Labarai

Na shafe watanni Ina haɗa jinina da zoɓon sayarwa, inji mai cutar ƙanjamau

Na shafe watanni Ina haɗa jinina da zoɓon sayarwa, inji mai cutar ƙanjamau

Daga WAKILINMU Wata mata da kawo yanzu babu wani cikakken bayani a kanta ta bayyana cewa tana amfani da jini mai ɗauke da ƙwayoyin cutar ƙanjamau wajen haɗa zoɓon da ta ke sayar wa jama’a. Matar wadda ta yi wannan ikirari ta bayyana hakan a yayin wani shiri mai taken ‘hada-hadar kasuwanci’ na MarketRunz da gidan rediyon Wazobia FM ya saba watsawa a duk daren ranar Laraba. A cikin shirin dai masu sauraro kan kira ta lambar waya su faɗi ababen da suke aikatawa a bayan fage kan harkokinsu na kasuwanci waɗanda abokan hulɗarsu ba su da masaniya a kai,…
Read More

Xi Jinping: Sin na goyon bayan shigar da ƙungiyar AU G20

Daga MARYAM YANG Cikin jawabin da ya gabatar a yayin zaman farko na taron ƙolin G20, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, ƙasar Sin tana goyon bayan shigar da ƙungiyar tarayyar ƙasashen Afirka wato AU cikin ƙungiyar G20. Ya ce, a halin yanzu, ƙasashen duniya, musamman ma ƙasashe masu tasowa suna fuskantar ƙalubalen raguwar tattalin arziki. Don haka ya ba da shawarar kafa dangantakar abokantaka ta neman farfaɗo da tattalin arzikin duniya, da mai da aikin neman ci gaba, da raya al’umma a matsayin babban aikin da aka sanya gaba, tare da mai da hankali kan buƙatun ƙasashe…
Read More
2023: Kotu ta umarci INEC ta ci gaba da yi wa ‘yan ƙasa rijistar Katin Zaɓe

2023: Kotu ta umarci INEC ta ci gaba da yi wa ‘yan ƙasa rijistar Katin Zaɓe

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta Abuja ta bai wa Hukumar Zabe Mai Zama Kanta ta ƙasa (INEC) umarni kan gaggauta komawa ta ci gaba da yi wa masu zaɓe rijistar zaɓen 2023. Kotun ta buƙaci INEC ci gaba da shirin nata har sai ya rage kwana 90 kafin zaɓen na 2023.Alƙalin kotun, Mai Shari’a Inyang Ekwo, ya bai wa INEC umarnin ta tabbatar ba ta hana dukkan ’yan Najeriya da shekarunsu ya kai 18 damar yin rajistar ba. Hukuncin da ya yanke ranar Talata, Alƙalin ya ce haƙƙi ne a kan INEC ta tabbatar da ta…
Read More
Aisha Buhari ta karye, an garzaya da ita asibiti

Aisha Buhari ta karye, an garzaya da ita asibiti

Daga WAKILINMU An garzaya da Matar Shugaban Ƙasa, Aisha Muhammadu Buhari, zuwa asibitin Abuja sakamakon karyewa da ta yi a ƙarshen mako. Duk da dai babu wani cikakken bayani dangane da yadda Aisha ta samu karayar, sai dai majiyarmu ta ce, "faɗuwa ta yi inda ta karye a ƙafa." Kafin faruwar lamarin, an shirya Aisha za ta shirya liyafar aure na bikin Bilkisu Rimi, 'ya ga Jakadan Nijeriya a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, Mohammed Rimi, ranar Lahadi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Idan za a iya tunawa, a ranar Alhamis da ta gabata Aisha Buhari ta ƙaddamar da yaƙin…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta fara karɓe kadarorin waɗanda ke ɗaukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta fara karɓe kadarorin waɗanda ke ɗaukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A cigaba da daƙile ayyukan ta'addanci da ake fuskanta a lungu da saƙon ƙasar nan, Gwamnatin Nijeriya ta fara ƙoƙarin karɓe kadarorin waɗanda aka gano suna taimaka wa ko ɗaukar nauyin 'yan ta'adda ta hanyar amfani da kuɗaɗensu da shawarwarin su da dai sauransu don haɓaka ta'addanci a cikin ƙasar. Kamar yadda wasu gidajen jaridu suka rawaito, sun ce jami'an tsaro da sauran hukumomin ƙwararru a kan lamuran tsaro suna bibiyar kadarorin masu taimaka wa 'yan ta'adda da suka haɗa da kamfanoni da asusun ajiya na banki da kuma wasu ƙungiyoyi masu alaƙa da…
Read More
Sojoji sun hallaka mai kai wa su Turji makamai a Shinkafi

