Ra’ayi

Barazanar jefa ƙuri’ar ƙananan yara

Barazanar jefa ƙuri’ar ƙananan yara

Ƙuri’ar ’yan ƙasa da shekaru 18 wata ɓarna ce a tsarin zaɓen Nijeriya. Shekarun da suka cancanci shiga zaɓe a ƙasar sune ’yan shekaru 18 zuwa sama. Sai dai a lokacin zaɓe, ana barin yara su kaɗa ƙuri’a a wasu sassan ƙasar. Wani lokaci ma matattu ma suna yin zaɓe. Kuma wannan shine tushen fara rigingimu. Lokacin da aka ba wa yaran da ba su kai shekarun jefa quri'a damar jefa ƙuri'a ba, hakan yana kawo cikas ga sahihancin tsarin zaɓe kuma yana sanya alamar tambaya kan sakamakon aikin. A kwanakin baya, gamayyar ƙungiyoyin farar hula 10 (CSO) sun koka…
Read More
Me ya sa aka dakatar da koyar da ilimin jima’i a makarantu?

Me ya sa aka dakatar da koyar da ilimin jima’i a makarantu?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ba da jimawa ba ne ofishin Ministan Ma'aikatar Ilimi Malam Adamu Adamu ya fitar da wata sanarwa game umarnin dakatar da cigaba da koyar da ilimin jima'i a ƙananan makarantu da sanarwar fara amfani da harshen uwa na gado wajen koyar da yaran makarantun firamare, a tsarin koyarwa na makarantun ƙasar nan. Batutuwan da yanzu haka ke cigaba da ɗaukar hankalin masana ilimi da sauran jama'ar ƙasa. A wannan mako nima ina son yin tsokaci ne game da batun dakatar da koyar da ilimin jima'i a makarantu, kamar yadda taken rubutun ya nuna, domin qara fayyace…
Read More
Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga Sufeto Janar na ‘Yansanda, Usman Alƙali Baba

Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga Sufeto Janar na ‘Yansanda, Usman Alƙali Baba

Daga NAFI'U SALISU Kamar yadda yake a dokar ƙasa, dukkan wani jami’in tsaro aikinsa shi ne kare rayuka da dukiyar al’ummar ƙasa. Don haka ne ma kowanne ma’aikacin Ɗansanda sai ya yi rantsuwa da littafin addininsa a yayin kama aikinsa na bada tsaro, cewar ya rantse da kundin tsarin mulkin ƙasarsa zai yi aiki a bisa doka da oda, wajen ƙare rayuka da dukiyar al’umma. Babu wata al’umma da za ta rayu cikin aminci face sai da hukuma a cikinta, kasancewar hukuma a cikin al’umma kuma shi ne ginshiƙin tafiyar da rayuwa cikin tsari, ta hanyar bin doka da oda.…
Read More
Me ke kawo taƙaddama tsakanin surukai a ƙasar Hausa?

Me ke kawo taƙaddama tsakanin surukai a ƙasar Hausa?

Daga AMINA YUSUF ALI Masu karatu sannu da jimirin karatun jaridarku mai farin jini, Blueprint Manhaja. A wannan mako muna tafe da bayanai a kan yadda alaqar tsakanin surukai take ƙara lalacewa a ƙasar Hausa har take zama ma kamar kishi ne tsakaninsu ba wai surukuta ba. Wannan abu ne mai matuar ban mamaki musamman idan muka yi la'akari da yadda alaƙar surukai take jiya a ƙasar Hausa. A zamanin da, ba komai sai kunya da tsakanin surukai a ƙasar Hausa. Kuma mafi yawan lokuta ma a gida guda suke zaune. Amma hakan bai sa ko da wasa suruka ta…
Read More
Abuja-Kaduna: Shin farin jinin jirgin ƙasa ya ragu?

