Month: January 2021

Gwamnati ta tallafa wa mata 8,000 da kudi N20,000 a Legas

Gwamnati ta tallafa wa mata 8,000 da kudi N20,000 a Legas

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta jaddada aniyarta ta kyautata rayuwar talakawa da marasa galihu a fadin kasa inda ta raba wa mata su 8,000 tallafin kudi na naira 20,000 ga kowaccensu a karkashin shirin nan nata na tallafa wa matan karkara da kudade. Ministar Jinkai da Agaji, Sadiya Umar Farouq ce ta bada jaddadin yayin kaddamar da shirin tallafa wa matan a Legas. Da take jawabi a wajen taron kaddamar da shirin a bisa wakilcin babban sakataren ma'aikatarta Bashir Nura Alkali, Sadiya ta ce, "Kudirinmu shi ne mu ga mata sama da 8,000 sun amfana da shirin a tsakanin…
Read More
Buhari ya jaddada bukatar hadin kan kasashen duniya wajen magance matsalolin duniya

Buhari ya jaddada bukatar hadin kan kasashen duniya wajen magance matsalolin duniya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya jaddada bukatar da ke akwai na kasashen duniya su hada kawunansu su yaki annobar korona da sauran manyan matsalolin da suka addabi duniya. Buhari ya yi wannan furuci ne a fadarsa da ke Abuja, sa'ilin da yake karbar wasikun shaida daga sabbin jakadun Masar da Saudiyya da kuma Argentina a Nijeriya. A cewarsa, "Matsaloli iri guda ne ke ci wa kasashenmu tuwo a kwarya, ciki har da matsalar ta'addanci da tabarbarewar tsaro da sauyin yanayi da karuwar yawan al'umma da safarar mutane da rashawa da talauci da kuma safarar makamai manya da…
Read More
Bankwana: Buratai ya zayyano nasarorin da ya samu a tsakanin watanni 66

Bankwana: Buratai ya zayyano nasarorin da ya samu a tsakanin watanni 66

Daga AISHA ASAS Tsohon Babban Hafsan Hafsoshin Nijeriya, Lt. Gen. Tukur Yusuf Buratai ya ce, watanni 66 da ya shafe a matsayin shugaban rundunar sojoji abin a yaba ne. Ya ce, a zamaninsa fannin sojin kasar nan ya samu nasarori da daman gaske tsakanin 2015 zuwa Janairun 2021. Buratai ya fadi haka ne a jawabinsa na bankwana da ya yi yayin da yake mika ragamar aiki ga magajinsa Maj. Gen Ibrahim Attahiru, a Alhamis da ta gabata a Abuja. Kafin nada Attahiru a matsayin sabon shugaban sojojin Nijeriya da Shugaba Buhari a Talatar da ta gabata, Buratai ya kasance Babban…
Read More
Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Adaga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Kasa ta sanar cewa sabbin shugabannin sojojin da aka nada kwanan nan za su bayyana gaban Majalisar Dattawa domin tabbatar da nadin nasu. A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, Hadimin Shugaba Buhari Kan Harkokin Majalisar Tarayya (Bangaren Dattawa), Sanata Babajide Omoworare ya bayyana cewa, tuni Shugaba Buhari ya tura wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, yana mai bukatar a tabbatar da nadin wadanda lamarin ya shafa. Sanarwar ta nuna cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da Majalisar Tarayya nadin da ya yi tare da neman majalisar ta tabbatar da nadin nasa…
Read More
Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Daga UMAR M. GOMBE Tsohon shugaban rundunar sojan Nijeriya, Lt. Gen. Tukur Buratai, ya bayyana cewa, kiris ya rage tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya yi masa ritaya daga aikin soja shekaru 21 da suka gabata. Ya ce, wannan ya faru ne a lokacin yana matsayin Manjo, tare da bayyana samun zarafin kaiwa matsayin 'Lieutenant General' da kuma Babban Hafsan Hafsoshi da ya yi a matsayin al'amari da ya shiga tarihi. Buratai, ya yi wadannan bayanan ne yayin da yake jawabin bankwana wajen mika ragamar aiki ga magajinsa Maj. Gen. Ibrahim Attahiru a babban ofishin sojoji da ke Abuja a…
Read More
Yadda mafarauci ya hallaka ahalinsa a Anambra

