Labarai

Ta kashe mijin abokiyar maɗigonta a Anambara

Ta kashe mijin abokiyar maɗigonta a Anambara

Wata mata ta kashe mijin abokiyar maɗigonta ta hanyar daɓa masa wuƙa a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya. Rahotanni sun nuna cewa, ba a bayyana sunan matar da ta yi kashe Ikechukwu Onuma da aka fi sani da ‘Ayaaya Onye-Obodo’ ba, amma tana aiki a Kwalejin horo na lafiya a Onitsha. Ta gudanar da wannan aika-aikar ne a gidan mutumin a kan titin Ogboli da misalin qarfe 9:20pm na daren Talata a birnin Onitsha da ke jihar Anambra. Marigayi Mista Onuma ya isa gida ba tare da matarsa ta sani ba, inda ya tarar da ita da…
Read More
MURIC ta buƙaci a gaggauta yin adalci kan kisan Sheikh Aisami

MURIC ta buƙaci a gaggauta yin adalci kan kisan Sheikh Aisami

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Kare 'Yancin Musulmi (MURIC) ta yi kira da a gaggauta yin adalci kan kisan shahararren malamin nan Shaykh Goni Aisami da wasu sojoji biyu suka yi. MURIC ta bayyana kashe malamin da aka yi a ranar Juma'a, 19 ga Agustan 2022 a matsayin kisan wulaƙanci wanda ya zama wajibi a bi wa marigayin kadinsa. Ƙungiyar ta yi waɗannan kalaman ne cikin sanarwar manema labarai da ta fitar ran Litinin ta hannun daraktanta, Farfesa Ishaq Akintola. Sanarwar ta ce, “Wani soja da ya yi iƙirarin yana bakin aiki ya kashe fitaccen malamin Islaman nan da ke Gashua,…
Read More
Kotu ta tasa ƙeyar matashin da ya yi sanadiyyar rasa ƙafar matashiya Fatima a Sakkwato

Kotu ta tasa ƙeyar matashin da ya yi sanadiyyar rasa ƙafar matashiya Fatima a Sakkwato

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Wata kotun majistare dake a Sakkwato ta tasa ƙeyar Aliyu Sanusi Umar matashin da ake zargi da yin tuƙin ganganci da ya yi sanadiyar rasa ƙafar ɗalibar makarantar Khalifa dake Sokoto Fatima. Wannan dai ya biyo ne bayan ƙarar da lauyan Fatima suka shigar a gaban kotu, da suke buƙatar kotun ta ƙwato wa Fatima haƙƙinta daga wanda ake zargi da zama sillar rasa ƙafarta. Mahaifin Fatima bayan fitowa daga kotu Lauyan mai ƙarar a zaman kotun na ranar Litinin ya buƙaci kotun da ta duba yuwar bada belin wanda ake zargin la'akari da tanadin…
Read More
Matasa sun nutse a ruwa a yayin da suke murnar cin jarrabawa a Legas

Matasa sun nutse a ruwa a yayin da suke murnar cin jarrabawa a Legas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar 'yan sanda a Jihar Legas ta ce wasu matasa huɗu sun nutse a ruwa a yayin da suke murnar cin jarrabawar kammala sakandire. Lamarin ya afku ne a ranar Talata a tekun Elegushi da ke unguwar masu galihu ta Lekki. Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan SP Benjamin Hundeyin, ya wallafa a shafinsa na tiwita cewa matasan sun nitse bayan sun karvi sakamakon jarrabawarsu daga makaranta. Hukumar gudanarwar tekun ta ce mamatan na daga ckin ɗalibai 10 da suka je wajen don yin murnar samun nasara a jarrabawarsu ta kammala karatun sakandire.…
Read More
Za mu taimaka wajen yaɗa littattafan Sheikh Farouk Cheɗi – Sa’adatu Rimi

Za mu taimaka wajen yaɗa littattafan Sheikh Farouk Cheɗi – Sa’adatu Rimi

Daga MIUHAMMADU MUJJITABA a Kano An bayyana cewa littattafai da sauran bayanai na na ilimi wasu a rubuce wasu ma ba a buga littattafan ba, dama kasat-kasat, na Marigayi Sheikh Yahaya Faruku Cheɗi abu ne da su ke da matuƙar muhimmanci wajen fito da ilimi a cikin su. Don haka littattafan da aka buga su a yanzu da kuma wanda za a bugasu a nan gaba za su tsaya tsayin daka wajen ganin sun kaisu makarantar Sa`adatu Rimi da ma sauran kwalejoji ilimi na Kano da taimaka wajen yaɗa su ga al'umma domin jama'a na yanzu da masu zuwa nan…
Read More
Gwamna Ganduje ya kafa kwamitin binciken zargin karkatar da Naira miliyan 352 a Jami’ar Wudil

