Month: March 2021

Alaƙar Buhari da Tinubu tana ƙara armashi – Fadar Shugaban Kasa

Alaƙar Buhari da Tinubu tana ƙara armashi – Fadar Shugaban Kasa

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya musunta zargin da ake yaɗawa kan cewa ruwa ya yi tsami tsakaninsa da tsohon Gwamnan Jihar Legas kuma jigo a jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu. Buhari ya musunta zargin hakan ne ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu ya fitar inda ya bayyana cewa hakan ba gaskiya ba ne. Sanarwar ta nuna cewa, hasali ma alaƙar da ke tsakanin dattawan biyi sai armashi da ƙarƙo take ƙarawa. A cewar Shehu Garba, “Fadar Shugaban Ƙasa na faɗa da babbar murya cewa babu wani rashin jituwa a tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari…
Read More
Majalisa za ta binciki yadda aka kashe Dala bilyan $1.5 wajen gyaran matatar mai a Fatakwal

Majalisa za ta binciki yadda aka kashe Dala bilyan $1.5 wajen gyaran matatar mai a Fatakwal

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Wakilai ta Ƙasa ta umarci kwamitinta mai sanya ido kan albarkatun man fetur da ya gudanar da bincike domin sanin haƙiƙanin gaskiyar lamari game da matatar mai na Fatakwal wadda Gwamnatin Tarayya ta ware zunzurutun kuɗi har Dala bilyan $1.5 domin aikin gyaran matatar. Kazalika, majalisar ta farlanta wa kwamitin gudanar da bincike kan kuɗaɗen da aka kashe a baya wajen gyaran matatar mai na Fatakwal da sauran matatun mai da ake da su a faɗin ƙasa. Ɗaukar wannan mataki ya faru ne biyo bayan ƙorafin da ɗan majalisa Onofiok Luke, na jam'iyyar PDP daga…
Read More
JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta bada sanarwar ya zuwa ranar 8 ga Afrilu mai zuwa za ta soma gudanar shirin yin rajista na UTME/ Direct Entry (DE) na 2021 a faɗin ƙasa domin amfanin masu neman gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandare. A sanarwar da hukumar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta, Fabian Benjamin a Abuja, hukumar ta ce ana sa ran kammala shirin yin rajistan ya zuwa 15 ga Mayu. Yayin wani taro da jagororin hukumar suka gudanar a Talatar da ta gabata, sun cim ma matsayar cewa dole duk…
Read More
Ramadan 2021: Jerin sunayen limaman da za su jagoranci salloli a Masallacin Ka’aba

Ramadan 2021: Jerin sunayen limaman da za su jagoranci salloli a Masallacin Ka’aba

Hukumar Saudiyya ta fitar da jerin sunayen limaman da aka tsara za su jagoranci sallar Tarawi da ta Tahajjud a Masallacin Makka Mai Alfarma yayin azumin Ramadan na bana. Jaridar Hajj Reporters ta wallafa jerin sunyen limaman a shafinta na twita kamar haka: Sheikh Abdul Rehman Al SudaisSheikh Saud Al ShuraimSheikh Abdullah Awad Al JuhanySheikh Maher Al MuaiqlySheikh Bandar BaleelahSheikh Yasir Al Dossary
Read More
APC za ta shafe shekara 32 riƙe da mulkin ƙasa, cewar Buni

APC za ta shafe shekara 32 riƙe da mulkin ƙasa, cewar Buni

Daga WAKILINMU Shugaban Kwamitin Riƙo na Ƙasa na Jam'iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce jam'iyyarsu na da niyar yin mulkin ƙasa nan da shekaru 32 masu zuwa. Buni ya bayyana haka ne a wajen taron ƙaddamar da wani kwamitin APC na musamman mai mambobi 61, ƙarƙashin shugabancin Gwamnan Jigawa Badaru Abubakar, tare da ɗora wa kwamitin nauyin fito da hanyoyin da za a bi wajen gyara zaman jam'iyyar tasu. Kazalika, Buni ya ce ana buƙatar kwamitin ya gudanar bincike a tsakanin mambobin jam'iyya da ma al'umma baki ɗaya sannan ya fitar da manufa da burin…
Read More
Attah ya yi ƙarin haske kan batun biyan harajin sayen jiragen sama

