04
Dec
Daga BASHIR ISAH Yanzu dai ya tabbata fadan da ke tsakanin matar Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari, da ɗalibin nan Aminu Mohammed Adamu, ya ƙare. Hakan ya biyo bayan ganawar da Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ya yi da Aminu ɗin ne bayan da aka sako shi daga gidan maza. Aminu, wanda ɗalibi ne a Jami'ar Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa, ya gamu da fushin Aisha ne bayan da ya caccake ta a shafinsa na Tiwita inda ya ce ta ci kuɗin talakawa ta yi ɓul-ɓul. Lamarin da ya sanya jami'an tsaro na DSS suka bi sawun ɗalibin har makarantarsu suka…