Ra’ayi

’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

Daga IBRAHIM SHEME Kwanan nan Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i, ya jawo wata muhawara a kan batun a yafe wa ‘yan bindiga ko a kashe su idan an gan su. Matsayar sa ita ce kada a yi wani zaman tattaunawa da su don a samu hanyar da za a warware ibtila’in kashe-kashe da ke faruwa a yankin Arewa-maso-yamma na ƙasar nan. Gara a nuna masu ƙarfin soja, a murƙushe su, babu sassautawa ko jinƙai. A wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon BBC, El-Rufa’i ya bayyana cewa duk wata hanyar lalama da za a bi…
Read More
Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Daga TIJJANI SARKI  A 'yan makonnin nan an sami tashin tashina a wanin ɓangare na jihohin kudancin ƙasar nan, har inda wani gwamna ya ke ba da sanarwar korar ƙabilar Fulani makiyaya daga faɗin jihar sa, abin har ya kai da ƙona musu gidaje da masallaci  duk dai bisa dogaro da su ba 'yan jihar ba ne. Kuma suna kawo yamutsi a jihar, kodayake mun jiyo Gwamnan Jihar Ogun na cewa suna zaman lafiya da Fulani sama da shekaru ɗari a jiharsa. Zai yi kyau mu ɗan yi waiwaye akan ƙabilar Fulani makiyaya wanda suke da ɗumbin yawa musamman a…
Read More
Toshe hanyar abinci a matsayin makami

Toshe hanyar abinci a matsayin makami

Daga IBRAHIM SHEME Toshe wa mutane hanyar da abinci zai isa gare su wani makami ne da ake amfani da shi a lokacin yaƙi. An yi amfani da shi a lokacin Yaƙin Basasar Nijeriya, wato Yaƙin Biyafra. Manufar wannan matakin ita ce a karya lagon abokan gaba, a rage masu ƙarfi, kuma a tilasta masu su aje makaman su. To amma Majalisar Ɗinkin Duniya ta haramta ɗaukar irin wannan matakin a kan farar hula. Duk wanda aka kama ya yi hakan, ya aikata babban laifi; ana iya gurfanar da shi a Kotun Miyagun Ayyuka ta Duniya (ICC). Sashe na  8(2)(b)(xxv)…
Read More
Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Kwanan nan ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kaɗa hantar wasu ‘yan Nijeriya lokacin da ya tunatar da bankuna da sauran hukumomin da ke kula da hadahadar kuɗi cewa dokar nan da ta haramta amfani da kuɗin intanet, wato kuɗin kirifto (cryto currency), ta na nan daram. Karo na uku kenan a cikin shekara biyar da babban bankin ya yi magana kan harka da irin wannan kuɗi da ake ganin ta na tattare da babban ganganci a cikin ta. Sakamakon hakan, bankuna sun shiga soke duk wani asusu da aka buɗe da sunan yin harka da irin wannan kuɗin. Majalisar…
Read More
Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Daga FARFESA UMAR LABDO ShimfiɗaIna yin wannan rubutu a matsayina na Babban Sakataren ƙungiyar FULDAN na ƙasa. FULDAN (Fulani Development Association of Nigeria) ƙungiya ce mai fafutuka don ci gaban Fulani a fagagen ilmi, al'adu, tattalin arziki da zamantakewa. An kafa ta a shekarar 1999, tana da wakilci a yawancin jihohin ƙasar nan kuma tana da alaƙa da ƙungiyoyi takwarorinta a ƙasashe makota. Ƙungiyar tana shirya tarukan wayar da kan Fulani da koya musu sana'o'i da sabbin dabarun kiwo don inganta sana'arsu. Haka nan tana gudanar da azuzuwan yaƙi da jahilci da koyon addini a rugage da ƙauyukan Fulani. GabatarwaAl'ummar…
Read More
Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Daga IBRAHIM SHEME A ranar Litinin da ta gabata, sabon shugaban Hukumar Yaƙi da Safara da Shan Muggan Ƙwayoyi (NDLEA), Janar Mohammed Buba Marwa (ritaya), ya yi wata magana wadda ya kamata ta farkar da duk ɗan Nijeriya game da matsalar da fataucin muggan ƙwayoyi ke janyo wa ƙasar nan. Cewa ya yi kashi 90 cikin ɗari na muggan laifukan da ake aikatawa a Nijeriya, sakamakon ɗirkar muggan ƙwayoyi da wasun mu ke yi ne. A cewar sa, laifuka irin su hare-haren ‘yan bindiga, ta’adda, satar mutane, fyaɗe da sauran su duk ‘yan ƙwaya ne ke aikata su. Marwa, wanda…
Read More
Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Labarin da aka bayar cewa Gwamnatin Tarayya na shirin bada tallafin sama da naira biliyan 600 don agaza wa manoma abin farin ciki ne. Ba shakka, abin da ya dace ne idan har ana so a faɗaɗa hanyoyin inganta tattalin arzikin ƙasar nan, wanda ya shafe sama da shekara hamsin ya na dogaro da man fetur wajen samun kuɗaɗen shiga. Ministan Aikin Gona Da Raya Yankunan Karkara, Alhaji Sabo Nanono, shi ne ya bayyana labarin a cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na ma’aikatar sa, Mista Theodore Ogaziechi, ya rattaba wa hannu kwanan nan a Abuja. A sanarwar, an…
Read More
Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Daga IBRAHIM SHEME Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware ranar 4 ga Fabrairu ta kowace shekara a matsayin Ranar Yaƙi Da Cutar Daji ta Duniya, wato a turance 'World Cancer Day'. Muhimmancin ranar shi ne mutane su tuna da irin ɓarnar da cutar ke yi da matakan da ya kamata a ɗauka don rigakafi da kuma hanyoyin magance ta. A jiya Alhamis ne wannan rana ta kama a bana. Abin mamaki, ban ji inda aka yi wata yekuwa ko gangami don tunawa da ranar ba a jiya. Akwai 'yan labarurruka da ƙungiyoyi masu yaƙi da cutar su ka ɗan yaɗa, su…
Read More