Attah ya yi ƙarin haske kan batun biyan harajin sayen jiragen sama

Daga AISHA ASAS Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa ta yi ƙarin haske tare da kore raɗe-raɗin da aka yi ta yaɗawa kan batun biyan harajin VAT da Kwastam Duti kan sayen jiragen sama da sauran kayayyakin jiragen. Idan dai za a iya tunawa, wasu kafafen yaɗa labarai sun ruwaito Shugaban Air Peace Airline na cewa har yanzu Hukumar Kwastam na karɓar harjin Duti da na VAT duk da umarnin hani ga hakan da Gwamnatin Tarayya ta gindaya wanda a cewarsa hakan na maida wa kamfanonin sufurin jiragen sama hannun agogo a baya. Sai dai mai magana da yawun hukumar…
Read More
Kaduna: Ana ci gaba da binciken gano sarakunan da suka ɓace

Kaduna: Ana ci gaba da binciken gano sarakunan da suka ɓace

Daga FATUHU MUSTAPHA A halin da ake ciki, jami'an tsaro a jihar Kaduna sun bazama bincike domin gano wasu masu rawani su uku da suka ɓata a masarautar Atyap cikin ƙaramar hukumar Zangon Kataf waɗanda aka sace su bayan kammala wani taron sulhu da suka gudanar a Lahadin da ta gabata. A cewar Gwamnatin Jihar Kaduna, mutum shida ne suka ɓata da farko a kan hanyarsu ta komawa gida bayan taron. Ta ce jami'an tsaro sun samu nasarar gano mutum guda daga cikinsu kuma sun miƙa shi ga 'yan sanda, kana wasu mutum biyu daga ciki sun tsere daga hannun…
Read More
Kuɗin makamai: Majalisar Wakilai ta gayyaci Attahiru da Emefiele

Kuɗin makamai: Majalisar Wakilai ta gayyaci Attahiru da Emefiele

Daga FATUHU MUSTAPHA Majalisar Wakilai ta Ƙasa ta buƙaci Hafsan Hafsoshi, Lieutenant General Ibrahim Attahiru da Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, da su bayyana a gaban wani kwamitinta ya zuwa watan gobe. Kwamitin Majalisar ƙarƙashin shugabancin Hon Olaide Akinremi, ya gayyaci waɗanda lamarin ya shafa ne a Litinin da ta gabata bayan da suka ƙi amsa masa gayyatar farko da ya yi musu. Hon Bede Eke shi ne wanda ya gabatar da ƙudirin a gayyato mutum biyun zuwa gaban Majalisar, wanda ya nuna ɓacin ransa kan rashin amsa gayyatar kwamitin majalisar a baya. 'Yan majalisar mambobi ne a…
Read More
Ƙoƙarin da Nijeriya ke yi don kauce wa sake fama da annobar korona, Ministan Lafiya

Ƙoƙarin da Nijeriya ke yi don kauce wa sake fama da annobar korona, Ministan Lafiya

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnatin Tarayya ta bada haske kan wasu matakan da ta ɗauka domin tabbatar da Nijeriya ba ta yi fama da ɓarkewar annobar korona karo na uku ba. Yayin da wasu ƙasashen duniya suka soma sake fama da bugun annobar karo karo na uku, Ministan Lafiya, Dr Osagie Ehanire ya ce Nijeriya za ta ci gaba da aikin gwaje-gwaje da take yi domin ganowa, killacewa da kuma kula da waɗanda suka kamu da cutar. Ehanire ya bayyana haka ne a Litinin da ta gabata a Abuja yayin da kwamitin Shugaban Ƙasa kan Yaƙi da Cutar Korona ke…
Read More