Month: March 2021

Ƙara taɓarɓarewar harkar ilimi a Arewa

Ƙara taɓarɓarewar harkar ilimi a Arewa

Wani rahoton musamman da jaridar Blueprint ta buga a ranar Talata ta makon jiya ya nuna cewa a cikin watanni uku kacal ’yan bindiga sun ci gaba da kai hare-hare a makarantu aƙalla guda biyar a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-maso-gabas. Hakan ya haifar da damuwa a kan batun samar da ilimi ba kawai a waɗannan yankunan kaɗai ba har ma da lardin Arewa baki ɗayan sa. Rahoton ya ambaci jihohin Katsina, Zamfara da Kaduna a Arewa-maso-yamma da kuma Neja a Arewa-ta-tsakiya a matsayin inda ayyukan ta’addancin ’yan bindigar ya fi ta’azzara. Hari na baya-bayan nan da aka kai, an kai…
Read More
Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (3)

Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (3)

Daga FARFESA SALISU AHMAD YAKASAI Mafi kyawun fahimta ita ce abu ya zama da harshen mutum ake yinsa, idan ba haka ba to wasu abubuwa za su shige duhu. Tun kafin zuwan Turawa, a ƙasar Hausa ana amfani da shari’ar Musulunci ne. Wannan tsari na sharia a cikin Larabci yake, wanda ba kowa da kowa ya iya fahimta ba. Don haka da wuya jama’a su san kanta sosai da sosai, musamman ma idan wata matsala ta taso. Da Bature ya zo, shi ma dai ba ta sake zani ba. Ita tasa shariar a cikin Turanci take, ko haifaffen harshen ma…
Read More
‘Ya’yan mu da shaye-shayen kayan maye (2)

‘Ya’yan mu da shaye-shayen kayan maye (2)

Daga AISHA ASAS Idan ka sama wa ‘ya’yan ka uwa tagari to ka ba su kaso sittin bisa ɗari na tarbiyya. Uwa mai ilimi ce ta san fara tarbiyyar ‘ya’ya tun daga ɗaukar cikin su ne ba bayan haihuwa ba. Manzon (S.A.W) ya sanar da mu addu’a da ya ce ‘duk ma’aurata da su ka zo kwanciyar aure su ka karanta ta, idan an ƙadaro shigar ciki a wannan kwanciyar Allah zai nisanta ɗan da shaiɗan. “Allahumma janibnan shaiɗan ana, wa janibnan shaiɗan ala ma razaƙana” wannan kuwa mai ilimi ce kawai ta ke yin ta, ta ke tunawa mijin…
Read More

Muhammad bin Abdulkarim al Maghili (1440 – 1505)

Daga FATUHU MUSTAPHA An haifi Muhammad bin Abdulkarim al Maghili a alƙaryar Tabalbala dake Tilmisan na Ƙasar Magrib (Algeria) a shekarar 1440. Asalin sa ɗan ƙabilar Maghila ne daga babbar ƙabilar nan ta Berbers. Tun tasowar sa ya maida himma wurin neman ilmin addini a fannoni da dama, ya fara karatun sa a gidan su, daga baya da ya fara kaɓura sai ya shiga makarantar wani shehin malami da ake zancen sa a wannan lokaci, Imam Abdulrahman al Tha’alabi, da ya ƙara tumbatsa sai kuma ya koma karatu a ƙarƙashin wani bajimin malamin, Abu Zakariya Yahya ibn Yadir ibn ‘Atiq…
Read More
Yadda za a kula da tsaftar haƙora

Yadda za a kula da tsaftar haƙora

Daga AISHA ASAS Haƙora na ɗaya daga cikin ɓangarorin jiki da su ke bayyanar da tsafta ko ƙazantar mai su. Da yawa mu na ƙorafin bakin mu na wari ba dalili, alhali rashin kulawa da haƙori ya janyo hakan. Duk da cewa akwai matsalolin da ka iya haifar da warin baki ko da kuwa ana matuƙar kula da shi, kamar ciwon olsa da sauran su. Duk da haka kula da baki yadda ya kamata makami ne babba na yaƙar warin baki. Uwargida ki sani, saka makilin a magogi (burushi) ki goge baki da safe ba shi kaɗai bakin ki ke…
Read More
Ƙin samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro

