Month: March 2021

Musabaƙa: Ganduje ya gwangwanje Gwarzo da Gwarzuwa da kyautar milyan N5

Musabaƙa: Ganduje ya gwangwanje Gwarzo da Gwarzuwa da kyautar milyan N5

Daga UMAR M. GOMBE An kammala Musabaƙar Karatun Ƙur'ani ta Ƙasa karo na 35 a Kano tare da Muhammad Auwal Gusau daga jihar Zamfara a matsayin wanda ya zama gwarzo a ɓangare maza, yayin da Nusaiba Shu’aibu Ahmed daga Kano, ta zama gwarzuwa a ɓangaren mata. Albarkacin bajintar da suka nuna a yayin gasar ya sa Gwamnatin Kano ta yi wa jaruman biyu kyautar kuɗi ta Naira milyan N2.5 ga kowannensu. Da yake jawabi a wajen rufe gasar Asabar da ta gabata, Gwamnan Jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, a bisa wakilicin mataimakinsa Dr Nasiru Yusuf Gawuna, ya ce maza…
Read More
Hajjin 2021: NAHCON ta umurci jihohi su yi wa maniyyatansu rigakafin korona

Hajjin 2021: NAHCON ta umurci jihohi su yi wa maniyyatansu rigakafin korona

Daga AISHA ASAS Hukumar Hajji ta Nijeriya (NAHCON) ta ce ta samu wasiƙa daga Hukumar Bunƙasa Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA) tare da neman NAHCON ta bai wa duka Hukumomin Kula da Walwalar Alhazai na jihohin ƙasar nan 36 su yi wa maniyyatansu allurar rigakafin korona. A wata takardar sanarwa wadda Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike da Yaɗa Labarai na NAHCON, Sheikh Suleman Momo Imonikhe ya sanya hannu a ranar Lahadi, hukumar ta buƙaci ɗaukacin Hukumomin Kula da Walwalar Alhazai na jihohin ƙasar nan da su hanzarta yi wa baki ɗayan maniyyatansu allurar rigakafin korona. A cewar NAHCON yin allurar a kan…
Read More
Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu mai zamanta a Akure babban birnin jihar Ondo, ta umarci rundunar 'yan sandan jihar da ta biya diyyar Naira milyan N100 ga Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Agboola Ajayi. Laifin da ya haifar wa 'yan sandan hukuncin biyan diyyar shi ne, a ranar 20, Yuni, 2020 'yan sandan sun hana mataimakin gwamnan jihar na wancan lokaci, wato Agboola Jayi, fita daga Fadar Gwamnatin jihar wajajen ƙarfe 7 na dare, haka ma abin ya sake faruwa washe gari 21, Yuni, 2020 da misalin ƙarfe 9 na safe, bisa zargin cewa Ajayi na take-taken ficewa daga jam'iyyar APC.…
Read More
Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ce farfaɗo da yankin Tabkin Chadi zai taimaka wajen sassauta matsalar neman ƙetarawa zuwa Turai da matasa kan yi ta hanyar ketawa ta sahara. Buhari ya bayyana haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncin takwaransa na Chadi,  Marshal Idris Deby a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Asabar. A cewar Buhari, kimanin mutane milyan 30 ne matsalar tsukewar Tabkin Chadi ta shafa wanda a yanzu kashi 10 cikin 100 na girman tabkin ne ya yi saura idan aka kwatanta da asalin girmansa, inji sanarwar da mai magana da yawun shugaban,…
Read More
Shirye-shiryen Zuwan Ramadan

Shirye-shiryen Zuwan Ramadan

Daga IMAM YAHYA ALYOLAWI Kalmar Ramaḍan an tsago ta ne daga Kalmar “Ramad”, wadda ke nufin abin da ya duku da zafin rana. Larabawa kan kira tumakin da suka sha zafin rana a wajen kiwo da suna ‘ramidah’, zafin ranar da har kan yi sanadin lalacewar hantar dabbobin saboda tsananin zafi. Watan Ramadan ya samu sunansa ‘Ramadan’ ne saboda ƙona zunuban bayin Allah na gaskiya da yakan yi. Imām Qurtubi ya ce: ''Ramadan ya samu sunansa ne saboda ƙona kurakuran bayin Allah nagartattu da yake yi.” Abu Huraira (RA) ya ruwaito Annabi (SAW) na cewa: "Duk wanda ya azumci watan…
Read More
AFCON 2022: Super Eagles ta tsallake siraɗi

