Kasuwanci

Muna cigaba da gamsuwa da jagorancin shuwagabanin kasuwar Mile12 a Legas – Alhaji Ummaru

Muna cigaba da gamsuwa da jagorancin shuwagabanin kasuwar Mile12 a Legas – Alhaji Ummaru

Daga Ummaru Dan Gara a Legas Sakataran Kuɗi na Ƙungiyar ’Yan Karas a Jihar Legas, Alhaji Ummaru Dan gara Sarina ta Ƙaramar Hukumar Garko, mazaunin Unguwar mile12 da ke Legas, ya bayyana cewa, shi da sauran al'ummar kasuwar mile12 suna ƙara gamsuwa da jagorancin shugabam a kasuwar mile12, Alhaji shehu Usman jibirin samfam tare da sauran shuwagabannin ɓangarorin kasuwar ta kewayanta gaba ɗaya. Alhaji Ummaru Dan Gara ya yi wannan tsokaci ne a gidansa da ke Sarina jim kaɗan bayan kammala karɓar baƙuncin waɗansu ɗimbin al'ummar da suka fito daga sassa daban-daban na ƙasar nan, su ka shigo jihar Kano…
Read More
MTN na shirin ƙara kuɗin kira da farashin data

MTN na shirin ƙara kuɗin kira da farashin data

Kamfanin sadarwa na MTN ya ce yana shirin ƙara kuɗin kira da farashin Data saboda tsadar rayuwa da yawan harajin da aka ɗora wa kamfanin. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin rahoton zangon farko na da kamfanin ya fitar kwanan nan. Kamfanin ya ce da alama yanayin kasuwanci a ragowar 2023 zai kasance mai tattare da ƙalubale. Don haka kamfanin ya ce shi ma zai duba sannan ya yi abin da ya dace don iya tafiyar da harkokinsa a wannan lokaci na ƙalubale. Kamfanin ya ƙara da cewa, ƙarin farashin shi ne mafita a wannan hali, saboda ta haka ne…
Read More
An kafa ƙungiyar mata masu kasuwancin intanet a Kano

An kafa ƙungiyar mata masu kasuwancin intanet a Kano

Daga AMINA YUSUF ALI Mata masu gudanar da kasuwanci a shafukan intanet a jihar Kano da ke Arewacin Najeriya sun kafa wata ƙungiya mai suna Women Online Vendors Association (WOVA) da za ta samar da aminci tare da kyautata hulɗa tsakanin mai saye da mai sayarwa. Shugabar ƙungiyar ta WOVA Hajiya Ayat Uba Adamu ta bayyana wa majiyarmu cewa sun kafa ƙungiyar ne da nufin haɗa kan matan da suke gudanar da kasuwancinsu a shafukan intanet tare kuma da samar da aminci tsakanin masu saye da sayarwa. “Samar da aminci tsakanin masu saye da sayarwa ta hanyar karkaɗe ɓata gari…
Read More
Kamfanin KAEDCO zai iya rasa lasisinsa sakamakon Bashin Naira biliyan 51.93

Kamfanin KAEDCO zai iya rasa lasisinsa sakamakon Bashin Naira biliyan 51.93

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin rarraba wutar lantarki na jihar Kaduna (KAEDCO) yana fuskantar barazanar rasa lasisin gudanar da kamfanonin saboda bashin Naira biliyan 51.93. Kamfanin KAEDCO ya amshi sanarwa daga hukumar kula da ƙa'idojin wutar Lantarki (NERC) a ranar Litinin xin da ta gabata. Inda ake umartar Bankin game da niyyar NERC na soke lasisinsa na gudanarwa. Wasu rahotanni da suka bayyana a ranar Talatar da ta gabata sun bayyana cewa, KAEDCO ta tara wa kanta bashin Naira biliyan 41.49 a tsakanin shekaru 2015 zuwa 2021, wanda Hukumar rarraba wutar ta Nijeriya a kan sari (NBET) da MO suka…
Read More
Farashin kayayyaki ya ƙaru da kashi 22.22 a Nijeriya – NBS

Farashin kayayyaki ya ƙaru da kashi 22.22 a Nijeriya – NBS

A halin da ake ciki, farashin kayayyakin masarufi a Nijeriya ya ƙaru zuwa kashi 22.22 a watan Afrilu saɓanin 22.04 a watan Maris. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Hukuma Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta fitar a ranar Litinin. A cewar Hukumar, ƙididdigar hauhawar farashi ta watan Afrilun 2023, ta nuna an samu ƙarin kashi 0.18 na tsadar kayayyaki idan an kwatanta da watan Maris da ya gabata. NBS ta ce bisa la'akari da sheka-shekara, an samu hauhawar farashi mai yawa a Afrilun bana idan aka kwatanta da yadda lamarin yake a Afrilun 2022, wato kashi 16.82. Hukumar…
Read More
Tsadar rayuwa: Kamfanin MTN zai ƙara kuɗin kira da farashin data

