Ra’ayi

Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Duk da matsayin da jihohin yankin Arewacin Nijeriya suka samu kawunan su a cikin shekaru 16 da su ka shuɗe har zuwa yanzu da gwamnatin APC ke mulkin ƙasar, alamuran yankin suka shiga taɓarɓarewa, harkar tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma ya kau, kusan kowane ƙauye su na fama da ruɗani masu garkuwa da mutane, don amsar kuɗin fansa, su na fama da hare-hare da rigingimun makiyaya. Gwamnonin da haƙƙin hakan kuma ya rataya a wuyan su ba su taɓuka ba, don ɗaukar wani mataki, walau na gaggawa ko wanda aka tsara na musamman, don magancewa. Haka nan su na ji,…
Read More
Wata Guguwa

Wata Guguwa

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM Bayan fargaba da asarar rayuka da dunkiyoyi da annobar kwarona ta haddasa, rayuwa ta fara dawowa daidai a wasu wurare da dama, harkoki sun fara komawa kamar yadda aka san su. Farkon ɓullar wannan cuta mutane da dama ba su ɗau abin da muhimmanci ba, tunanin kowa shine cutar za ta tsaya ne a iyakar inda ta ɓulla kamar yadda aka saba, abu kamar wasa sai ga ta ta game duniya gabaɗaya ta buwayi duniya har ta illata tattalin arzuƙin mutane da ƙasashe da dama musamman ƙasashe masu tasowa da kuma talakawanta. Har yanzu ba wai…
Read More
Wake ɗaya ɓata gari: Allah sarki ’yar jarida!!!

Wake ɗaya ɓata gari: Allah sarki ’yar jarida!!!

Daga KWAMRED IBRAHIM ABDU ZANGO Akwai wata ’yar jarida wacce ta koyi aikin jarida a wata kafa ta rediyo da wani hamshaƙin ɗan jarida ya koya mata, wato aikin jaridar rediyo. Kullum ka je za ka same ta a ƙasa, shi kuma yana kan kujera! Ya kan ba su damar hirar siyasa da irin ’yan siyasar baka ɗin nan. Ta haka waccan ’yar jarida ta koyi yadda ake hira ta cikin radiyo! Ni a tunanina gani nake cewa, a makaranta ake koyar da wannan babbar sana’a ta jarida tunda akwai fannin wani darasi da ake kira Maskom, wato ‘Mass Communication’.…
Read More
Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Tun lokacin zuwan gwamnatin wannan lokaci a shekara ta 2015 ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, ta karkata manufar tattalin arzikin Nijeriya kusan kacokan daga ɓangaren ɗanyen mai zuwa kan harkokin noma, inda gwamnatin ta buɗe wuta wajen ingaza dukkan wani sha’ani da yake da alaƙa da fannin noma ta fuskar ɗaukar matakai daban-daban. Gwamnatin Buhari ta samar da shirye-shirye da tsare-tsare kala-kala, domin cimma wannan buri kama daga ƙarfafa samar da rance mai sauƙi ga manoma zuwa ba su tallafin noma. Haka nan gwamnatin ta kuma tabbatar da rufe iyakokin qasar da hana shigo da shinkafa, wanda hakan ya bai…
Read More

Rundunar Ebube Agu ma ta fara cara!

Tawagar Gwamnonin Kudu-maso-gabas Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sabuwar rundunar ’yan banga da gwamnonin Kudu maso Gabashin Nijeriya suka kafa mai taken “Ebube Agu” da harshen Igbo ta fara cara, saboda jagororin kafa ta na da babban muradin farko na hana kiwo a fili, kamar yadda Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Otom, ya zartar, duk da cewa shi ɗan mabilar Tibi ne kuma daga Arewacin Nijeriya. A lokacin da na ga labarin gagarumin tsaron gwamnonin na Igbo a garin Owerri, sai na tuno da kafa irin wannan runduna da tun farko gwamnonin yankin Yarabawa suka yi mai taken “Amotekun” da muradin hana kiwon…
Read More
Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

