Ra’ayin Manhaja

Lokacin Hunturu: Matakan da suka wajaba a ɗauka don zama lafiya

Lokacin Hunturu: Matakan da suka wajaba a ɗauka don zama lafiya

A duk lokacin da aka shiga hunturu, wato lokacin sanyi da iska, wani lokaci ne da yanayi kan canja, wanda kowa da irin yadda yanayin yake zuwa masa, ta yadda wasu sukan samu kansu cikin wani yanayi na ƙunci, wasu kuma a wannan lokaci ne suka fi samun jin daɗin yanayi ta rayuwarsu gaba ɗayanta. Lokacin hunturu, lokaci ne na tsananin sanyi, iska da kuma ƙura, kuma wannan yanki namu na Arewa ne abin ya fi tsanani, ta yadda wasu lokuta ma hatta yanayin samaniya kan canja, a kan yi hadarin sanyi kamar yadda ake yin hadarin ruwan sama. Lokacin…
Read More
Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ga duk mai bibiyar al’amuran da suka shafi shafin yanar gizo, ko kuma mu ce harkar yaɗa labarai a ƙasar nan ya san yadda a ’yan watannin nan ake yawan samun koke-koken game da yadda wasu malaman jami’o’i ke lalata da ɗalibansu don su ba da maki, ko kuma don a kai su inda ba su kai ba a harkar jarrabawa. Ko ba a ce komai ba, wannan wani mummunan abu ne da za a iya cewa bai kama da hakali ba, ko kuma mu ce wani abu ne da ya zama bala’in wanda idan ba a yi hankali ba…
Read More
Dakatar da bautar da ƙananan yara a Nijeriya

Dakatar da bautar da ƙananan yara a Nijeriya

Akwai wani al'amari mai matuƙar tayar da hankali da ban tausayi kan yadda ake amfani da yara masu ƙananan shekaru maza da mata don yin aiki ko bauta a gidaje da sauran wurare da suka haɗa da shaguna, otel-otel, wuraren kwana na manyan makarantu ko ɗakunan kwanan ɗalibai a jami’o’i. Akasarin yaran ’yan ƙasa da shekaru 15 ne kuma ana ɗaukarsu ne da nufin yin aikace-aikacen da suka haɗa da shara, wanke-wanke, wanki, goge-goge, ɗebo ruwa da rainon jarirai da kula da yayayyun yara da makamantansu. Mafi yawan yaran ana kawo su cikin birni daga ƙauyuka lokaci zuwa lokaci, ta…
Read More
Batun sake duba dawo da martabar noma a Nijeriya

Batun sake duba dawo da martabar noma a Nijeriya

Kamar dai yadda kowa ya sani ne cewa, akwai gayar muhimmanci ga gwamnati ta sake duba batun bunqasa harkokin noma a ƙasar nan, duba da rawar da ɓangaren ke takawa wajen ci gaban tattalin arzikin ƙasa da samar da wadataccen abinci. Ayyukan noma su ne ginshiƙi kuma babbar hanyar da za ta iya jure kowace irin kwaramniya ga ci gaban ƙasa tare da al’ummarta baki ɗaya. Noma babbar abu ce a Nijeriya, ana ma kallon cewa ita ce sana’ar da ta fi kowace sana’a muhimmanci, wacce idan babu ita rayuwar ma sam-sam ba za ta yiwuwa ba. Haka zalika, kamar…
Read More
Illar gurɓata muhalli ga rayuwar al’umma

Illar gurɓata muhalli ga rayuwar al’umma

Rahotanni daga Hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO) sun nuna cewa, aƙalla gurɓata muhalli na sanadiyyar salwantar rayukan kusan mutum miliyan goma a duniya a kowace shekara. Wani babban abin tashin hankalin shi ne Nijeriya na daga cikin ƙasashen Afirika da wannan matsala ta yi ƙamari a cikinta, kuma ita ce ta huɗu a cikin jerin ƙasashen duniya da ake fama da wannan matsala ta gurɓata muhalli. Domin kuwa ƙididdiga ta nuna cewa, duk cikin ’yan Nijeriya dubu ɗari, akwai mutum ɗari da hamsin da ke mutuwa sakamakon shaƙar gurɓatacciyar iska a kowace shekara. A ƙasar Afganistan mutum 406,…
Read More
Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

