Month: May 2021

Rasuwar Attahiru babban ibtila’i ne ga ƙasa – Magashi

Rasuwar Attahiru babban ibtila’i ne ga ƙasa – Magashi

Daga UMAR M. GOMBE Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Salihi Magashi, ya ce abin kaɗuwa ne ainun rasuwar da Babban Hafsan sojoji na 21, Lt General Ibrahim Attahiru, ya yi a haɗarin jirgin sama kimanin watanni huɗu da naɗa shi kan sabon muƙaminsa. Cikin saƙon ta'aziyyar da ya miƙa, Janar Magashi ya ce haɗarin jirgin wanda ya yi ajalin Attahiru da sauran jami'an da suke tare, babban ibtila'i ne ga ƙasa. Ministan ya miƙa ta'aziyyarsa ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da Rundunar Sojoji da iyalan mamatan da ma ƙasa baki ɗaya dangane da wannan babban rashi da ya auku. Magashi…
Read More
Shugaban Rundunar Sojoji, Ibrahim Attahiru ya rasu a haɗarin jirgin sama a Kaduna

Shugaban Rundunar Sojoji, Ibrahim Attahiru ya rasu a haɗarin jirgin sama a Kaduna

Daga WAKILINMU Wani jirgin saman sojojin Nijeriya ɗauke da Shugaban Rudunar Sojoji, Ibrahim Attahiru tare da wasu jami''an rundunar,. ya yi haɗari. Duk da dai babu ciikakken bayani game da haɗari, amma dai bayanan da MANHAJA ta kalato sun nuna babu wanda ya tsira a haɗarin. A cewar majiyar MANHAJA, haɗarin ya auku ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin Juma'a a babban filin jirgin saman Kaduna sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka samu. Rundunar Sojan Sama ta Nijeriya (NAF) ta tabbatar da aukuwar haɗarin. Sanarwar da rundunar ta fitar wadda ta samu sa hannun Daraktan Sashenta na Hulɗa…
Read More
Wa zai auri ma’aikaciyar lafiya? (2)

Wa zai auri ma’aikaciyar lafiya? (2)

Daga AMINA YUSUF ALI Bismillahir rahmanir rahim. Da fatan masu karatu suna tare da ni kuma za su ci gaba da jimirin karanta wannan jarida tamu mai farin jini wato Manhaja. Mai fitowa kowanne mako. A makon da ya gabata ne muka kawo muku bayani masu yawa a game da yadda mata ma'aikata musamman waɗanda suke aiki a ɓangaren lafiya suke fuskantar ƙalubale da dama. Walau a wajen aikin nasu, ko gidajen iyayensu, har ma da gidajen aurensu da kuma sauran fannoni na rayuwarsu. Wasu daga cikin kalubalen da muka zano su ne; yadda mutane suke gudun su aure ko…
Read More
Ina mafita a musayar kalamai tsakanin Gwamnatin Kaduna da Ƙungiyar Ƙwadago?

Ina mafita a musayar kalamai tsakanin Gwamnatin Kaduna da Ƙungiyar Ƙwadago?

Daga AMINU ƊANKADUNA AMANAWA, Sokoto Wani babban abin da ya fi jan hankalin jama’ar Nijeriya a wannan lokacin da ake ciki, bai wuce turka-turkar da ke wakana ba tsakanin Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufa’i, da Ƙungiyar Ƙwadago (NLC), wacce shugabanta na ƙasa, Kwamred Ayuba Wabba, ke jagorantar gudanar da zanga-zangar ƙin jinin matakin da gwamnan na Kaduna ya ɗauka na dakatar da ma’aikatan ƙananan hukumomi da wasu tarin ma’aikatan jihar da sunan rage yawan kuɗaɗen da ma’aikatan ke laƙumewa na ɗan abin da jihar ke samu daga Gwamnatin Tarayya. Wannan kusan shine abinda bayanai, kafofin yaɗa labarai dama…
Read More
Tarwatsa zanga-zanga: ’Yan daba sun maye gurbin ’yan sanda

Tarwatsa zanga-zanga: ’Yan daba sun maye gurbin ’yan sanda

*A baya jami’an tsaro ake zargin da kawo cikas*Yanzu ’yan daba sun hutasshe su*Shin ko bambancin salon mulkin APC da na PDP ne?*Yadda fusatattun matasa suka kai wa NLC hari a Kaduna Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A Nijeriya lokutan gudanar da zanga-zangar nuna ƙin jinin gwamnati ko adawa da wani mataki da ta ɗauka an saba ganin yadda ta ke amfani da jami’an tsaro na ’yan sanda wajen tarwatsa masu zanga-zanga, inda ake zargin su da yin amfani da hayaƙi mai sa hawaye, motar ruwan zafi, kulake, wani lokacin ma har da harsashin bindiga ko makamatansu, don kawo…
Read More
Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

A kwanaki kaɗan da suka gabata, wato ranar 16 ga Mayu, 2021, ne, Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya buga bulaguro zuwa Birnin Paris, babban birnin Ƙasar Faransa, inda Shugaban ƙasar ta Faransa, Emmanuel Macron, ya karɓi baƙuncin shugabannin ƙasashen Afrika a taron tattaunawa kan jikkatar da aka sha sakamakon ɓarkewar annobar Cutar Korona da kuma duba yiwuwar samun tallafi, musamman bisa irin bashin da ya yi wa ƙasashen na Afrika katutu, sannan kuma ya ke ci gaba da ƙaruwa. Sai dai kuma, a sanarwar da Fadar Shugaban Nijeriya da ke Abuja ta bayar mai ɗauke da sa hannun Babban Mai…
Read More
Shugaban INEC ya buƙaci jama’a su sa ido kan kayan hukumar da ake lalatawa

Shugaban INEC ya buƙaci jama’a su sa ido kan kayan hukumar da ake lalatawa

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce hare-haren da ake kai wa hukumar tare da ƙona mata dukiya a wasu jihohi abin damuwa ne, domin zai shafi ƙoƙarin da ta ke yi na inganta tsarin zaɓe a ƙasar nan. Shugaban ya bayyana haka ne a wajen taron Kwamishinonin Zaɓe na jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya (FCT) wanda aka yi a ranar Laraba a Abuja. Yakubu ya ce yawaitar hare-haren ta ƙaru tun daga zaɓen 2019, to amma yanzu abin ya munana zuwa babbar matsala. Ya ce a cikin kimanin makwanni uku…
Read More
Hajjin 2021: Legas za ta soma yi wa maniyyata bitar mako-mako

Hajjin 2021: Legas za ta soma yi wa maniyyata bitar mako-mako

Daga WAKILINMU A matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen hajjin bana, Gwamnatin Jihar Legas ta ce za ta soma gudanar da taron bita na mako-mako ga maniyyatan jihar domin faɗakar da su game da harkokin hajji. Bayanan Hukumar Kula da Walwalar Maniyyata ta Jihar sun nuna cewa, Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Jihar Legas, Prince Anofiu Olanrewaju Elegushi, shi ne zai jagoranci ƙaddamar da shirin bitar nan ba da daɗewa ba. A sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, Sakataren hukumar, Mr. Rahman Ishola, ya ce an shirya gudanar da tarurrukan ne domin bada horo ga sabbin maniyyatan jihar da ma…
Read More