Yadda mafarauci ya hallaka ahalinsa a Anambra

Daga WAKILINMU Rahotanni daga yankin Amanuke a karamar hukumar Awka ta Arewa a jihar Anambra, sun nuna wani mafarauci mai suna Uchechukwu Nweke, ya harbe matarsa Mrs Patricia da bindiga har lahira sannan ya banka wa gidansu wuta tare dansa Mr Obinna a ciki a bisa dalilan da ba a kai ga ganowa ba. Mai magana da yawun 'yan sandan jihar CSP Haruna Muhammed ya tabbatar da aukuwar lamarin. Inda ya ce wanda ake zargi, ya aikata ta'asar ne a safiyar Alhamis, 28 ga Janairun 2021 kana daga bisani shi ma ya harbe kansa. CSP Muhammed ya ce, "'Yan bijilantin…
Read More
Raud al-jinan: Gudunmawar Waziri Gidado bin Laima

Raud al-jinan: Gudunmawar Waziri Gidado bin Laima

Tare da FATUHU MUSTAPHA Kwanakin baya, Farfesa Malumfashi Ibrahim ya janyo hankalina a wani rubutu da wani masani daga Kasar Amurka: Hui Xinpeng ya yi a kan shahararren littafin nan da Wazirin Sokoto : Gidado bin Laima ya rubuta a kan karamomim Shehu Usman bin Fodio, wannan rubutu ya burgeni, kuma har na kwafa na sanya shi a bango na na Facebook. To Amma ba wannan ne ya dauki hankali na ba, wani abu ne ya faru wasu mutum biyu daga cikin mutanen da suka yi koment a kan bayanin, sun kira littafin da tatsuniya: wannan abu ya bani mamaki…
Read More
Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Daga FATUHU MUSTAPHA Hamshakin dan kasuwar nan na Kasar Amurka, Bill Gates, ya shawarci Nijeriya da ta karkatar da hankalinta zuwa ga inganta fannin lafiyarta maimakon kashe makudan kudade wajen sayo allurar rigakafin cutar korona. Gates ya ba da shawar ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai ta bidiyo a Talatar da ta gabata, inda ya yi kira ga Nijeriya da kada ta yi amfani da 'yan kudaden da ta ware don kula da fannin lafiyarta wajen sayen rigakafin COVID-19 mai tsadar gaske. Jaridar Manhaja ta kalato dan kasuwar na cewa, “Ina mai bada shawarar a bai wa…
Read More
An kashe naira miliyan 900 wajen samar da manhajar sayar da tikitin jirgin kasa – Amaechi

An kashe naira miliyan 900 wajen samar da manhajar sayar da tikitin jirgin kasa – Amaechi

Daga WAKILIN MU Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ya bayyana cewa an samar da dandalin sayar da tikitin jirgin kasa ta intanet na Hukumar Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) a kan kudi naira miliyan 900 ta hanyar wata yarjejeniya ta shekara 10.Ministan ya bayyana haka ne kwanan nan sa'ilin da ya ke kaddamar da manhajar sayar da tikitin, ya na mai cewa hakkin kula da manhajar zai kasance ne a hannun wadanda aka yi yarjejeniyar da su na tsawon shekara 10, kana daga bisani ta koma karwashin kulawar NRC. A cewar sa, samun manhajar babban cigaba ne ga hukumar NRC da…
Read More
Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Daga UMAR M. GOMBE Babban Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Sha’anin Tattalin Arziki, Dakta Doyin Salami ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe kusan Naira Tiriliyan 2 wajen sayen kayayyakin abinci daga kasashen ketare tsawon watanni tara, lokacin da dukkanin iyakokin kan tudu ke rufe. Dakta Salami ya fadi haka ne a yayin da yake gabatar da jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan makomar tattalin arzikin kasar nan da ya gudana ta kafar bidiyo a Legas a tsakiyar wannan makon. A cewar Dakta Salami duk da rufe iyakokin kan tudu da Nijeriya ta yi, sai da gwamnati…
Read More