Editor

9513 Posts
Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa ta yi kira da a sake nazari a kan ƙarin kuɗin wutar lantarkin da aka yi a baya-bayan nan, inda ta yi barazanar shiga yajin aiki. A cikin wata sanarwa, shugaban ƙungiyar, Adebiyi Adeyeye, ya yi gargaɗin yiwuwar shiga yajin aikin matuƙar ba a sauya ba. Hukumar da ke sa ido kan wutar lantarki ta Nijeriya ta kara haraji ga kwastomomin da ke samun wutar lantarki na sa’o’i 20 a kullum, lamarin da ya haifar da ƙarin farashin.  Adeyeye ya bayyana rashin daidaiton tsarin a matsayin hanyar da ke kashe…
Read More
Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Daga MAHDI M. MUH'D Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana cewa ƙungiyarsa na fuskantar babban ƙalubale idan suka kara da Real Madrid a gasar La Liga. Idan dai ba a manta ba, Man City ta fitar da 'yan wasan Carlo Ancelotti a kakar wasan da ta gabata a cikin salo mai ban sha'awa (ci 5-1) a hanyarsu ta ɗaukar kofin zakarun Turai na UEFA a karon farko a tarihinsu. Pep Guardiola ya tattaro haziƙan ’yan wasansa wajen ganin sun lallasa Real Madrid da ci 4-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe a filin wasa na Etihad bayan…
Read More
Makamashi: Matsaloli da mafita a Nijeriya

Makamashi: Matsaloli da mafita a Nijeriya

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Kamar yadda mu ka kwana a makon jiya cewa, mafita daga dukkan tarin matsalolin da Nijeriya da ma wannan nahiya ta Afrika suke fuskanta ta fannoni daban-daban shi ne sauya tunani, daga gurvataccen tunani da ya ke dankwafar da kasar Nijeriya da nahiyar mu ta Afrika. Kai tsaye shugabannin na Nijeriya su sauya tunanin nasu na ɗaukar duk wata shawara da ta fito daga Yammacin Turai da uwar gijiyarsu Amurka. Duk wata shawara da ta fito daga yammacin turai da Amurka tun bayan yakin duniya na biyu, shawarwarine na haɓaka qasashensu, misali cinikin makashin wuta…
Read More
Musulmi sun yi azumi cikin zafin rana da na aljihu

Musulmi sun yi azumi cikin zafin rana da na aljihu

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da nake wannan rubutu ya rage saura kwanaki ƙalilan musulmi su kammala azumin watan Ramadan na 2024, kamar yadda suka saba gudanarwa duk shekara har tsawon kwanaki 30 ko 29. Sai dai a bana an gudanar da azumin ne cikin wani yanayi na tsananin zafin rana, wanda a wasu ranakun har yana kai digiri 38 zuwa 40 na ma'aunin zafi a Nijeriya. Hakan ya jefa mutane da dama cikin wani muwuyacin hali, a yayin da suke ƙoƙarin sauke haƙmin ibada na wajibi da ke kansu. Kamar yadda muka sani, azumi wani muhimmin rukuni ne…
Read More
Matan aure barka da Ramadan! (3)

Matan aure barka da Ramadan! (3)

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barkanmu da sake kasancewa a wani makon a filinku mai albarka a jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. A wannan mako mun zo muku da ci gaba na maudu'in nan mai taken matan aure barka ramadan. Allah ya kawo kashi na uku kuma kashin ƙarshen wannan maudu'in da muke kawo muku girke-girke kala-kala wand amarya ko Uwargida za su samu su sabunta tukwanensu ga mai gida da sauran iyali saboda zuwan watan Ramadan mai albarka su ma su samu su samu ƙarin lada da rahamar Ubangiji Subhanahu wata'ala. Kamar yadda kuka sani…
Read More
Ya kamata marubuta su riƙa taimakawa mabuƙata – Nimcyluv

