13
Nov
Farashin kayayyakin abinci ya yi tashin goron-zabi a Nijeriya musamman a yankin kudancin ƙasar sakamakon matsalar ambaliyar ruwa wadda ta haifar da cikas wajen safarar abincin daga arewacin ƙasar zuwa kudanci, al'amarin da ke ƙara jefa jama'a cikin halin ni-’yasu. Ambaliyar wadda ta yi sanadiyar mutuwar mutane 600 tare da raba miliyan biyu da muhallansu, ta haddasa asara ga 'yan kasuwa da ke safarar hajojinsu daga Arewa zuwa kudanci sakamakon yadda ta mamaye hanyoyin da motoci suka saba ratsawa. A cikin wata sanarwa da ta fitar a baya-bayan nan, Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi nuni da cewa, ana sa ran…