An yi hasashen cewa 'yan Nijeriya miliyan 25 na iya fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Disambar 2023 idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba don magance matsalar. Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nakalto Cadre Harmonise a watan Oktoba na shekarar 2022, wani bincike na abinci mai gina jiki ƙarƙashin jagorancin gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya, yana mai nuni da cewa an yi hasashen cewa alƙaluman na ƙaruwa daga sama da mutane miliyan 17 da ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a halin yanzu a ƙasar. A cikin wannan adadi, mutane miliyan uku suna…
Read More
Kawo ƙarshen matsalar fyaɗe a Nijeriya

Kawo ƙarshen matsalar fyaɗe a Nijeriya

A kwanakin baya ne alqalin kotun da ke shari’ar laifukan fyaɗe da cin zarafin cikin gida da ke Ikeja, ya yanke wa daraktan kula da lafiya na gidauniyar kula da cutar daji, Dokta Olufemi Olaleye, hukuncin ɗaurin rai-da-rai kan laifin yi wa ’yar uwar matarsa fyaɗe. An tuhumi Olaleye da laifuka biyu na lalata da kuma keta haddin ’yar uwar matarsa, laifukan da ake zarginsa da aikata tsakanin Maris 2020 da Nuwamba 2021. An gurfanar da wanda ake tuhuma a ranar 30 ga Nuwamba, 2022 kuma ya musanta aikata laifin. Kwana ɗaya da faruwar, kotun da ke zamanta a Legas,…
Read More
Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

An yi hasashen cewa 'yan Nijeriya miliyan 25 na iya fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Agusta 2023 (lokacin bazara) idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba don magance matsalar. Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nakalto Cadre Harmonise a watan Oktoba na shekarar 2022, wani bincike na abinci mai gina jiki ƙarƙashin jagorancin gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya, yana mai nuni da cewa an yi hasashen cewa alƙaluman na ƙaruwa daga sama da mutane miliyan 17 da ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a halin yanzu a Ƙasar. A cikin wannan adadi, mutane miliyan…
Read More
Ƙaruwar cutar mantuwa a Nijeriya

Ƙaruwar cutar mantuwa a Nijeriya

Wani bincike na masana ya nuna cewa ’yan Nijeriya na cikin waɗanda suka fi fama da ciwon mantuwa a duniya. Ciwon mantuwa da ake kira ‘dementia’ na ɗaya daga cikin cututukan da ke barazana ga lafiyar bil’adama. Ƙungiyar da ta gudanar da binciken mai suna Alzheimer’s Disease International ta ce, sama da mutum miliyan 40 ke fama da cutar a duniya ba tare da sun sani ba. Binciken ya kiyasta cewa kashi 75 cikin 100 na ɗauke da cutar ba tare da sun sani ba, kuma waɗannan alƙaluma sun fi yawa a ƙasashen Nijeriya da Indiya da kashi 90 cikin…
Read More
Barace-baracen ƙananan yara a tituna abin dubawa ne

Barace-baracen ƙananan yara a tituna abin dubawa ne

Ga duk mai dubi zuwa ga yadda aka jefa Ƙananan Yara cikin harkar barace- barace, musamman a biranen ƙasar nan zai ga cewa akwai sosar zuciya mutaƙa, musamman ganin yadda yaran ke fama da wahala, sannan ga ɓata sunan Hausawa da abin ke jawowa. Akwai abubuwa da dama, waɗanda idan mutum ya yi dubi zuwa gare su za su dagula masa rayuwa ya ma rasa abin da ke masa daɗi, musamman idan aka duba yadda wasu abubuwa ke jawo wa rayuwar al’ummar da abin ya shafa. Wasu daga cikin waɗannan abubuwa, waɗanda kuma za mu iya cewa babu wani mai…
Read More