Month: March 2021

Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Daga FARFESA UMAR LABDO ShimfiɗaIna yin wannan rubutu a matsayina na Babban Sakataren ƙungiyar FULDAN na ƙasa. FULDAN (Fulani Development Association of Nigeria) ƙungiya ce mai fafutuka don ci gaban Fulani a fagagen ilmi, al'adu, tattalin arziki da zamantakewa. An kafa ta a shekarar 1999, tana da wakilci a yawancin jihohin ƙasar nan kuma tana da alaƙa da ƙungiyoyi takwarorinta a ƙasashe makota. Ƙungiyar tana shirya tarukan wayar da kan Fulani da koya musu sana'o'i da sabbin dabarun kiwo don inganta sana'arsu. Haka nan tana gudanar da azuzuwan yaƙi da jahilci da koyon addini a rugage da ƙauyukan Fulani. GabatarwaAl'ummar…
Read More
Kwastam ta kama kayayyakin fasa-ƙwauri na sama da milyan N66

Kwastam ta kama kayayyakin fasa-ƙwauri na sama da milyan N66

Daga AISHA ASAS A ci gaba da yaƙi da harkokin fasa-ƙwauri da take yi, Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa a shiyya ta biyu (ZONE B) mai hedikwata a Kaduna, ta kama tarin haramtattun kayayyaki daga sassa daban-daban a shiyyar waɗanda a ƙiyasce kuɗinsu ya kai naira milyan N66,133,892.00. Shugaban hukumar a shiyyar 'Zone B' Comptroller AB Hamisu psc(+) shi ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da suka gudanar a Larabar da ta gabata, tare da nuna kayayyakin da suka kama ga manema labaran. Hamisu ya ce, kayayyakin da suka kama har da wuƙaƙe guda 180 a yankin…
Read More
Gwamna Sule ya nuna takaicinsa kan jinkirin kammala cibiyar lantarki

Gwamna Sule ya nuna takaicinsa kan jinkirin kammala cibiyar lantarki

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Nasarawa, Engineer Abdullahi Sule, ya nuna takaicinsa kan jinkirin da aka samu wajen kammala aikin cibiyar lantarki mai ƙarfin 330 KV a yankin Akurba. Gwamnan ya nuna damuwarsa ne bayan da ya kai ziyarar gani da ido domin duba yadda aikin kafa cibiyar ke gudana. Sule ya nuna rashin jin daɗinsa ga 'yan kwangilar da aikin gina cibiyar ke hannunsu, tare da bada tabbacin cewa gwamatinsa za ta tallafa don tabbatar da aikin ya kai ga gaci nan bada daɗewa ba. Bayanai sun nuna an samu jinkiri wajen kammala aikin ne sakamakon tsaiko da aka…
Read More
Sadiq Daba ya rasu

Sadiq Daba ya rasu

Daga AISHA ASAS Tsohon tauraron masana'antar fina-finai ta Nollywood, Sadiq Abubakar Daba ya rasu. Marigayin ya rasu ne a yammacin Larabar da ta gabata bayan ya yi doguwar jinyar fama da cutar daji. A halin rayuwarsa, an samu wasu fitattun 'yan Nijeriya da suka tallafa wajen ɗaukar nauyin kula da lafiyar marigayin, ciki har da hamshaƙin attajirin nan, wato Femi Otedola da Sanata Dino Melaye da Azuka Jebose dai sauransu. A matsayinsa na ɗan wasan kwaikwayo a halin rayuwarsa, Sadiq Daba ya samu kyaututtuka da dama, ciki har da lambar yabo daga Africa Movie Academy wadda aka ba shi a…
Read More
Gwamnati ta amince da kashe bilyan N797 kan aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano

Gwamnati ta amince da kashe bilyan N797 kan aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Zarartawa ta Tarayya, ta amince da kashe naira bilyan N797.2 domin aikin babbar hanyar Abuja-Kaduna-Kano. Da yake yi wa manema labarai ƙarin haske kan lamarin jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a Abuja, Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, ya ce aikin wanda da farko kwaskwsrima aka so yi wa hanyar amma aka canja shawara zuwa sake gina hanyar baki ɗayanta. Ministan ya ce canjin fasalin aiki da aka samu shi ya haifar da ƙari kan kuɗaɗen da aka yi nufin kashewa da farko daga naira bilyan N155 zuwa bilyan N797.2. Daga nan, ministan ya…
Read More
Harƙallar nukiliya: Iran ta ƙi amincewa ta tattauna da Amurka da Turai

Harƙallar nukiliya: Iran ta ƙi amincewa ta tattauna da Amurka da Turai

Daga AISHA ASAS Ƙasar Iran ta ce ba yanzu ne lokacin da ya dace a yi magana kan batun makaman nukiliya ba duba da halin da ƙasashen Amurka da Turai suka nuna. Iran ta ƙi amincewa da ta yi zaman tattaunawa da ƙashashen Amurka da Turai domin tattauna yadda za a farfaɗo da yarjejeniyar nukilya ta 2015, tana mai cewa dole sai Amurka ta ɗage duka takunkuman da ta ƙaƙaba mata kafin ta amince. A cewar mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran, Saeed Khatibzadeh, la'akari da halin da Amurka da wasu ƙasashen Turai suka nuna, ya sa Iran…
Read More
Cutar korona: Mutum 1 kacal ya harbu da korona cikin sa’o’i 48 a Madina

Cutar korona: Mutum 1 kacal ya harbu da korona cikin sa’o’i 48 a Madina

Daga WAKILINMU Rahotanni daga Ƙasar Saudiyya, sun nuna a tsakanin sa'o'i 48 da suka gabata, mutum ɗaya kacal aka samu ya harbu da cutar korona a birnin Madina. Bayanai sun nuna wannan wata alama ce da ke nuni da yiwuwar samun zarafin aiwatar da Hajjin bana. A halin yanzu dai maniyyata daga sassan duniya, na ci gaba da fatan samun nasarar karya lagon annobar korona domin bada damar yin Hajjin 2021 cikin salama.
Read More
Gudun hijira: Mutum milyan 2.6 suka rasa matsuguni a faɗin Nijeriya – cewar Hukuma

Gudun hijira: Mutum milyan 2.6 suka rasa matsuguni a faɗin Nijeriya – cewar Hukuma

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Ƙasa ta bayyana cewa a halin yanzu kimanin mutum milyan 2.6 ne suka rasa matsugunansu a faɗin ƙasa. Kwamishinan hukumar, Bashir Mohammed ne ya sanar da hakan a Litinin da ta gabata yayin ƙaddamar da shirin raba tallafin abinci ga mutum 7,500 waɗanda ibtila'i ya shafa a fadar gwamnatin jihar Kano. Garba ya ce 'yan gudun hijirar da ake da su a Kano mutane ne waɗanda matsalar tsaro da ambaliyar ruwa suka shafa daga jihohin Kudancin ƙasa. Ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kammala shirinta na sake tsugunar…
Read More