Ra’ayi

A kiyaye amfani da addini don son zuciya

A kiyaye amfani da addini don son zuciya

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Nijeriya na daga cikin ƙasashen duniya na sahun farko da jama'ar ƙasar ta ke da son addini. Wata majiyar ma na cewa, Nijeriya ce ƙasar da mutanen ta ke da tsananin son al'amarin addini. Komai na 'yan Nijeriya sai ka samu addini a ciki, ko da kuwa a sautin ƙarar waya ne, sai ka fahimci ƙarar wayar Musulmi da ta wanda ba Musulmi ba. Muna nuna son junan mu saboda addini, mu taimaki bare saboda addini, mu gujewa ɗan uwa saboda addini. Akwai masu addini na tsakani da Allah, akwai 'yan na gada, 'yan son zuciya…
Read More
Me ya sa maza suke kasa sauke haƙƙin iyalansu?

Me ya sa maza suke kasa sauke haƙƙin iyalansu?

Daga AMINA YUSUF ALI Wai meye ma haƙƙoƙin da suke kan namiji na iyalinsa? Musulunci Addini ne wanda cikin hikima za a ga ya kawo dukkan wasu hukunce-hukunce na zamantakewa. Don haka zaman aure ma bai bar shi a baya ba. Ya tsara haƙƙoƙin mace da miji a aure. Kuma ya jaddada su a cikin Al-Ƙur'ani da hadisai, domin a samu daidaito da fahimtar juna. A cikin haƙƙin da aka ɗora wa mace babba daga ciki shi ne ta yi biyayyar aure. Ta bi mijinta sau da ƙafa tare da ƙauna da tausayawa. Sannan mace ita ke da haƙƙin kula…
Read More
Duniyar ce ta sauya ko mutanen cikinta?

Duniyar ce ta sauya ko mutanen cikinta?

Assalamu alaikum. Tarbiyyar yara a wannan lokacin ta wuce a ce iyaye ne kawai za su kula da ita, zamani ya zo na sauyin rayuwa, yara da manya kowa ya san kuɗi kuma ya san inda ake kashe su, savanin shekarun baya da muka samu labarin cewa wani sai ya haura shekaru goma sha biyar ba ya kashe kuɗi da kansa sai dai in aikensa aka yi sayen wani abu. A zamanin iyaye da kakanni ana rayuwa ne ba tare da dogon buri ko hangen wani ya fini ba, mutum mai wadata yana iya riƙe yaran maƙotansa da sauran yaran…
Read More
Garaɓasar ranar Arfa

Garaɓasar ranar Arfa

Wasu daga cikin yadda za ku tsara yin amfani da ranar Arafat kamar yadda ya da ce don cimma alfanu mai tarin yawa. Yin barci kaɗan a daren ranar Arafa.Tashi daga barci don yin salloli da sahur da niyyar ɗaukar azumin ranar Arafa.Sai yin sallar nafila raka’a biyu ko huɗu, sannan a tabbatar an yi adu’oi a yayin sujjada na samun duk alherin duniyar nan da na lahira, kar a manta a yi wa Allah godiya da Ya ba da ikon ganin wannan rana mai albarka wadda Allah (S.W.T) Ya ke bada alkhairai da yafiya ga al’umma ma su yawa.Kafin…
Read More
Mahara sun matsa lamba

Mahara sun matsa lamba

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Mahara a sassan Nijeriya na kara matsa lamba ko ƙaimi kan hare-hare don jefa tsoro da nuna gazawar tsarin da zai iya ƙalubalantarsu. Maharan a dazuka da birane na barazana ga rayuwar jama’a da kawo zaman zullumi. Gabanin ɓullowar ɓarayin daji, an samu wani yanayi ne inda a Abuja ma a kan kai hari da bom da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Gaskiya wasu hare-haren na da ban mamaki yadda su ke faruwa. Ko ma waye ya ke alhakin kai harin, rashin imanin sa ya kai a rubuta a jikin dutse. Harin bom…
Read More
Hare-haren ta’addanci a kan ayarin motocin Buhari da na Kuje