Sojoji sun hallaka mai kai wa su Turji makamai a Shinkafi

Daga BASHIR ISAH A wani samame da Rundunar Mayaƙan Sama ta Nijeriya (NAF) ta kai da jirigin yaƙinta a Jihar Zamfara, Rundunar ta samu nasarar kashe Malam Ila wanda ya yi ƙaurin suna waje safarar makamai a ƙauyen Manawa cikin Ƙaramar Hukumar Shinkafi a jihar. Majiyar PRNigeria ta ce, Ila shi ne babban mai yi wa ‘yan ta’adda safarar makamai, musamman ma Bello Turji a Zamfara. Majiyar ta ce, “A ranar 18 ga Nuwamban 2022 NAF a ƙarƙashin Operation Hadarin Daji suka kai samamen inda aka hallaka Malam Ila. “Malam Ila ya kasance wanda ake nema ruwa a jallo saboda…
Read More
Jami’ar Jihar Kwara ta yi babban rashi

Jami’ar Jihar Kwara ta yi babban rashi

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi Mataimakin Shugaban Jami'ar Jihar Kwara (KWASU), Muhammed Akanbi, rasuwa. Marigayin wanda farfesa ne a fannin doka kuma Babban Lauyan Nijeriya (SAN), ya bar duniya yana da shekara 51. Rijistaran jami'ar ya tabbatar da rasuwar marigayin cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi da daddare. “Cikin alhini da sadaukarwa ga Allah, Hukumar Gudanarwar ta Jami'ar Jihar ke sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban jami'ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi SAN,” inji sanarwar. An naɗa marigayi Akanbi a matsayin Mataimakin Shugaban KWASU ne a watan Afrilun 2020. Marigayin ɗa ne ga shugaban hukumar ICPC na farko, marigayi…
Read More
Bayan tilasta biyan ‘Kuɗin Kariya’, ’yan bindiga sun wawushe mutum 44 a ƙauyen Zamfara

Bayan tilasta biyan ‘Kuɗin Kariya’, ’yan bindiga sun wawushe mutum 44 a ƙauyen Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aƙalla mutum 44 ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da su a ƙauyen Kanwa da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara. Mazauna yankin sun ce maharan sun yi wa ƙauyen ƙawanya ne cikin dare, inda suka riƙa bi gida-gida suna kwasar mutane, galibi mata da ƙananan yara. A baya-bayan nan dai, an ɗan sami salamar yawan satar mutane a ƙauyukan Zamfara, amma bisa ga dukkan alamu a ’yan kwanakin nan, cikin mazauna ƙauyukan ya fara ɗurar ruwa saboda yadda lamarin ya sake dawowa. Ana dai zargin cewa riƙaƙƙen ɗan bindigar nan na yankin, Dankarami…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 20 a Zamfara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 20 a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau 'Yan bindiga a Jihar Zamfara,sun sace mutum 20 ciki har da wasu tagwaye 'yan mwana huɗu da haihuwa. Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan da Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ibrahim Dosara, ya bayyana cewa an inganta tsaro a jihar. Garkuwa da mutanen ta faru a garin Daura cikin Ƙaramar Hukumar Zurmi a jihar. Wani mazaunin garin, Malam Haruna Ahmad Dauran, ya tabbatar wa Blueprint Manhaja aukuwar hakan a tattaunawar da suka yi ranar Lahadi. A cewarsa, ‘yan bindigar sun mamaye garin ne da misalin ƙarfe 8:30 na safiyar Asabar inda suka fara bincike…
Read More
Dogara Yaro ne Sarkin Hausawan Legas – Tinubu

Dogara Yaro ne Sarkin Hausawan Legas – Tinubu

Daga WAKILINMU Ɗan takarar Jam'iyyar APC kuma tsohon Gwamnan Jihar Legas, Sanata Ahmed Bola Tinubu, ya amince da Alhaji Aminu Dogara a matsayin Sarkin Hausawan Jihar Legas, lamarin da ya warware matsalar shugabanci da ta kunno kai kuma ta dabaibaye al'ummar Arewa mazauna Birnin Ikko, wato Legas. Asiwaju Bola Tinubu ya kawo ƙarshen rikicin ne a ranar Juma'a, 18 ga Nuwamba, 2022, bayan da ya amince da rahoton kwamitin da ya kafa ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Alhaji Lawal Abbas Garba a matsayin Sakataren Kwamitin. A yanzu an amince da Alhaji Aminu Dogara Yaro a…
Read More