Ƙin samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro

Daga NAJEEB MAIGATARI Kwanakin baya tattaunawa ta haɗa ni da wani aboki na, sai yake ce mun ai ana sane aka ƙi samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro (Malaria) duk da irin yanda kuwa cutar ta addabi musamman ƙananun yara da yanda ta ke kashe su. Har ya jefo mun wata tambaya; me yasa ba a damu da samar da rigakafin ‘Malaria’ ba, amma aka damu mutane da yi mu su rigakafin cutar shan inna (Poliomyelitis) duk da cewar yanzu ba a fama da ita? Maganar gaskiya shi ne a wancan lokacin ba ni da amsar tambayar shi, saboda…
Read More

Ilimin ‘ya mace ya fi na namiji muhimmanci – Saratu Garba

Saratu Garba Hajiya Saratu G. Abdul ƙwararriyar malamar jinya ce kuma babbar ɗaliba wadda ta zage damtse a ɓangaren karatun aikin jinya tun a nan gida Nijeriya har zuwa ƙasashen ƙetare. A yanzu haka ta na ƙasar Amurka ta na ci gaba da karatun digiri na uku a ɓangaren aikin jinya. Saratu Garba Abdullahi dai ta na sahun farko kuma gaba-gaba a rukunin matan da su ka samu ilimi mai zurfi a arewacin Nijeriya, musamman ma a ɓangaren aikin jinya da ta ke cigaba da neman ilimi da ƙwarewa a kai. An dai ce waƙa a bakin mai ita ta…
Read More
Kotu ta ɗaure Farfesa kan maguɗin zaɓe a Akwa-Ibom

Kotu ta ɗaure Farfesa kan maguɗin zaɓe a Akwa-Ibom

Daga UMAR M. GOMBE Wata babbar kotu a jihar Akwa-Ibom ta yanke wa Farfesa Peter Ogban hukuncin zaman kaso na shekara uku bayan da ta kama shi da laifin tafka maguɗin zaɓe. Kotu ta kama malamin da laifin shirya sakamakon zaɓe na ƙarya tare da sanar da sakamakon yayin babban zaɓen 2019 a matsayinsa na shugaban zaɓe a shiyyar Akwa-Ibom ta Arewa maso-yamma. Farfesan wanda malami ne a Jami'ar Calabar a Sashen Nazarin Harkokin Noma, ya tafka maguɗi wajen haɗa sakamon wasu ƙananan hukumomi guda biyu a wancan lokaci, wato ƙaramar hukumar Oruk Anam da Etim Ekpo. A can baya,…
Read More
‘Labarina’: Shirin fim ɗin Hausa mai dogon zango

‘Labarina’: Shirin fim ɗin Hausa mai dogon zango

Daga AYSHA SHAFI’EE a Kano Shahararren mai bada umarnin nan Malam Aminu Saira tare da ƙwararren marubucin finafinan Hausa Ibrahim Birniwa, sun zo da wani sabon shiri na Hausa mai taken ‘Labarina’, wanda ake nunawa a tasha mai farin jini ta Arewa24, shiri ne mai dogon zango da ke ɗauke da fuskokin jaruman da mu ka sani da ma kuma wasu sababbin fuska. Taurarin ciki sun haɗa da Nafisa Abdullahi a matsayin Sumayya, Nuhu Abdullahi a matsayin Mahmoud da kuma sabuwar fuska Maryam Isa Waziri a matsayin Laila. Sauran taurarin sun haxa da Hafsat Idris, Fatima Isa, Hadiza Muhammad, Ibrahim…
Read More
Gwamnati na shirin kashe tiriliyan N1 don gina masana’antu a ƙananan hukumomi 774

Gwamnati na shirin kashe tiriliyan N1 don gina masana’antu a ƙananan hukumomi 774

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta gabatar da ƙudirin ƙirƙiro da masana'antar cikin gida guda ɗaya a kowace ƙaramar hukuma daga ƙananan hukumomi 774 da ake da su a ƙasar nan. Gwamnatin ta ce tana sa ran kashe kuɗi naira tiriliyan N1 ne domin cim ma wannan ƙudiri. Ministan Ayyuka na Musamman, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan yayin ganawarsu da Kwamitin Majalisar Dattawa Kan Ayyuka na Musamman. Inda ya ce irin wannan masana'anta ta cikin gida za ta maida hankali ne wajen samar da kayayyakin masarufi don amfanin al'ummar yankin da aka kafa masana'antar a cikinta. Da yake…
Read More