Labarai

‘Yan bindiga sun buɗe wuta cikin wani masallaci a Katsina

‘Yan bindiga sun buɗe wuta cikin wani masallaci a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina 'Yan bindiga sun yi dirar mikiya a wani masallaci dake garin Maigamji a Ƙaramar Hukumar Funtua a dai-dai lokacin da ake gabatar da Sallar Issha'i. Wani mazaunin garin ya shaida wa majiyar Manhaja cewa, da zuwan ɓarayin ana tsaka da Sallah sai suka buɗe wuta inda nan take suka harbi mutane biyu ciki har da wanda rahotanni suka ce shi ne limamin dake jan Sallar. Wanda yanzu haka suna karɓar magani a babban asibitin garin funtua. Rahotannin dai sun bayyana cewar, maharan sun yi awon gaba da mutane da dama. Harin na zuwa ne bayan…
Read More
An cafke matar da ta jefa jaririnta cikin masai a Jigawa

An cafke matar da ta jefa jaririnta cikin masai a Jigawa

Daga ABUBAKAR M TAHEER Rundunar 'Yan Sanda ta Jihar Jigawa ta sanar da kama wata mata mai suna Balaraba Shehu bayan Jefa jaririn da ta haifa a masai da niyyar binne shi. Lamarin ya faru ne a ƙauyen Tsurma da ke Ƙaramar Hukumar Kiyawa, Jihar Jigawa, inda aka gano jaririn aka garzaya da shi Asibitin Dutse inda a nan aka tabbatar da mutuwarsa. Kakakin 'yan sandan jihar, DSP Shiisu Lawan Adam, shi ne ya sanar da hakan ga manema labarai. Ya ce, "Mun samu labarin jefar da jariri a masai inda jami'anmu suka garzaya domin bincike da kuma kama matar.…
Read More
Ƙungiyoyi sun yi ƙorafin an yi wa ƙananan yara 84,000 rijistar zaɓe a Filato

Ƙungiyoyi sun yi ƙorafin an yi wa ƙananan yara 84,000 rijistar zaɓe a Filato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gamayyar ƙungiyoyin farar hula CSOs, guda goma da ke aiki domin tabbatar da sahihin zaɓe a Nijeriya, sun buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta, INEC, da ta gaggauta yin bincike kan rijistar masu zaɓe a Jihar Filato. Ƙungiyar, a wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, ta ce ta gano sama da ƙananan yara dubu 84 da suka yi wa rijistar zabe a ƙananan hukumomi 17 da ke jihar. Vanguard ta rawaito cewa ƙungiyoyin lura cewa, INEC, bisa la'akari da sashe na 19 (1) na dokar zaɓe, 2022, ta wallafa rajistar masu…
Read More
Tsohon Shugaban Jami’ar Gusau, Farfesa Garba zai sha ɗaurin shekara 35

Tsohon Shugaban Jami’ar Gusau, Farfesa Garba zai sha ɗaurin shekara 35

Daga SUNUSI MUHAMMAD a Gusau Wata Babbar Kotun Tarayya dake zama a Abuja ta yanke wa tsohon Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau, Farfesa Magaji Garba, hukuncin ɗauri na tsawon shekara 35. Mai shari’a Maryam Hassan Aliyu, wadda ta yanke hukuncin ta ce an samu Farfesa Garba ne da laifuka biyar da suka jiɓanci amfani da ƙarya wajen karɓar kuɗi da kuma zamba. Hukumar EFCC ce ta gurfanar da tsohon shugaban jami’ar gaban kotu ranar 12 ga watan Oktoba tana zargin sa da tatsar kuɗi daga wani mutum bisa alƙawarin ba shi kwangilar katange jami’ar, wadda kuɗinta ya kai Naira…
Read More
Ɗalibi Aminu zai gana da Buhari bayan sako shi daga kurkuku

Ɗalibi Aminu zai gana da Buhari bayan sako shi daga kurkuku

Daga BASHIR ISAH An sako ɗalibin nan, Aminu Mohammed Adamu, wanda aka tsare tare da maka shi a kotu don ya soki matar Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari. Rahotannin da Manhaja ta samu sun nuna, Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari zai gana da Aminu kafin daga bisani a miƙa shi ga ‘yan uwansa. Idan dai ba a manta ba, kimanin makonni biyu da suka gabata jami’an tsaro suka damƙe ɗalibin inda suka ɗauke shi zuwa Abuja sakamakon sukar da ya yi wa Aisha Buhari a shafinsa na Tiwita, inda ya ce Aisha ta ci kuɗin talakawa ta yi ɓul-ɓul. A ranar Talatar…
Read More
INEC za ta fara raba Katin Zaɓe 12 ga Disamba