AFCON 2022: Super Eagles ta tsallake siraɗi

Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya, Super Eagles, ta samu nasarar shiga gasar Cin Ƙofin Ƙasashen Afirka (AFCON) wadda aka shirya gudanarwa a ƙasar Kamaru a 2022. Nijeriya ta samu wannan nasarar ce sakamakon kunnen doki na rashin jefa ƙwallo a raga da Lesotho da Saliyo suka yi a rana ta biyar na buga wasan cancantar shiga gasar.
Read More
CBN ya bai wa DisCos bilyan N33.4 don aikin rarraba mita, inji NERC

CBN ya bai wa DisCos bilyan N33.4 don aikin rarraba mita, inji NERC

Daga FATUHU MUSTAPHA Kawo yanzu, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bai wa Kamfanonin Rarraba Lantarki (DisCos) kuɗi Naira bilyan N33.4 daga cikin bilyan N59.2 da aka ware musamman domin aikin raba mita ga 'yan Nijeriya na Gwamnatin Tarayya, in ji Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC). Shugaban NERC, Engr Sanusi Garba ne ya bayyana haka yayin wata ganawa tsakanin Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sha'anin Lantariki da jami'an NERC da kuma wakilan DisCos, kwanan nan a Abuja. Garba ya ce shirin raba mitar wanda ake sa ran gidaje miliyan guda su ci moriyarsa a faɗin ƙasa tsakanin Oktoban 2020…
Read More
An gano mutum 51ɗauke da cutar tarin fuka a Binuwai

An gano mutum 51ɗauke da cutar tarin fuka a Binuwai

Daga UMAR M. GOMBE Dr Chubby Eze daga gidauniyar KNCV Foundation mai zaman kanta, ya ce mutum 51 ne aka tabbatar sun kamu da cutar tarin fuka (TB) daga cikin mutum 609 da aka yi musu gwaji a Makurdi babban birnin jihar Binuwai. Eze ya bayyana haka ne sa'ilin da yake amsa tambayoyin manema a Makurɗi a Juma'ar da ta gabata, tare da cewa an ɗauki samfurin mutane daga sassan ƙananan hukumomin jihar aka tafi da su cibiyoyin gwaji. Mr Dominic Alamkah wanda ke da hannu a shirin gwajin, ya shawarci waɗanda aka gano ɗauke da cutar da su tabbatar…
Read More
Ihejirika ya zama ɗan APC

Ihejirika ya zama ɗan APC

Daga WAKILINMU Shugaban Kwamitin Riƙo na APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya karɓi tsohon Shugaban Rundunar Sojoji Lt.Gen. Oyeabo Azubike Ihejirika (mai murabus) a jam'iyyarsu ta APC. Manhaja ta gano cewa, tun bayo na Ihejirika ya soma raɓar APC inda sai a wannan lokaci ya tsunduma cikinta a bayyane. Sanarwa da ta fito ta hannu Daraktan Yaɗa Labarai ga Buni, Mamman Mohammed, ta nuna an gabatar da Gen. Ihejirika a hukumance ga shugaban riƙo na jam'iyyar APC a Juma'ar da ta gabata a bisa jagorancin Gwamnan Jigawa, Alhaji Abubakar Badaru da Hon. Farouk Adamu Aliyu. Buniya ce,…
Read More
Yadda APC za ta iya ci gaba da mulki har shekara 32

Yadda APC za ta iya ci gaba da mulki har shekara 32

Daga IBRAHIM SHEME A ranar Talata, shugaban riƙo na jam’iyyar APC na ƙasa, Mai Mala Buni, ya faɗi wata magana wadda ta bar baya da ƙura. A cewar sa, jam’iyyar za ta ci gaba da mulkin Nijeriya har zuwa shekaru 32 masu zuwa; wato dai, har zuwa shekara ta 2053. Idan ka haɗa da shekaru shida da ta yi daga 2015 zuwa yau, za ka samu shekara 38 kenan. Na so a ce Mai Mala Buni ya faɗa mana kuma yadda mulkin jam’iyyar zai ƙare a cikin 2053 tunda dai a nan ya yi mata iyaka. Shin a lokacin ne…
Read More