Nishadi

Manyan fitattun jaruman Kannywood na 2024

Manyan fitattun jaruman Kannywood na 2024

DAGA MUKHTAR YAKUBU Shekarar ta 2024 ta zo ƙarshe kuma a yanzu an shiga sabuwar shekara ta 2025 ga mai yawan rai. Abubuwan da dama sun faru na ci gaba a cikin masana'antar finafinai ta Kannywood tun daga farkon ta zuwa ƙarshen ta waɗanda idan aka ce za a yi bayanin su ɗaya bayan ɗaya za a ɗauki tsawon lokacin ana bayani a kansu. Amma da yake an ce abin da yawa, wai mutuwa ta je kasuwa, bari mu ɗauki wani ɓangare mafi muhimmanci a cikin harkar fim musamman ga masu kallo. Wannan ɓangaren kuwa shi ne na jaruman da…
Read More
Hukumar NDLEA ta yi ram da wani jarumin fim kan safarar tabar wiwi 

Hukumar NDLEA ta yi ram da wani jarumin fim kan safarar tabar wiwi 

Daga AISHA ASAS  Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa NDLEA ta kama wani mai fasahar zance, Emeka Emmanuel Mbadiwe da laifin safarar kashi 33 na Loud, wato tabar wiwi mai nauyin kilogiram 17.30. Hakan ya fito ne a wata sanarwa da Daraktan yaɗa labarai da bayar da shawarwari na hukumar Femi Babafemi ya fitar a ranar Lahadi. A cewar Babafemi, Mbadiwe, wanda kuma ɗan wasan finafinan Hollywood da na Nollywood ne da Amurka ta horar, an kama shi ne a ɗakinsa na otal ɗin Lekki ranar Juma’a 27 ga watan Disamba, 2024, biyo bayan kama abokin…
Read More
Taron ranar Jammaje: Mawaƙan Kannywood sun yi bajekolin fasahar su

Taron ranar Jammaje: Mawaƙan Kannywood sun yi bajekolin fasahar su

DAGA MUKHTAR YAKUBU A ranar alhamis 26 ga Disamba ne aka yi taron bikin ranar Jammaje wato 'Jammaje Day' wanda aka saba gudanar da shi a duk ƙarshen shekara. Taron na ƙarshen shekara ta 2024 wanda aka gudanar da shi a babban ɗakin taro na Musa Abdullahi da ke sabuwar Jami'ar Bayero a Kano, ya samu halartar jama'a daga sassa daban daban na faɗin ƙasar nan. Tun da farko da yake jawabin maraba da baƙi, Malam Kabiru Musa Jammaje, ya nuna farin cikin sa a game da yadda ya ga taron bikin na shekarar 2024 ya yi tasiri fiye da…
Read More
Duk wanda yake sana’ar fim ba ya talauci – Danbaba 

Duk wanda yake sana’ar fim ba ya talauci – Danbaba 

"Yanayin yadda jarumai maza da mata ke ƙoƙarin bada tarbiyya na birge ni" Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Karibullahi Abdussalam Mahmud da aka fi sani da Danbaba jarumi ne a masana'artar finafinai ta Kannywood, wanda masu karatu za su fi tunawa da shi a matsayin Danbaba a fim ɗin nan mai dogon zango wato, 'Dadinkowa' na tashar Arewa24. A tattaunawarsa da wakilinmu a Kano, Ibrahim Hamisu, za ku ji tarihinsa da kuma yadda ya yi finafinai fiye da 20 a ƙanƙanin lokaci. Don haka ku gyara zama, don karanta yadda tattaunawar ta kasance: MANHAJA: Za mu so ka gabatar mana…
Read More
Ko fim ɗin ”Muhalli” zai iya canza akalar harkar finafinai a Kannywood?

Ko fim ɗin ”Muhalli” zai iya canza akalar harkar finafinai a Kannywood?

DAGA MUKHTAR YAKUBU An ɗauki tsawon lokacin da masu kallon finafinan Hausa musamman na Kannywood suke kan yadda finafinan suka tsaya iya bayar da labarin soyayya da nuna ta'addanci, domin kusan duk wani fim da za su kalla sai su ga jigon labarin soyayya ne da 'yammata da samari, ko kwartanci ko kuma nuna harkar daba, hakan ya sa ake ganin kamar masu shirya fim sun mayar da soyayya da cin amana da ta'addanci kamar wasu muhimman abubuwa a cikin Al'adun ƙasar Hausa. Sai dai a yanzu za a iya cewa an fara samun sauyi da kuma canzawar tunani ga…
Read More
A lokacinmu bayan wahala da magana da manya-manyan kalmomin Turanci a fim, sannan ne za a biya mu 15,000, inji Jarumi Chiwetalu Agu

