
Read More
EFCC ta farauto fiye da Naira Biliyan 201 na kuɗaɗen harajin ma’adanai daga kamfanoni

EFCC ta farauto fiye da Naira Biliyan 201 na kuɗaɗen harajin ma’adanai daga kamfanoni

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Hukumar Yaƙi da yi wa Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC), ta bayyana cewar ta farauto zunzurutun kuɗaɗe fiye da Naira biliyan 201 kuɗaɗen harajin ma’adanai daga kamfanonin man fetur da ya kamata su bai wa Hukumar Bunqasa Cigaban Yankin Neja Delta (NNDC) da suka yi wa Hukumar Daidata Ƙa’idojin Haƙo da Man Fetur (NUPRC) ƙurmusu. Shugaban hukumar ta EFCC, Abdulrasheed Bawa shi ne ya yi wannan furuci yayin da yake yin jawabin manema labarai a wani shirin faɗakarwa da tawagar manema labarai a fadar shugaban ƙasa ta shirya makon jiya. Ya ce daga cikin wannan adadi,…
Read More