A kwanan nan ne jami’an tsaro na Jamhuriyar Nijer suka damƙe wasu muggan makamai da ake yunƙurin shiga da su Nijeriya, don kai su Maiduguri, babban birnin jihar Borno, inda aka fi fama da balahirar yaƙin Boko Haram. Jami’an qasar Nijer ɗin ne suka bayyana hakan, inda suka ce sun kama wata mota ƙirar Toyota Hilux danlare da muggana makaman da suka haɗa da harsashi da bindigogi ƙirar AK-47, inda aka cafke su a Agadez bayan sun tsallako daga kan iyakar Ƙasar Libya da nufin tunkrar Nijeriya, domin kai su. Sashen tsaro na Birnin Agadez da ke Nijer shine ya…
Read More
Biafara na barazana ga Wazobia

Biafara na barazana ga Wazobia

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Kawo ƙarshen yaƙin basasar Nijeriya a 1970 bai zama ƙarshen muradin masu son raba Nijeriya don neman kafa ƙasar Biafara ta ƙabilar Igbo a Kudu maso gabashin Nijeriya ba. Wannan ya nuna dakarun Nijeriya sun ci nasarar wargaza ɗamarar yaƙin ’yan Biafara ne amma waɗannan masu son kafa ƙasar ’yan aware na nan da muradin su. Da alamu su kan ma gadar da muradin ga ’ya'yan su ko da bayan sun mutu masu tasowa su ɗora daga inda suka tsaya har sai sun cimma muradin nasu. Ɓullowar ƙungiyar IPOB ta Nnamdi Kanu ta zama sabuwar tafiya…
Read More
Ilimin ‘ya’ya mata a zamanin da ke wanzuwa

Ilimin ‘ya’ya mata a zamanin da ke wanzuwa

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM A tarihin duniya mata na da wani irin tasiri da muhimanci a rayuwa kasancewarsu iyaye mata ko matan aure, ko ‘ya’ya mata ko kuma dai a taƙaice iyayen al’umma. Gudunmawar mata a cikin al’umma na da dumbin yawan gaske saboda waxan can dalilan da na ambata a sama. Ta hanyar auratayya da su ake haɗa nasaba mai kyau ake kuma faɗaɗa nasabar nan zuwa inda ma ba zata ba. Gudunmawar mata ga cigaban al’umma yana da faɗin gaske kama tun daga lokacin Annabawa zuwa yanzu. A dalilin haka ne ya kyautu a baiwa mace duk wani…
Read More

Shaikh Zakzaky a shekaru 70 masu albarka

Shaikh Zakzaky Daga NAJEEB MAIGATARI A shekarar 2009 an gayyaci Chimamanda Ngozi Ndichie zuwa wani taro da ‘TED talk’ ta shirya a jami’ar Oxford da ke birnin Ingila. Cikin muƙalar da ta gabatar a taron mai taken “The Danger Of A Single Story” ta bayyana hadarin da ke tattare da labari daya tilo mai bangare daya (single story). Cikin jawabin ta a lokacin, Chimamanda ta bayyana irin tasirin da ‘single story’ ya ke da shi ga al’umma, ta yanda cikin ƙanƙanin lokaci ake yarda da wannan labarin, ko da ya saba da abun da ya ke a zahiri. Misali, saboda…
Read More

Tallafin Sadiya Farouq a kan Korona

Sadiya Daga IBRAHIM SHEME A bara ne aka samu ɓullar cutar nan mai suna 'Coronavirus' (COVID-19 a taƙaice), wadda da Hausa ake kira Korona. Cuta ce wadda ta mamaye duniya, ta zama annobar da mu dai a zamanin mu ba mu taɓa ganin irin ta ba. Ta tsiro ne daga birnin Wuhan da ke yankin Hubei na ƙasar Chaina inda daga can ta yaɗu a faɗin duniya. Ta tilasta rurrufe wurare tare da jawo bala'o'i da su ka haɗa da yawan mace-mace, rashin samun kuɗin shiga, hana tafiye-tafiye, rufe masana'antu da wuraren kasuwanci, rasa aikin yi, da kuma tsananin fargaba.…
Read More