A lokacinmu bayan wahala da magana da manya-manyan kalmomin Turanci a fim, sannan ne za a biya mu 15,000, inji Jarumi Chiwetalu Agu

Daga AISHA ASAS  Kamar yadda ake cewa, mutanen da su ne suka san yadda ake nema, don haka su suka san darajar kaɗan da ake biyan su. Idan muka kalli yadda ababe suka sawwaka, da yadda hanyoyin samu suka yawaita, za mu gane cewa, mutanen da albarka suka fi mu ba yawa ba. Da wannan ne tsohon jarumi da har yau ake tafiyar da shi Chiwetalu Agu, ya janyo hankalin matasan jarumai don su san irin sa'ar da suka yi a harkar fim, ma'ana ko kusa ba sa shan wahala kamar yadda suka sha a harkar ta fim, kuma abinda…
Read More
Yadda aka gudanar da taron bikin Kalankuwar Afirika KILAF AWARD 2024

Yadda aka gudanar da taron bikin Kalankuwar Afirika KILAF AWARD 2024

(Ci gaba daga makon jiya) DAGA MUKHTAR YAKUBU A farkon bude taron da misalin ƙarfe tara na safe ƙwararre kuma masani a kan harkar fim Yomi Olugbod shi ne ya gabatar da bita a kan aikin manajan shirya fim , wato 'Production Manager' inda ya yi dogon bayani a game da alaƙar manajan shirya fim da furodusa darakta da kuma jaruman fim. Haka nan ya bada misalai da dama a kan tasirin managan shirya fim da kuma ingancin fim da kuma rashin ingancin sa. Nasiru B Muhammad, shi ne ya yi sharshi tare da ƙarin bayani bayan Mista Yomi Olugbod…
Read More
An gudanar da bukukuwan Kalankuwar Afrika ta KILAF 2024 a Kano

An gudanar da bukukuwan Kalankuwar Afrika ta KILAF 2024 a Kano

DAGA MUKHTAR YAKUBU Kamar dai kowacce shekara, a bana ma an yi taron bikin Kalankuwar Afirika mai taken KILAF AWARD 2024 wanda ake gudanarwa a Kano wanda a bana she ni karo na 8 wato 'Kano Indigenous Languages of Africa film Market & Festiɓal'. A ranar Litinin 25 ga Nuwamba 2024 aka fara gudanar da bikin inda aka shafe tsawon kwanaki 5 ana yi. A rana ta farko dai an buɗe taron ne da yin lakcoci a sahin koyar da aikin jarida na Jami'ar Bayero in da manyan masana a kan aikin jarida da kuma harkar fim suka gabatar da…
Read More
Ba a iya aktin ne kawai mata za su iya samun ɗaukaka a Kannywood ba – Mansurah Isah 

Ba a iya aktin ne kawai mata za su iya samun ɗaukaka a Kannywood ba – Mansurah Isah 

Daga MUKHTAR YAKUBU  A ci gaba da tattaunawa da jaruma kuma darakta a masana'antar finafinai ta Kannywood, Mansurah Isah, mai karatu zai ji yadda take son ta amfanar da matan Kannywood daga tallafin da NITDA ta ba su, don ganin sun tsayu da ƙafafunsu ta yanda ko shahara ta yi masu kaye suna da madogara da za ta hana su shiga mawuyacin hali. Idan mai karatu na biye da mu, kuma bai manta ba, mun fara tattaunawa da jaruma Mansurah kan yadda ta samu wannan tallafi, da kuma yadda matan Kannywood ke shiga mawuyacin hali yayin da suka bar fitowa…
Read More
 Za mu yi amfani da tallafin da NITDA ta bamu wajen ci gaban matan Kannywood – Mansurah Isah

 Za mu yi amfani da tallafin da NITDA ta bamu wajen ci gaban matan Kannywood – Mansurah Isah

DAGA MUKHTAR YAKUBU A sakamakon tallafin da Mansurah Isah ta samu daga National Information Technology Development Agency (NITDA) ta sha alwashin kawo sauyi a masana'antar domin su samu su ma su dogara da kansu a maimakon su tsaya suna fitowa a matsayin jarumai, wanda kuma daga an daina yayin su ko suka yi aure kuma shi kenan sana'ar ta su ta tsaya, don haka take ganin a yanzu dama ta samu da za su koyar da mata duk wasu harkoki na sana'ar fim don a kawar musu da tunanin cewar sai aktin kawai za su iya.  A cikin tattaunawar da…
Read More