Ya kamata marubuta su riƙa taimakawa mabuƙata – Nimcyluv

"Na ciyar da mabuƙata fiye da ɗari cikin Ramadan" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Tun da watan Ramadan ya kama a wannan shekara, marubutan adabi maza da mata suka shiga cikin hidimar kyautata addininsu da kusancinsu da Allah, ban da shirye-shirye da suke gabatarwa a zaurukansu na Facebook da whatsapp, wasu kuwa har ƙungiyoyi ne da su da suke tallafa wa mabuƙata da ciyar da su abincin buɗe-baki. Na'ima Suleiman Sarauta na daga cikin marubutan da suke gudanar da irin wannan aikin neman lada na ciyarwa da taimakon marayu. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, Nimcyluv kamar yadda…
Read More
Gwamnatinmu za ta ci gaba da cika alƙawurran da ta ɗaukar wa al’umma —Gwamna Abba

Gwamnatinmu za ta ci gaba da cika alƙawurran da ta ɗaukar wa al’umma —Gwamna Abba

Ya ce duk wanda zai kawo mana tashin hankali a jihar Kano hukuma za ta yi aiki kansa Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya bayyana ƙudurin gwamnatinsa na cigaba da cika alƙawarin da ya yi wa al'ummarsa yayin neman zaɓe na bambaɗa musu ayyukan more rayuwa. Gwamna ya bayyana haka ne a ranar Ƙaramar Sallah yayin aike wa al'ummar jihar da ma ƙasa baki ɗaya da saƙon goron sallah. Ya ce, daga lokacin da gwamnatinsa ta karɓi ragamar mulki zuwa yanzu, sun aiwatar da ayyuka da daman gaske. Daga nan, ya ƙara jaddada…
Read More
Basarake ya kwanta dama bayan kammala  Sallar Idi a Legas

Basarake ya kwanta dama bayan kammala Sallar Idi a Legas

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa Sarkin Masarautar Isolo da ke Jihar Legas, Oba Kabiru Agbabiaka, Adeola Olushi III, rasuwa. Majiyarmu ta ce basaraken ya rasu ne a ranar Laraba jim kaɗan bayan da ya dawo daga sallar Idi. Shugaban Yankin Rayawa na Isolo (LCDA), Olasoju Adebayo, ya tabbatar da mutuwar basaraken. Ya ce za a yi jana'izar marigayin da misalin ƙarfe 4 na yamma daidai da karantarwar Islama. “Na samu umarnin Gwamman Legas, Mr. Babajide Sanwo-Olu, kan in sanar da rasuwar Sarkin Masarautar Isolo, Oba Kabiru Agbabiaka, Adeola Olushi III, a yau 10 ga Afrilun 2024. Ya rasu…
Read More
Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Yahaya S. Kaya fasihin marubucin labarin fim ne, da ya rubuta finafinai fiye da 20 a masana'antar fim ta Kannywood. A tattaunawasa da Ibrahim Hamisu a Kano za ku ji cikakken tarihinsa da kuma irin nasarorin da ya samu cikin shekaru 8 da shigar sa Kannywood, ku biyo mu: MANHAJA: Ka gabatar mana da kanka? YAHAYA S. KAYA: Sunana Yahaya S Kaya. Ni marubuci ne, ina rubutun littafi, ina na film. Ko za ka ba mu taƙaitaccen tarihinka? An haife ni a Garin Zariya, a shekarar 1996, na ta so a garin Zariya, anan na…
Read More
Ƙaramar Sallah: Gwamnan Zamfara ya miƙa saƙon goron sallah ga al’ummar Musulmi

Ƙaramar Sallah: Gwamnan Zamfara ya miƙa saƙon goron sallah ga al’ummar Musulmi

*Ya buƙaci a yi wa ƙasa addu'ar zaman lafiya Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya taya al'ummar Musulmi murnar bikin Ƙaramar Sallah, tare da kira kan yi wa Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya addu'ar samun dauwamammen zaman lafiya. Lawal ya miƙa saƙon nasa ne cikin sanarwar da Kakakinsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar. Sanarwar ta ce watan Ramadan da ya ƙare ya bai wa 'yan ƙasa damar zazzaga wa ƙasa addu'o'in samun zaman lafiya da kuma kwaranyewar matsalolin tsaron da ƙasa ke fama da su. Ta ƙara da cewa, yana da kyau Musulmi su ci…
Read More