04
Dec
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gamayyar ƙungiyoyin farar hula CSOs, guda goma da ke aiki domin tabbatar da sahihin zaɓe a Nijeriya, sun buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta, INEC, da ta gaggauta yin bincike kan rijistar masu zaɓe a Jihar Filato. Ƙungiyar, a wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, ta ce ta gano sama da ƙananan yara dubu 84 da suka yi wa rijistar zabe a ƙananan hukumomi 17 da ke jihar. Vanguard ta rawaito cewa ƙungiyoyin lura cewa, INEC, bisa la'akari da sashe na 19 (1) na dokar zaɓe, 2022, ta wallafa rajistar masu…