Labarai

Dalilin da ya sa NBC ta garƙame wasu gidajen rediyo da talabijin a Nijeriya

Dalilin da ya sa NBC ta garƙame wasu gidajen rediyo da talabijin a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabin ta Ƙasa (NBC) ta ba da sanarwar rufe wasu tashoshin rediyo da talabijin a faɗin Nijeriya. Darakta Janar na hukumar, Balarabe Shehu ne ya ba da sanarwar rufe tashoshin, yana mai cewa an ɗauki matakin haka ne saboda ƙin sabunta lasisinsu da tashoshin suka yi. Shehu ya bai wa rassan hukumar a jihohi umarni kan su haɗa kai da hukumomin tsaro wajen tabbatar da kafofin da lamarin ya shafa sun daina aiki cikin sa'o'i 24 masu zuwa. Ya ƙara da cewa, gwamnati na bin tashoshin da abin ya shafa bashin…
Read More
2023: Babban Sufeton ‘Yan Sandan Nijeriya ya ƙaddamar da bai wa jami’ansa horo a Borno

2023: Babban Sufeton ‘Yan Sandan Nijeriya ya ƙaddamar da bai wa jami’ansa horo a Borno

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Maiduguri Babban Sufeto Janar na 'yan sandan Nijeriya, IGP Usman Alƙali ya ƙaddamar da horas da jami’an 'yan sanda, wanda ya ƙunshi samar da tsaro a lokutan manyan zaɓukan 2023 mai zuwa, wanda ya haɗa da wani taron bita ta hanyar haɗin gwiwa da masana da sauran ɓangarorin hukumomin tsaron a jihar Borno. Kamar yadda ajandar taron ta nuna, wannan wani ɓangare ne na shirye-shiryen da take aiwatarwa wajen tabbatar da ganin zaɓukan sun gudana cikin tsanaki, ba tare da samun wata tangarɗa ba a babban zaɓe mai zuwa. A makonnin da suka gabata ne Sufeto…
Read More
Iyaye da malamai sun shiga damuwa bayan da Gwamna Inuwa ya kulle wasu makarantun jinya a Gombe

Iyaye da malamai sun shiga damuwa bayan da Gwamna Inuwa ya kulle wasu makarantun jinya a Gombe

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Iyayen dubban ɗaliban makarantun koyon kiwon lafiya, wato Schools of Health a Jihar Gombe, yanzu haka, suna cikin wani hali na damuwa, biyo bayan rurrufe makarantun kusan 20 dake faɗin Jihar, waɗanda Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bada umarnin a rufesu tun watanni kusan huɗu da suka wuce. Binciken da muka gudunar ya nuna cewa, makarantun suna nan kango, cike da ƙwari da shara, a wasu ma, ko masu gadi babu, tunda duk ƙofofin shiga harabar makarantun a garƙame suke kam-kam, kulle da makullai. Ko me ya jawo dalilin rufe waɗannan makarantun masu muhimmanci ga…
Read More
Tubabbun mayaƙan Boko Haram sun gudanar da aikin share unguwanni a Maiduguri

Tubabbun mayaƙan Boko Haram sun gudanar da aikin share unguwanni a Maiduguri

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Maiduguri Wasu tubabbun mayaƙan Boko Haram sun gudanar shara da tsaftace birnin Maiduguri, a ranar Asabar a yunƙurin da gwamnati ke yi na al'umma su sake amincewa da su, don ci gaba da rayuwa kamar yadda aka saba. Cibiyar Cigaban Dimukuraɗiyya (CDC) tare da haɗin gwiwa da gwamnatin jihar Borno ne suka shirya aikin tsaftace muhalli da tubabbun mayaƙan suka aiwatar. Da yake bayanin maƙasudin aikin, Malam Mustafa, babban jami'in gudanar da bincike a cibyar, ya bayyana cewa an ɓullo da wannan mataki ne a matsayin wani ɓangare na shirin mayar da tubabbun cikin al'umma don…
Read More
Bashin da ake jibga wa Nijeriya ke jawo gwamnati neman sayar da kadarorinta – Ɗanpass

Bashin da ake jibga wa Nijeriya ke jawo gwamnati neman sayar da kadarorinta – Ɗanpass

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana cewa yawan basukan da gwamnatin Nijeriya ke yawan karɓowa daga ƙasashen waje na neman tilasta ƙasar cefar da wasu muhimman kadarorinta. Ɗan Saran Kano, Alhaji Gambo Ɗanpass shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano cikin makon nan. Ana raɗe-raɗin Gwamnatin Nijeriya da yiwuwar za ta cefanar da asibitocin Gwamnatin Tarayya ga 'yan kasuwa da sauran ma wasu kadarorin, wanda Ɗanpass ya bayyana hakan a matsayin illolin bashin da ƙasar ke karɓowa. Ya ce dama illar cin bashi kenan da zai kasance ƙasa za ta zama ba ta da 'yanci da…
Read More
Hana sana’ar acaɓa a Nijeriya: Gwamnati za ta rasa kuɗin shiga mai yawa