Tsadar rayuwa: Kamfanin MTN zai ƙara kuɗin kira da farashin data

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kamfanin Telecomms na MTN, ya ce, yana shirin ƙara farashin ayyuka a layinsa saboda hauhawar farashin kayayyaki a wuraren aiki. An bayyana hakan ne a cikin rahoton kafanin na farko da aka shigar a kasuwar hada-hadar hannayen jari ta Johannesburg a ranar Alhamis. A hasashen da ta yi na sauran shekarar 2023, kamfanin ya MTN ya ce, “Muna sa ran cewa yanayin kasuwanci a faɗin kasuwanni zai ci gaba da zama ƙalubale har zuwa ƙarshen shekarar 2023 kuma za mu ci gaba da aiwatar da matakan da za mu ɗauka don shawo kan ƙalubalen da ke…
Read More
Dangote ya kusa ƙaddamar da katafariyar matatar mai a Legas

Dangote ya kusa ƙaddamar da katafariyar matatar mai a Legas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ana sa ran Kamfanin Matatar Man Fetur na Dangote na biliyoyin daloli zai kawo mafita ga al'amuran matatar mai a Nijeriya. An ruwaito wata majiya ta bayyana cewa, shugaba Buhari zai ƙaddamar da kamfanin. A baya dai, kamfanin Dangote ya yi nuni da cewa, za a ƙaddamar da matatar man a Legas kafin ƙarshen wa’adin mulkin shugaba Buhari a ranar 29 ga watan Mayun 2023. Babban jami’in hulɗa da jama’a na kamfanin Dangote, Mista Anthony Chiejina, a wata sanarwa da ya fitar ya ƙaryata rahotannin da ke cewa matatar na daga cikin ayyukan da Buhari zai…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ƙara harajin shigo da shinkafa da alkama

Gwamnatin Tarayya ta ƙara harajin shigo da shinkafa da alkama

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin tarayya ta ba da sanarwar sake waiwayar harajin shigo da kayan waje (IAT) a matsayin wani ɓangare na tsara dokar harajin Gamayyar kasuwanci ta Afirka (ECOWAS) (CET) 2022-2026, wannan ya sa ta yi ƙari a kan haraji ga jasashe masu shigo da shinkafa, alkama, barasa, da sauran hajoji guda 189. Wannan sabon ƙarin harajin na shekarar 2023, ya ɗaga harajin kan shinkafa da ta haura kilo 5, ko mai yawa amma a rarrabe zuwa kilo 5, to za a biya harajin kaso 60, wanda kaso 50 ake biya a baya. Hakazalika, shigo da alkama ko…
Read More
Duniya rawar ‘yammata: BUA ya kere arzikin Ɗangote a watan Afrilun bana

Duniya rawar ‘yammata: BUA ya kere arzikin Ɗangote a watan Afrilun bana

Daga AMINA YUSUF ALI AbdulSamad Rabiu, hamshaƙin ɗan kasuwa a Nijeriya, kuma mutum na biyu ma fi dukiya a ƙasar ya buga tarihi a watan Afrilun shekarar bana ta 2023 a cewar sakamakon binciken kwanan nan da Forbes suka gudanar. Ƙarfin arzikin na Abdulsamad Rabi'u ya yi tashin gwauron zabi zuwa Dalar Amurla biliyan $8.6 a ƙarshe watan Afrilun na bana. Wato dai an samu ƙaruwar maƙudan kuɗi har Dalar Amurka biliyan $300 wato kwatankwacin Naira biliyan 138.14 musamman idan aka kwatanta dukiyarsa da dalar Amurka biliyan $8.3 da take a 1 ga watan Afrilu, 2023. Wannan ya nuna cewa,…
Read More
Jarumi Uzee ya zama jakadan Bankin Musulunci na TajBank

Jarumi Uzee ya zama jakadan Bankin Musulunci na TajBank

Daga AMINA YUSUF ALI Fitaccen jarumin nan na Kannywood da Nollywood, Usman Uzee, ya zama jakadan bankin nan na Musulunci, wato TajBank. A ranar Alhamis, 4 ga Mayu, 2023, jarumin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar da bankin tare da manyan jami’an bankin. Idan dai za a iya tunawa, bankin na TajBank yana daga cikin kalilan din bankuna a Nijeriya da ba su mu’amula da kudin ruwa. Shi kuwa Jarumi Uzee yana daga kalilan din jarumin Nijeriya da suke fitowa a finafinan Arewa da na Kudu. Daya daga cikin fitattun finafinan da ya fito shine, Voiceless, wanda ya samu hawa manhajar…
Read More