Hare-haren ta’addanci a kan ayarin motocin Buhari da na Kuje

A baya-bayan nan ne ’yan ta’adda suka kai hari a Cibiyar Gyaran Hali da ke Kuje, babban birnin tarayyar Abuja, inda suka kuvutar da fursunoni kusan 600, wanda 64 daga cikinsu ’yan ta’addar Boko Haram ne. Harin wanda ya ɗauki tsawon sa'o'i da dama ya yi sanadin mutuwar mutane biyar da suka haɗa da jami'an hukumar NSCDC waɗanda ba su ɗauke da makamai da kuma fursunoni huɗu. A yayin da suka isa wurin da yawa a kan babura, an ce 'yan ta'addar sun yi amfani da bama-bamai wajen rusa katangar gidan yarin. A cewar hukumomin wurin, jimillar fursunoni 879 ne…
Read More
Masu iya sayen bindiga a Zamfara da sauran garuruwa don kare kansu

Masu iya sayen bindiga a Zamfara da sauran garuruwa don kare kansu

Daga MUS'AB ISAH MARAFA Wannan dama da Gwamnatin Zamfara ta ba wa 'yan jiha wani cigaba ne daga inda ake yanzu. Kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya ce cikin wani Hadisin Tirmizi "wanda aka kashe wurin kare dukiyarsa ya yi shahada. Wanda aka kashe wurin kare addininsa, ya yi shahada; wanda aka kashe wurin kare jininss ya yi shahada; wanda aka kashe wurin kare iyalinsa ya yi shahada." Musulunci bai yarda ka tsaya wani ɗan iska ya wulaqanta ka ya wulaƙanta iyalinka don kawai yana da bindiga, ko da ko kai ba ka da bindiga balle a ce kana da…
Read More
Wa masu gidajen biredi za su yi wa yajin aiki?

Wa masu gidajen biredi za su yi wa yajin aiki?

Daga SALMAN MUKHTAR A yau na tsinci wani labari daga kafar sadarwa ta BBC Hausa akan yajin aikin da ƙungiyar masu Gidan Biredi watau (Association of Master Bakers and Caterer Of Nigeria), ke shirin shiga a satin nan sakamakon tsadar fulawa da kayan haɗi. Al'amarin yajin aikin nasu ya gicciyar da tunanina da na wasu ire-irena a kan wa za su yi wa? Gwamnati, da ba ta da gonar noma, ba ta da alkama, ba ta da kamfanin fulawa, ba ta da gidan biredi, a ƙarshe ba ta da bakin magana ballantana ta sa baki a sassauta muku? 2.Masu noma…
Read More
Tsakanin Bulama Bukarti da Gardi Zahra Mansur: darasi da nazari da izina

Tsakanin Bulama Bukarti da Gardi Zahra Mansur: darasi da nazari da izina

Daga DAKTA MUHAMMAD SULAIMAN FAGGE Wato da farko dai ya kamata Bulama Bukarti ya gode wa Allah. Mutane da yawa har da ni mai rubutun nan, mun kyautata masa zaton cewa shi ba mutumin banza ba ne, musamman da har za a zarge shi da harka da mata. Kuma wannan shaidar da ya samu daga bakuna masu yawa, tana da muhimmanci sosai, duk da cewa, ko me za a yi wasu ba za su yarda ba. Amma abin tambaya a nan, meye idan ka munana zato ga ɗan uwanka, bayan abin da kake zaton, ba tabbas? Wannan batu dole ne…
Read More
Ɓacewar takardun karatun ’yan siyasa wasa ne da hankalin ’yan Nijeriya

Ɓacewar takardun karatun ’yan siyasa wasa ne da hankalin ’yan Nijeriya

Daga ABBA YAKUBU ABDULLAHI Wani muhimmin batu da ya sake kunno kai a fagen siyasar ƙasar nan shi ne batun ɓacewar takardun shaidar karatun wasu ’yan siyasa masu neman manyan muqamai a ƙasar nan. Labari na baya bayan nan shi ne na sanarwar ɓacewar takardun shaidar kammala makarantar firamare da sakandire na mataimakin ɗan takara na wucin gadi ga Bola Ahmed Tinubu wanda Jam'iyyar APC ta tsayar domin ya yi mata takarar shugaban ƙasa. Rahotanni na bayyana cewa, Kabir Ibrahim Masari wanda aka gabatar da sunan sa a matsayin mataimakin Tinubu, ya shaida wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta INEC…
Read More