INEC za ta fara raba Katin Zaɓe 12 ga Disamba

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta ce, ta rarrabe tsarin karɓar Katin Zaɓe (PVC) zuwa matakin gundumomi daga ranar 6 ga Janairun 2023. Kazalika, hukumar ta ce daga ranar 12 ga Disamba, 2022 za ta soma raba wa waɗanda suka yi rajista Katin Zaɓe a dukkan ƙananan hukomimi 774 da ake da su a faɗin ƙasa. INEC ta bayyana hakan ne cikin sanarwar da ta fitar Juma’ar da ta gabata, inda ta ce an cimma matsayar haka ne a wajen taron da ta gudanar kwanan nan a Legas. Sanarwar wadda ta sami sa hannun…
Read More
Suturar mutum uku Aisha ke sakawa saboda ƙiba – Solomon Dalung

Suturar mutum uku Aisha ke sakawa saboda ƙiba – Solomon Dalung

Daga BASHIR ISAH Tsohon Ministan Matasa da Wasannin Motsa Jiki, Solomon Dalung, ya ce a halin yanzu, suturar da za ta wadaci mutum uku matar Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari ke sakawa saboda ƙiba. Dalung wanda ya riƙe muƙamin Minista a wa'adin farko na Shugaba Buhari, ya faɗi hakan ne a sa'ilin da yake tsokaci dangane da tsare ɗalibi Aminu Mohammed da aka yi don ya soki Aisha Buhari a kafar Tiwita. Ya bayyana hakan ne cikin wani bidiyo da aka yaɗa wanda jaridar Daily Nigeria ta samu gani. A cewar Ministan, babu abin da ɗalibin da aka kama ɗin ya…
Read More
Kwaleji ta haramta wa masu juna-biyu da raino shiga harabarta a Ibadan

Kwaleji ta haramta wa masu juna-biyu da raino shiga harabarta a Ibadan

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata Kwalejin Kimiyya da ke Ibadan ta haramta wa ɗalibai mata masu juna biyu da masu shayarwa kawo jarirai zuwa ajujuwa da ɗakunan kwanan ɗalibai. An bayyana hukuncin na kwalejin ne a cikin ƙa'idar ɗabi'a da majalisar gudanarwa ta sa hannu. Makarantar ta ce, za a dakatar da ɗaliban da ke tare da juna a bainar jama'a a harabar jami'ar har tsawon zango ɗaya. Adewole Soladoye, mai magana da yawun kwalejin, ya tabbatar da tsauraran ƙa'idojin. “Makarantar ba gidan jinya ba ce. Shin daidai ne a kawo jarirai a cikin ajujuwan lacca? Lallai abin shagaltuwa ne.…
Read More
Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai fara aiki ran Litinin, cewar Gwamnati

Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai fara aiki ran Litinin, cewar Gwamnati

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar jirgin ƙasan Abuja–Kaduna zai dawo da aiki ya zuwa ranar Litinin, 5 ga Disamba. Shugaban Hukumar Kula da Jiragen Ƙasa ta Nijeriya (NRC), Fidet Okhiria ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) hakan ranar Alhamis. Ya ce, yanzu an kammala duk wani shiri da ya kamata don jirgin ya dawo ya ci gaba da aiki. Sai dai Okhiria, ya shawarci masu sha'awar su bi jirgin da su sabunta manhajar sayen tikitin jirgin da ke wayoyinsu daga ranar 3 ga Disamba don cimma nasara. Ya ƙara da cewa, za a…
Read More
Azal: Boka ya bindige wanda ya zo neman maganin bindiga

Azal: Boka ya bindige wanda ya zo neman maganin bindiga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’Yan Sandan Jihar Enugu ta cafke wani boka da ya kashe wanda yazo wurinsa neman maganin harbin bindiga a lokacin da ya ke gwada maganin a kansa. Bokan ɗan asalin jihar yana ɗaya daga cikin mutane 17 da aka kama aka kuma gabatar da su bisa laifin haɗa baki, kisan kai, fashi da makami, kwace manyan motoci, garkuwa da mutane, da kuma mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba a ’yan kwanakin nan a jihar. An bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata, 29 ga watan Nuwamba, 2022, ta hannun jami’in…
Read More