Sababbin hafsoshin Buhari

An daɗe ana kira da roƙo ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya sauya manyan hafsoshin sojan ƙasar nan masu jagorancin rundunonin tsaro, amma ya na ƙi. Sai da ta kai Majalisar Tarayya ta zartar da ƙudirori a kan lallai ne Shugaban ya kori hafsoshin, amma dai maganar ta wuce ta bayan kunnen sa. Dalilai biyu su ka sanya aka riƙa yi masa wannan kiran. Na farko shi ne, wa’adin hafsoshin ya wuce, har ma ana ganin sun fara cin wa’adin wasu hafsoshin domin tun a cikin 2015 aka naɗa su. Dalili na biyu kuma shi ne gazawar da ake ganin…
Read More
Shin in Fulani makiyaya su ka fice daga Ondo salama ta samu?

Shin in Fulani makiyaya su ka fice daga Ondo salama ta samu?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Wa’adin da Gwamnan Ondo Rotimi Akeredolu, ya bai wa Fulani makiyaya su fice daga dazukan jihar sa, ya haddasa muhawara mai zafi tsakanin kudanci da arewacin Nijeriya. Muhawarar ta dogara ga yadda mai sharhi ko ra’ayi ya ke ganin abun. Ga masu ɗaukar makiyaya ko Fulani makiyaya cewa ’yan Arewa ne ko ma ’yan’uwan su ko ma a ce su na dangantaka da Musulunci ko da ma a iya samun mabiya adddinin Kirista a cikin su da waɗanda ba su san ko “Ba Sin Mi Ara Ba...” to, za su ɗauki wa’adin da Akeredolu ya ba…
Read More