Abuja-Kaduna: Shin farin jinin jirgin ƙasa ya ragu?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Kamar yadda hukumar sufurin jirgin ƙasa ta Nijeriya NRC a taƙaice ta ba da sanarwa a ranar Litinin ɗin da ta gabata za ta dawo da sufurin jirgin ƙasa tsakanin Abuja da Kaduna, hakan ya tabbata. Wannan kuwa tun dakatar da sufurin biyo bayan harin da ’yan ta’adda su ka kai wa ɗaya daga jiragen da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris na bana. Kafin dawo da sufurin a Litinin ɗin an so yin hakan a baya amma aka ɗage. Abun dubawa a nan shi ne yadda mutane su ka…
Read More
Game da gwajin maganin cutar mantuwa

Game da gwajin maganin cutar mantuwa

Ƙwayar magani ta farko da take taimakawa wajen rage lalacewar ƙwaƙwalwa ta samu yabo a matsayin mai muhimmanci. Binciken ya kawo ƙarshen shekarun da aka shafe ba tare da nasara ba kuma ta ba da damar samun maganin cutar Alzheimer's - nau'i mafi shahara na cutar mantuwa. Sai dai ya zuwa yanzu tasirin maganin na lecanemab ba shi da yawa kuma ana ta tafka muhawara game da aikinsa a rayuwar mutane. Ƙwayar na aiki ne tun a farko-farkon cutar, saboda haka wasu da dama maganin ba zai musu amfani ba idan ba a yi sa'ar gano ta da wuri ba.…
Read More
Dawo da jigilar jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna bayan harin ’yan bindiga

Dawo da jigilar jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna bayan harin ’yan bindiga

Assalam alaikum. Ina miƙa gaisuwa ta musamman ga Editan jaridar Blueprint Manhaja. Mun ji labarin jiragen ƙasa sun soma jigila tsakanin Abuja zuwa Kaduna karon farko tun bayan hare-haren da 'yan bindiga suka kai kan wani jirgin ƙasa a watan Maris ɗin da ya gabata. Jirgin ƙasan farko ya tashi daga Kaduna zuwa Abuja ranar Litinin ɗin nan da misalin takwas na safe inda ya isa tashar Iddu da misalin ƙarfe 10 da rabi. Kazalika, jirgin Abuja zuwa Kaduna ya tashi bayan ƙarfe tara na safe. Da aka je tashar jirgin da ke Abuja mutanen da suka shiga jirgin ba…
Read More
Ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa

Ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa, cin hanci da rashawa a matsayin barazana ga cigaban Nijeriya tare da yin kira da a ɗauki matakin gama gari a kan matsalar. Ya kuma hori ’yan Nijeriya da su guji cin hanci da rashawa, su rungumi gaskiya, su haɗa kai domin gina ƙasa mai inganci bisa gaskiya da riƙon amana. Mataimakin shugaban ƙasar, wanda ya bayyana hakan a Abuja a taron ƙaddamar da hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin qasa zagon ƙasa (EFCC) a hukumance na ƙungiyar makarantu, ya jaddada cewa duk wani cin hanci da rashawa a matsayin…
Read More
Sai yaushe ‘ya’yan Arewacin Nijeriya za su daina nuna halin ko-in-kula ga mahaifiyarsu?

Sai yaushe ‘ya’yan Arewacin Nijeriya za su daina nuna halin ko-in-kula ga mahaifiyarsu?

Daga MUHAMMAD NASEER LERE Allah Sarki. Daga zuciyata nake burin ina ma abinda nake saƙawa mafarki ne ko hasashe. Cikin sauri nayi firgigif nace in da mafarki ne da nayi burin farkawa daga wannan mummunan barci, inda kuma hasashe ne da na la'anci wannan kimiyya. Amma sai dai lamarin na kama da gaskiya a dukkan alamu na zahiri da ƙwaƙwalwa ke iya taskancewa. Me Ya Samu Mahaifiyarmu Arewa? Yanki me yalwar arziki, yankin da yake sheƙi da ganyayen amfani gona masu albarka. Ko Birtaniya ta san ana noma masara da dawa a cikin mahaifarmu. Hatta ƙasashen irin su Chana sun…
Read More
Samun man fetur a Arewa babbar nasara ce

Samun man fetur a Arewa babbar nasara ce

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Na san ko ba duka ba, amma akasarin 'yan Arewa sun shiga cikin murna da farin ciki, sakamakon gano man fetur da aka yi a Kolmani, wani ƙauye da ke iyakar Jihar Gombe da wani ɓangare na Jihar Bauchi. Ko da yake wasu ƙananan maganganu sun fara tasowa daga bakin wasu lauyoyi da ke Jihar Gombe suna ƙorafin cewa, yankin da ake magana a kai da ke kusa da samu man fetur bai shiga ƙauyen Barambu a ƙaramar hukumar Alƙaleri ta Jihar Bauchi ba, yana cikin Gombe ne. Har ma sun yi barazanar shiga kotu don…
Read More