Gwamna Ganduje ya kafa kwamitin binciken zargin karkatar da Naira miliyan 352 a Jami’ar Wudil

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya kafa kwamitin da zai binciki zargin karkatar da Naira miliyan 352 a Jami’ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil a jihar. A kwanakin baya ne wani kwamiti da aka kafa don binciken mahukuntan jami’ar kan zarge-zarge ya miƙa rahotonsa ga gwamnati. Daga cikin shawarwarin da kwamitin ya bayar kuma har da na buƙatar bincikar yadda ake zargin karkatar da kuɗaɗen, waɗanda aka ce na fanshon ma’aikatan jami’ar ne. Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya sanar da kafa kwamitin a cikin wata sanarwa da…
Read More
‘Yan sanda sun samu nasarar hallaka varayin daji masu tarin yawa a Katsina

‘Yan sanda sun samu nasarar hallaka varayin daji masu tarin yawa a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'yan sanda a jihar katsina ta ce jami'anta sun hallaka 'yan ta'adda da kawo yanzu ba a tantance yawansu ba a yayin wani gumurzu da ya haddasa musayar wuta a tsakanin ɓangarorin biyu. Kakakin rundunar SP Gambo Isah ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar lamarin dai ya faru a yankin Ƙaramar Hukumar Kurfi. A yayin artabun rundunar ta samu nasarar ƙwato tumaki 72 da awaki 34 gami da shanu 2 daga hannun 'yan ta'addar. Musayar wutar dai ta faru ne a ƙauyukan Dadawa da Barkiya na karamar hukumar,…
Read More
An kama wani ɗalibi ɗan shekara 18 bisa yunƙurin yin garkuwa da shugaban makaranta a Neja

An kama wani ɗalibi ɗan shekara 18 bisa yunƙurin yin garkuwa da shugaban makaranta a Neja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jami’an Hukumar Tsaron Al'umma ta Nijeriya (NSCDC), reshen Jihar Neja sun kama wani ɗalibi ɗan shekara 18 da haihuwa, bisa zargin yunƙurin yin garkuwa da Shugaban Makarantar Koyon Noman Kifi a Sabuwar Bussa. Hakan ya fito ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, ASC Nasir Abdullahi, ya fitar a ranar Laraba. Ya ce wanda ake zargin, wanda ɗalibin kwalejin ne, ya haɗa baki da wani mutum ɗaya, wanda a halin yanzu, ya rubuta wasiƙar barazanar yin garkuwa da Provost idan ya kasa biyan kuɗin fansa. Sai dai Nasir ya ce wanda ake zargin bai…
Read More
An yaba wa ɗan sandan Nijeriya da ya ƙi karɓar cin hancin sama da Naira miliyan 83

An yaba wa ɗan sandan Nijeriya da ya ƙi karɓar cin hancin sama da Naira miliyan 83

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Sufeton 'Yan Sandan Nijeriya Usman Alkali Baba ya yaba wa wani ɗan sandan ƙasar da ya ƙi karɓar cin hancin dala 200,000 kwatankwacin Naira miliyan 83.87. A wata sanarwa da rundunar 'yan sandan ƙasar ta wallafa a shafinta na Tuwita ranar Laraba, an kuma yaba wa wasu 'yan sanda biyu bisa jajircewarsu bisa ayyukansu. Sanarwar, wadda kakakin rundunar 'yan sandan Nijeriya, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya sanya wa hannu, ta ambato babban sufeton 'yan sandan yana bayar da umarni a bai wa 'yan sandan uku takaradar shaidar nuna ƙwazo bisa ayyukansu duk kuwa da…
Read More
Zan haɗa kan ‘yan Nijeriya idan na lashe zaɓe – Atiku

Zan haɗa kan ‘yan Nijeriya idan na lashe zaɓe – Atiku

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ɗan takarar shugabancin Nijeriya na Jam'iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya samu gagarumar tarba cikin ƙasaitaccen biki a garin Jada, wanda nan ne mahaifarsa. Da ya ke masa maraba, cikin ƙasaitaccen yanayi da aka shirya na musamman, shugaban ƙaramar hukumar Jada Honorable Salisu Muhammed Solo ya ce, suna mutuƙar alfahari da kasancewar Atiku ɗansu, inda ya yi alƙawarin mara masa baya a takarar shugabancin Nijeriya da ya ke yi.  A jawabinsa yayin taron, Sanata Dino Melaye ya bayyana muhimmancin ziyayar zuwa gida, inda yace wannan ya nuna cewar Atiku ya san asalin sa…
Read More