Editor

9513 Posts
Za mu ƙarfafa wa sojoji kan yaƙi da ta’addanci a Zamfara — Tinubu

Za mu ƙarfafa wa sojoji kan yaƙi da ta’addanci a Zamfara — Tinubu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa kan yaƙi da ta'addanci a Jihar Zamfara. Tinubu ya ba da odar tura ƙarin sojoji zuwa jihar a matsayin mataki na ƙarfafa wa sojoji gwiwa wajen yaƙi da ɓarayin daji a jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar manema labarai wadda mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Asabar. Sanarwar ta ƙara da cewa, Tinubu ya ƙarɓi baƙuncin wasu gwamnonin jihohi da kuma shugabancin Majalisar Tarayya a gidansa da ke Legas. Ta ce, gwamnonin sun kai ziyarar ne a ranar Juma'a…
Read More
An kama mutum 20 bisa mamaye sakateriyar gwamnatin Oyo

An kama mutum 20 bisa mamaye sakateriyar gwamnatin Oyo

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Yan sanda tare da haɗin gwiwar wasu Jami'an tsaron sun cafke mutum ashirin da ake zargin sun mamaye/kai hari harabar gwamnatin a Agodi, Ibadan ranar Asabar. An sami amsar harsashai, da katin ATMs daga waɗanda ake zargin. "Baki daya, mutum ashirin aka kama wanda ake same su da bindiga 3, da harsashi 291, adduna 67, rigar kariya daga harsashi guda 5, takalma 6, amsa kuwa guda 10, hula nau'in odua nation guda uku, maɗaurin ƙugu guda 7, kayan soja nau'in Odua nation, mota ƙirar nissan marar rajista, sai talabijin 3 da mashina guda 3"…
Read More
Ina yayu da ƙannen Emefiele?

Ina yayu da ƙannen Emefiele?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA A gaskiya sunan tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya Godwin Emefiele ke kan gaba a zahiri a yanzu cikin jami'an tsohuwar gwamnatin Buhari da a ke tuhuma da rub da ciki da dukiyar al'umma. Ba a yi mamakin hakan ba don zarge-zarge da a ke yi ma sa na murɗiya tun ma gabanin shigowar tsohon shugaba Buhari mulki a 2015. A iya tunani da duba tarihi Emefiele zai zama cikin na kan gaba da su ka fi daɗewa kan wannan kujera ta gwamnan babban banki. Ya yi aiki da shugabanni 3 na dimokuraɗiyya kuma an haƙiƙance ya…
Read More
A ceci al’ummar Borno kafin labarin mutuwa ta riske ku

A ceci al’ummar Borno kafin labarin mutuwa ta riske ku

Gari yayi zafi, ta ko ina ta ɗauki ɗumi. Rayuwa na sake yin tsada, komai na ta ƙaranci, hakan ya sa dole sai an shiga motar Zulum, wanda cunkusuwa ya yi yawa, hakan na iya sa mutane su rasa rayukan su. Kwamishina mai kama da agogo, wanda yana tare da Gwamna mai alfarma kuma mai tausayin al'umma. Nace tausayi, wanda kowa yasan an gani, kuma lallai an shaida. Ba a kammala wanka sai da sabulu, dole a duba lamarin nan don gyara adon amarya a gaban angon ta. Abubuwa da ke faruwa; Mutane na tururuwa cikin motar nan, ana matsi…
Read More
Kawo ƙarshen cutar maleriya a Afirka

Kawo ƙarshen cutar maleriya a Afirka

A duk shekara ɗaruruwa dubbai na yara ne ke mutuwa sakamakon zazzaɓin cizon. Sai dai yanzu wata allurar riga-kafin maleriya da aka yi gwajinta a Afirka ta ba da sakamako mai ƙarfafa gwiwa. Sama da mutane dubu 400 zazzaɓin cizon sauro ya yi ajalinsu a shekarar 2019. Sakamakon sabuwar allurar riga-kafin da aka wallafa a mujallar kimiyya ta The Lancet, kuma yanzu haka ake jiran a sake yin bincike kanta, ya nuna cewa riga-kafin samfurin R21/Matrix-M na da ingancin kashi 77 cikin 100, bayan an shafe wata 12 ana gwajinsa. Hakan ya dace da mizanin Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO,…
Read More
Sojoji sun bayyana sunayen shugabannin ’yan ta’addan da aka kashe a makon jiya

