Editor

9513 Posts
Yadda ɗan almajiri ya fille kan ƙaramin yaro da wuƙa a Kano

Yadda ɗan almajiri ya fille kan ƙaramin yaro da wuƙa a Kano

Daga BASHIR ISAH 'Yan sanda a Jihar Kano sun fara bincike kan badaƙalar fille kan wani ƙaramin yaro mai suna Mohammed Saidu da ake zargin wani ɗan almajiri da aikatawa a ƙauyen Kanwa da ke yankin Ƙaramar Hukumar Madobi a jihar. Kwamishinan 'Yan Sandan Kano, Usaini Gumel ne ya bayyana wa Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) hakan ranar Juma'a a Kano. Jami'in ya ce ana zargin ɗan al'majirin mai suna Abdullahi mai shekara 16 da kisan Saidu ɗan shekara 6 da haihuwa. A cewar Gumel, wani mutum ne ya ga Abdullahi wanda ɗan asalin Jihar Zamfara ne a ƙauyen…
Read More
Dara ta ci gida: An sace tsohon shugaban ’yan bindiga

Dara ta ci gida: An sace tsohon shugaban ’yan bindiga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu gungun mutane sanye da kayan sojoji sun yi garkuwa da wani shahararren tsohon shugaban tsagerun Ribas, High Chief Sobobo Jackrich, wanda aka fi sani da Egberipapa, daga gidansa na Usokun da ke Ƙaramar Hukumar Degema a Jihar Ribas. Majiyoyi na kusa da tsohon shugaban tsagerun sun ce 'yan bindigar sun kai farmaki gidansa ne da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar ranar Litinin, inda suka kashe wasu hadimansa biyu tare da ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a sani ba. Sai dai ɗaya daga cikin majiyar ta yi imanin cewa sojoji ne suka kai harin,…
Read More
Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 200, sun tsare 330 a cikin mako guda — DHQ

Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 200, sun tsare 330 a cikin mako guda — DHQ

Daga BASHIR ISAH Babban Ofishin Tsaro ya bayyana cewa sojoji sun samu nasarar fatattakar 'yan bindiga inda sika kashe 188 tare da tsare 330 a yyuka mabambanta fa suka suka aiwatar a sassan Arewa a tsakanin mako guda da ya gabata Ofishin ya ƙara da cewa, dakarun sun kuɓutar da wadanda 'yan bindigar suka yi garkuwa da su har mutum 133 a cikin makon. Daraktan yaɗa labarai, Maj. Gen. Edward Buba, shi ne ya bayyana haka yayin da yake ƙarin haske kan nasarorin da suka samu a baya-bayan nan dangane da yaƙi da 'yan bindiga a ƙasar. Sanarwar da ya…
Read More
Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya kwantarwa da ’yan Nijeriya hankali kan batun ƙarin farashin wutar lantarki da Gwamnatin Tarayya ta yi. Ben Kalu ya ce 'yan majalisar sun ƙudiri aniyar tafka muhawara kan ko ya kamata a yi ƙarin kuɗin wutar ko a'a. A cewar mai magana da yawun Kalu, Levinus Nwabughiogi, ɗan majalisar na amsa tambayar wani mai sauraro da ya yi kiran waya cikin shirin yana tambayar matsayar majalisa kan ƙarin kuxin wutar. Kalu ya ce, "Gama-garin matsala ce. Ina cikin hutu, amma daga abin da ke damu na akwai takardar da…
Read More
EFCC ta ƙwato Naira Biliyan 30 yayin binciken Better Edu

EFCC ta ƙwato Naira Biliyan 30 yayin binciken Better Edu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Tu'annati, EFCC, ta ce ta kwato wa Gwamnatin Tarayya Naira Biliyan 30, yayin da ta kuma sanya asusun ajiyar banki 50 a binciken da ake yi wa tsohuwar ministar harkokin jinqai da yaƙi da fatara, Betta Edu da wata ma’aikaciyar ma’aikatar, Halima Shehu. Kimanin watanni uku da suka gabata ne shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Betta Edu da Halima Shehu saboda zargin karkatar da maƙuden kuɗaɗe. Nan take kuma, Shugaban ya dakatar da shirin na Tallafi da rage talauci (NSIP), sannan ya buƙaci hukumar EFCC da…
Read More
’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

*Sun miƙe ƙafa a bainar jama’a Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Wasu dandazon ’yan ta'addar daji sun miƙe ƙafa a lokacin Ƙaramar Sallah da a ka gudanar ranar Larabar da ta gabata, inda suka fito suka gudanar da sallar idi tare da sauran bukukuwa a bainar jama'a a Jihar Zamfara da ke yankin Arewa Maso Yammacin Najeriya. Bikin sallar ’yan bindigar daji ya zo ne a daidai lokacin da wasu malamai su ka bijire wa umarnin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, na sauke azumin watan Ramadan a ranar Laraba. Sarkin Musulmi ya sanar da cewa, ba…
Read More
Wulaƙanta Naira ta janyo wa ɗan daudu, Bobrisky zaman kuruku na wata shida

Wulaƙanta Naira ta janyo wa ɗan daudu, Bobrisky zaman kuruku na wata shida

Daga BASHIR ISAH Labarin da muka samu yanzu-yanzu na nuni da cewa, ɗan daudun nan Idris Olanrewaju Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky, zai shafe wata shida a kurkuku ba tare da wani zaɓi ba bayan da kitu ta kama shi da laifin wulaƙanta takardun kuɗi na Naira. Mai shari'a Abimbola Awogboro na Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ce ta yanke wannan hukunci. Alƙalin ta ce hakan zai zama darasi ga sauran jama'a waɗanda ke da ɗabi'ar wulaƙanta Naira.
Read More
Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nuna alhininsa dangane da rasuwar jaruma a masana'antar shirya finafinai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi dani da Daso. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Afrilu da kuma sa hannun mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale. Tinubu ya yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta'aziyya ga 'yan uwan da abobakan aiki da masoyan marigayiyar da ke sassa daban-daban. Tinubu ya bayyana rasuwar jarumar mai shekara 56 a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya. Ya…
Read More
Alaƙar tattalin arzikin Nijeriya da sharrin Yahudawa da Nasara

Alaƙar tattalin arzikin Nijeriya da sharrin Yahudawa da Nasara

Daga ALIYU ƊAHIRU ALIYU  Da yawan mutane suna ɗauka karyewar darajar kuɗin ƙasa kamar sharrin Amurka ne ko kuma ba abu ne mai kyau ba. Amma sau da yawa gwamnatoci da kansu suke karya darajar kuɗin ƙasarsu ta hanyar "devaluation". Me ya sa? Karya darajar kuɗin yana da matsala ta wata fuskar amma yana da alfanu ta wata fuskar. Kuma tamkar kowane sha'ani na tattalin arziki, dole zaɓi ne ake yi a tsakanin matsaloli biyu a ɗauki ɗaya a bar xaya (trade-offs). A tattalin arziki ba a jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya.  Ƙasar da ta karya darajar kuxinta tana…
Read More