Editor

9513 Posts
Sani Muazu ya nuna kaɗuwarsa kan rasuwar Daso

Sani Muazu ya nuna kaɗuwarsa kan rasuwar Daso

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kwamitin Amintattu na Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Sani Muazu, ya bayyana alhini da kaɗuwarsa dangane da rasuwar jarumar Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi sani da Daso. Ya bayyana haka ne cikin bayanin da ya fitar dangane da rasuwar marigayiyar a ranar Talata. Ya ce, “Cike da alhini na bi sahun ‘yan uwa wajen sanar da rasuwar ɗaya daga cikin fitattun jaruman Kannywood, Hajiya Saratu Giɗaɗo, wacce masoyanta suka fi kira da Daso. “Rasuwarta ta zo da kaɗuwa saboda ƙalau take ba ta fama da wani rashin lafiya. Cikin ƙoshin lafiya ta…
Read More
Masu harkar DJ sun koka kan haramta musu sana’a a Katsina

Masu harkar DJ sun koka kan haramta musu sana’a a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Ƙungiyar masu kiɗan DJ reshen jihar Katsina, ta koka dangane da hana sana'ar a faɗin jihar. Shugaban ƙungiyar a jihar, Hassan Mamman, ya bayyana irin halin da mambobin ƙungiyar za su shiga bayan da hukumar Hisba ta jihar Katsina ta hana gudanar da sana'ar. Ƙungiyar ta bayyana damuwwarta a wani taro da ta kira don wayar wa al'umma da kuma hukumar Hisba ta jihar kai game da yadda mambobinta suke tafiyar da sana'ar DJ a jihar. A cewar shugaban ƙungiyar sun ɗauki harkar DJ a matsayin sana'a, ba suna yi ba ne don ɓata tarbiyyar…
Read More
Gwamnan Kano ya sake naɗa Ogan Ɓoye kan muƙaminsa

Gwamnan Kano ya sake naɗa Ogan Ɓoye kan muƙaminsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya sake bai wa Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) muƙamin da ya ƙwace na mai ba shi shawara na musamman kan harkokin matasa da wasanni. Abba ya sake naɗa Ogan Ɓoyen a karo na biyu ne a cikin wasu sabbin naɗe-naɗe da ya yi a daren da ya gabata, kamar yadda sanarwar Babban Daraktan Yaɗa Labaransa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ta tabbatar. Daga cikin sabbin naɗe-naden da Gwamnan ya yi sun haɗa da: Farfesa Ibrahim Magaji Barde, mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattara kuɗaɗen shiga…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Jaruma a Kannywood, Saratu Giɗaɗo ta riga mu gidan gaskiya

Da Ɗumi-ɗumi: Jaruma a Kannywood, Saratu Giɗaɗo ta riga mu gidan gaskiya

Daga BASHIR ISAH da RABI'U SANUSI Allah Ya yi wa fitacciyar jaruma a masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka di sani da Daso, rasuwa. Jarumar ta rasu ne a ranar Talata kamar yadda wani makusancinta ya bayyanawa MANHAJA. Da yake amsa tambayar wakilinmu, makusancin marigayiyar ya ce lafiya ƙalau Saratu ta wayi gari a wannan rana. Ya ƙara da cewa, hasali ma Mmarigayiyar ta ɗauki azumi a wannan rana. Har wa yau, wata majiyar ta sheda ma wakilinmu cewa, "Saratu Gidado tana fama da rashin lafiya a tsaitsaye ne, wanda a yau kuma ta yi mutuwar Fuj'a".…
Read More
Gwamnatin Nijeriya ta ƙara hutun Ƙaramar Sallah

Gwamnatin Nijeriya ta ƙara hutun Ƙaramar Sallah

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayyar Najeriya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, ta amince da ranar Alhamis, 11 ga watan Afrilu, 2024, a matsayin ƙarin hutun aiki domin bukukuwn Ƙaramar Sallah. Bayanin haka na ƙunshe a cikin wata sanarwa da Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji Ojo ya fitar a madadin Gwamnatin Tarayya. Da fari, rakunan Talata da Laraba na wannan makon Gwamnatin ta ayyana a matsayin ranakun hutu don bikin salla, amma daga bisani ta ƙara zuwa Alhamis sakamon Ƙaramar Sallah ta faɗa Laraba. Ministan ya yi amfani da wannan dama wajen taya al’ummar musulmi murnar kammala wata guda na…
Read More
Abin da Shugaban NFC, Ali Nuhu suka tattauna da Jakadan Spaniya a Nijeriya