Sojoji sun bayyana sunayen shugabannin ’yan ta’addan da aka kashe a makon jiya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Alhamis ne babban kwamandan rundunar sojin ƙasar ya fitar da cikakken bayanan wasu manyan kwamandojin ’yan ta’adda da aka kashe a yankin Arewacin ƙasar nan a yayin gudanar da ayyuka daban-daban a dukkanin wuraren da ke fama da rikici a tsakanin watan Janairu zuwa Maris, 2024. Daga cikin waɗanda sojojin suka kashe sun haɗa da shugaban lardin Is-Al Furqan (ISGS da ISWAP), Abu Bilal Minuki wanda aka fi sani da Abubakar Mainok a cikin 'yan ƙungiyarsa masu aikata laifuka da kuma Haruna Isiya Boderi. An ruwaito cewa, a ranar 21 ga watan Fabrairun 24…
Read More
Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Sanarwar da Ƙungiyar Ƙwadago ta Majalisar Ɗinkin Duniya (ILO) ta yi na baya-bayan nan ya nuna cewa, sama da yara miliyan 152 ko kusan ɗaya cikin yara 10 a duniya na fama da tilastawa wajen aure ko yin aikin ƙwadago wanda hakan ba wai kawai abin baƙin ciki ba ne amma har da nuna rashin mutuntaka. Ƙungiyar ta ce, qananan yara sama da miliyan 10 ke aiki a matsayin baran gida ko kuma masu hidima a ƙasashen duniya, wanda ake danganta shi da bauta. Ƙididigar da hukumar ta bayar cikin makon da ya gabata, ya nuna cewa, cikin adadin kashi…
Read More
Yadda yara uku ‘yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya rana guda a Nasarawa

Yadda yara uku ‘yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya rana guda a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Iyalan gidan Malam Sulaiman Ibrahim da ke garin Toto, cikin Ƙaramar Hukumar Toto, Jihar Nasarawa, sun tsinci kansu cikin halin jimami biyo bayan mutuwar wasu yaran gidan su uku wanda mota ta yi ajalinsu a lokaci guda da yammacin Juma'ar da ta gabata. Yaran da lamarin ya shafa wanda dukkansu mata ne, 'ya'yan mutum guda ne, kuma ajali ya cim musu ne a hanyarsu ta komawa gida bayan dawowa daga ziyarar gaisuwar sallah. Maihaifin yaran, Malam Sulaiman Ibrahim, ya yi wa MANHAJA ƙarin haske kan yadda lamarin ya faru inda ya ce, "Lamarin ya faru ne da…
Read More
Sifaniya ta hana tawagar Nijeriya bizar zuwa wasanni ƙasarta

Sifaniya ta hana tawagar Nijeriya bizar zuwa wasanni ƙasarta

Daga MAHDI M. MUH'D Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya, NFF, ta ce Ƙasar Sifaniya ta hana ’yan wasan tawagar Nijeriya ta 'yan ƙasa da shekara 15 bizar zuwa buga gasa ƙasar. Ta ce, hana bizar ya shafi 'yan wasa da jami'an da ke cikin tawagar masu lura da su. Don haka, "tawagar ba za ta je Sifaniya ba domin buga gasar UEFA ta 'yan ƙasa da shekara 16," kamar yadda NFF ta wallafa a shafinta na X. Sifaniya dai ba ta bayyana dalilin hana bizar ba. Sai dai hukumomin Sifaniya sun ce dalilin da Hukumar NFF ta bayar na neman bizar…
Read More
Waɗanne ƙasashen Afirka ne suka fi arziki da talauci a 2024? 

Waɗanne ƙasashen Afirka ne suka fi arziki da talauci a 2024? 

Daga AMINA YUSUF ALI Wani sakamakon bincike da Bankin ba da Lamun na Duniya ya yi, ya bayyana wasu ƙasashen Afirka mafiya talauci da mafiya arziki a shekarar 2024. A sha karatu lafiya.  Ana kallon nahiyar Afrika a matsayin wadda ta fi fama da talauci a faɗin duniya, inda abubuwa suka dabaibaye nahiyar kamar yadda tattalin arziki ke tangal-tangal da rashin tsaro da cin hanci da yaƙin basasa da kuma ayyukan ta'addanci. Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar da jerin ƙasashe mafiya arziki da kuma matalauta a faɗin Afrika na shekara ta 2024. Yayin duba ƙasashe masu arziki a…
Read More