Hana sana’ar acaɓa a Nijeriya: Gwamnati za ta rasa kuɗin shiga mai yawa

Yayin da ta'addanci zai ƙaru, cewar Hajiya Hauwa Inuwa Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Hajiya Hauwa Muhammad Inuwa, tsohuwar 'yar takarar kujerar Sanatan Gombe ta Arewa a Jam'iyyar Accord ta ce tana mai kira ga gwamnati da ta janye ƙudurinta na hana sana'ar Acaɓa a Nijeriya domin kar a jefa mutane cikin ƙuncin rayuwa. Hajiya Hauwa Inuwa, ta bayyana hakan ne a lokacin da take zantawa da manema labarai a Gombe, inda ta ce masu sana'o'i daban-daban guda 7 ne suke cin abinci a dalilin babura: Akwai masu faci, masu sayar da baƙin mai da makanikai da masu wanki…
Read More
Mun fatattaki muggan ɓarayi da ‘yan daba a garin Tafa – Kwamanda Adam Omajudo

Mun fatattaki muggan ɓarayi da ‘yan daba a garin Tafa – Kwamanda Adam Omajudo

Daga MOHAMMED ALI a Tafa Shugaban Tsaro na Ƙungiyar 'Neighborhood Watch' da reshen PCRC ta rundunar 'yan sanda dake garin Tafa ta Ƙaramar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, Kwamanda Ambasada Adam Omajudo, ya yi iƙirarin cewa, ƙungiyarsa ce ta 'yan sa kai ta yaƙi wasu muggan ɓatagari da suka addabi al'umma tsawon shekaru, hoɓɓasar da ya ce ta sa aka samu kwanciyar hankali a garin. Da yake hira da wakilin mu a Tafa Litinin ɗin wannan makon, Kwamanda Adam ya ce, kafin kafa ƙungiyar ta su mai rassa a Chakwama, Dulu, Sisiya, 'Yan Goro, Dogon Ƙarfe, da Unguwar Gwari baya…
Read More
Ƙungiyar Matasan Nijeriya ta buƙaci a samar da hukumar daƙile tashe-tashen hankula da rashin aikin yi a Borno

Ƙungiyar Matasan Nijeriya ta buƙaci a samar da hukumar daƙile tashe-tashen hankula da rashin aikin yi a Borno

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Maiduguri Ƙungiyar matasan Nijeriya (NYCN), reshen jihar Borno ta nemi gwamnatin jihar ta kafa hukumar da za ta magance tashe-tashen hankula da rashin aikin yi a tsakanin matasan jihar. Majalisar matasan ta bayyana cewa kusan dukan laifukan da ake aikatawa akwai zargin matasa ne masu aikata su, waɗanda ƙasar nan ke fama da tashe-tashen hankula, ta ƙara da cewa, duk da cewa matasa suna da hannu wajen samar da zaman lafiya a cikin al’umma. Wannan furucin ya fito ne daga shugaban ƙungiyar NYCN a jihar Borno, Kwamared Tanimu Tahir, a lokacin bikin ranar matasa, wadda Majalisar…
Read More
Ranar Matasa 2022: Atiku ya buƙaci ilimi ya zama haƙƙi ga matasan Nijeriya

Ranar Matasa 2022: Atiku ya buƙaci ilimi ya zama haƙƙi ga matasan Nijeriya

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Matasan Jam'iyyar PDP sun gudanar da bikin ranar matasa ta duniya 12 ga Agustan 2022 a Abuja, yayin wani ƙayataccen taro da ya samu halartar manyan jiga-jigan jam'iyyar daga sassan ƙasar nan ciki har da ɗan takarar shugabancin ƙasar nan na Jam'iyyar PDP a zaven baɗi Atiku Abubakar da Shugaban Jam'iyyar na Ƙasa Dr. Iyorchia Ayu da sauran shugabanni. A jawabinsa na buɗe taron, shugaban matasa na Jam'iyyar ta PDP Prince Muhammad Kadaɗe Sulaiman ya ce manufar taron mai taken: 'Haɗin gwiwar gudanar da shugabanci tare da mtasa na cikin muradun cigaba mai ɗorewa na…
Read More
Asibitin Aminu Kano zai fara dashen ɓargo – Mahukunta asibitin

Asibitin Aminu Kano zai fara dashen ɓargo – Mahukunta asibitin

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, AKTH, da ke Kano, a ranar Litinin ya ƙaddamar da wani sabon sashin kula da cututtukan jini kuma hakan ya nuna cewa za a fara dashen ƙargo a cibiyar. AKTH zai kasance asibitin koyarwa na biyu a Nijeriya da zai riƙa yin dashen ɓargo a ƙasar. Babban Daraktan Asibitin, Farfesa Abba Sheshe ne ya bayyana haka a wurin ƙaddamar da cibiyar a hukumance, wanda wani Injiniya Umar lbrahim ya bada ita a matsayin gudunmawa. Ya bayyana cewa asibitin koyarwa na jami’ar jihar Legas ne kaɗai ya yi nasarar dashen ɓargo…
Read More