Abin da Shugaban NFC, Ali Nuhu suka tattauna da Jakadan Spaniya a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH A ranar Litinin ta wannan makon Shugaban Hukumar Shirya Fina-finai ta Ƙasa (NFC), Dokta Ali Nuhu, ya yi ganawa ta musamman a Abuja tare da Jakadan Ƙasar Spaniya a Nijeriya, Juan Ignscio Sell, inda suka tattauna kan muhimman batutuwa. Tattaunawar tasu ta shafi samar da ƙawance tsakanin NFC da Spaniya domin bunƙasa harkokin masana'antar ƙirƙire-ƙirƙire a Nijeriya. Da yake jawabi, Ali Nuhu ya yaba wa Jakada Sell bisa goyon bayan da ofishinsa kan bai wa masana'antar, tare da neman ya faɗaɗa goyon bayan nasa zuwa ga hukumar NFC don bunƙasa harkar shirya fina-finai da sauransu a Nijeriya.…
Read More
Azumi da iyalanmu

Azumi da iyalanmu

Daga AISHA ASAS A cikin littafi mai tsarki, Allah Mai Girma da Ɗaukaka Ya sanar da mu daraja da falalar da ke cikin watan Ramadan, daga ciki kuwa har da 'yanta bayi daga shiga wuta, samun dace da dare mafi daraja da ke cikin watan, daren da ya fi darare dubu a nauyin lada, wato daren Lailatul Ƙadar. Da yawa daga cikinmu idan an ambaci watan Ramadan hankalinmu da tunaninmu zai karkata ne ga iya yawaita ibada, karatun Alƙur'ani, yawan sallah da kame kai daga zina. Wanda hakan ya ɗauke tunaninsu daga kallon kyautatawa iyali a matsayin ɗaya daga cikin…
Read More
Bikin Sallah: KAROTA ta gargaɗi ma su ganganci da abin hawa

Bikin Sallah: KAROTA ta gargaɗi ma su ganganci da abin hawa

Daga RABI'U SANUSI a Kano Hukumar Kula da Zirga-zirgar Abubuwan Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), ta haramta guje-guje da ababen hawa a lokutan bikin Ƙaramar Sallah a faɗin Jihar. Hukumar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Kakakinta, Nabilusi Abubakar Kofar Na'isa, ya aiko wa MANHAJA a ranar Litinin, inda ya ce sun ɗauki matakin ne a sakamakon yadda guje-guje da ababen hawa ke zama barazana ga rayuwar al'umma. "Hakan ne ya sa hukumar ta ce za ta girke jami'anta guda 1500 domin sa ido a shagulgulan bikin Sallah a lungu da saƙo na jihar, domin su…
Read More
An ga watan Ƙaramar Sallah a Nijar

An ga watan Ƙaramar Sallah a Nijar

Daga BASHIR ISAH Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun ce an ga watan Ƙaramar Sallah a wasu jihohi biyar na ƙasar. Don haka, Talata take 1 ga Shawwal kuma ranar Ƙaramar Sallah a ƙasar. Sai dai, maƙwabciyar Nijar, wato Nijeriya da Saudiyya da sauransu, aun ce ba su ga wata ba, wanda hakan ya sa za su yi azumi 30 a ƙasashen sannan Laraba su yi Ƙaramar Sallah.
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Ba a ga watan Ƙaramar Sallah ba a Nijeriya — Sarkin Musulmi

Da Ɗumi-ɗumi: Ba a ga watan Ƙaramar Sallah ba a Nijeriya — Sarkin Musulmi

Daga BASHIR ISAH Sarkin Musulmi, Alh Abubakar Sa'ad, ya tabbatar da cewa ba a jinjirin watan Shawwal ba a Nijeriy a wannan Litinin ɗin. Don haka ya buƙaci al'ummar Musulmi ƙasar su cika azumi watan Ramadan zuwa 30, ta yadda ya zuwa Laraba, 10 ga Afriluu 2024, sai a yi bikin Ƙaramar Sallah. Da wannan, ya tabbata cewa Laraba ce 1 ga watan Shawwal, 1445AH. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar manema labarai da Kwamitin bai wa Sarkin Musulmi Shawar kan lamurran addini ya fitar ranar Litinin mai ɗauke da sa hannun Fargesa Sambo Wali Junaidu, wanda shi ne…
Read More