Ra’ayin Manhaja

Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai

Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai

A kwanakin baya ne wata Babbar Kotun Tarayya da ta ke zamanta a garin Fatakwal taJihar Ribas ta samu wasu mutane biyar da laifin satar man fetur da kuma safarar man fetur ba bisa ƙa’ida ba kuma ba tare da lasisin da ya dace ba sannan ta yanke musu hukunci daban-daban. Wannan dai na ɗaya daga cikin yawaitar satar mai da ake tafkawa a harkar mai da iskar gas wanda bisa ga dukkan alamu hakan ba wai a fannin mai kaɗai ya ke kawo cikas ba, har ma da ƙasa baki ɗaya. Tony Elumelu, Shugaban Kamfanin Bankin UBA kuma Shugaban…
Read More
Matsalar watsi da manyan ayyukan raya ƙasa

Matsalar watsi da manyan ayyukan raya ƙasa

A cikin wasu ’yan shekaru da suka gabata, Shugaban Ma’aikatar tantancewa tare da kula da kwangilolin gwamnati (Bureau of Public Procurement), Injiniya Emeka Eze, ya bayyana wa Majalisar Dattijai cewa, akwai kimanin ayyuka 19,000 a wurare daban-daban na faɗin ƙasar nan da aka yi watsi da su. Waɗannan ayyuka, sun haɗa da na Gwamnatin Tarayya da kuma na jihohi waɗanda ko dai gwamnati da ta fare su ba ta samu damar kammalawa ba, ko kuma gwamnatin da ta gaji ayyukan ta yi watsi da su. Ko shakka babu, akwai yiwuwar adadin nasu ma ya fi haka da ba don Shugaban…
Read More
ASUU: Yajin aiki ba shi ne kaɗai mafita ba

ASUU: Yajin aiki ba shi ne kaɗai mafita ba

Matakin da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta yanke na tsawaita yajin aikin da ta fara har na tsawon makonni takwas, ya dagula wa ɗalibai, iyaye da kuma masu ruwa da tsaki a harkar ilimi lissafi, domin yajin aikin zai ƙara dagula al'amuran ilimi a jami'o'in ƙasar nan. Da ya ke yin biris da yadda harkar ilimi da tarbiyya ke durƙushewa a sanadin yajin aikin malaman jami’o’i, shugaban ASUU na yanzu, Farfesa Emmanuel Osodeke, wanda ya bayyana yajin aikin na watanni biyu a makon da ya gabata, ya bayar da hujjar cewa, “bayan ɗaukar rahotanni kan ayyukan da manyan jami’an gwamnati…
Read More
Inganta cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko

Inganta cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko

Da ya ke tabbatar da halin rashin kula da harkokin kiwon lafiya a matakin farko ke ciki, Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko na Ƙasa, Dakta Faisal Shuaib, a ranar 14 ga Fabrairu, ya ce, sama da kashi 70 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko na Ƙasar (PHC) ba su da ingantattun ababen more rayuwa, magunguna da sauran abubuwan kula da lafiya. Shuaib, wanda ya yi maganar a wajen rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin hukumar da wata ƙungiyar farar hula ta ‘Connect Development’ (CODE), kan ƙarfafa al’amuran kiwon lafiya, ya kuma ce…
Read More
Tabbatar da yanke hukunci don daƙile cin hanci da rashawa a Nijeriya

Tabbatar da yanke hukunci don daƙile cin hanci da rashawa a Nijeriya

Hukuncin da aka yanke wa tsohuwar ministar albarkatun ruwa, Sarah Reng Ochekpe, tare da wasu mutane biyu a baya-bayan nan, wani muhimmin cigaba ne a yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya. Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC ta kama su ne a ranar 22 ga watan Fabrairun 2022 a kan tuhume-tuhumen da ake yi masu. Sauran mutane biyun da aka yankewa hukuncin sune Evan Leo Sunday Jitong da Raymond Dabo, waɗanda suka kasance mataimakin darakta a yaƙin neman zaɓen Goodluck/Sambo 2015 da kuma tsohon shugaban riƙo na jam’iyyar PDP a jihar…
Read More
Tashin gwauron zabin kayan masarufi a Nijeriya

Tashin gwauron zabin kayan masarufi a Nijeriya

Magidanta a mafi yawan jihohin Nijeriya na cigaba da ɗanɗana kuɗarsu sakamakon matsananciyar tsadar kayan abinci a kasuwannin ƙasar. Wannan kuwa na zuwa ne daidai lokacin da har yanzu al’umma ke fama da wahalar ƙarancin man fetur da kuma tsadarsa. Mutane suna ta bayyana takaici kan wannan yanayi da aka samu kai a ciki, inda batun ya zama abin tattaunawa a zauruka da dama na shafukan sada zumunta. Tuni dai farashin kayan masarufi dama sauran kayayyakin amfanin yau da kullum ya yi tashin goron zabi abin da ya sa jama'a da dama suka shiga cikin ƙuncin rayuwa. A yanzu haka…
Read More
Matsalar damfara a yanar gizo

Matsalar damfara a yanar gizo

Babu makawa ga duk mai mu'amala da yanar gizo (wato internet) ko wayar salula ya san matakan kariya game yadda waɗansu ɓatagari ke baza tarko ta kowacce irin dama suka samu, don su damfari jama'a. Idan muka ce yanar gizo, to a nan mu na nufin ko wanne fanni na yanar gizo. Shin kai ma'abocin shiga yanar gizo ne, don karanta labarai ko mai binciken ilmi ko ma'abocin kafofin sada zumunci da dai sauransu? Yau za mu kawo hanyoyin da su ka fi shahara wajen yin damfara a yanar gizo, kuma sanin su zai taimaka ma ka wajen tsallake tarkonsu,…
Read More
Ruɗani kan shigo da gurɓataccen fetur a Nijeriya

Ruɗani kan shigo da gurɓataccen fetur a Nijeriya

A Nijeriya masu ababan hawa sun shiga tsaka mai wuya sakamakon ƙarancin man fetur a gidajen mai da kuma samun gurɓataccen man da wasu ke sayarwa, abin da ya sa kasuwar bayan fage tashi. Ruɗani a kan shigo da gurɓataccen man fetur ɗin dai ya jefa ’yan Nijeriya a hali na rashin tabbas a kan man da aka kwashe makwanni ana fuskantar ƙarancinsa, wanda dama aka danganta da alamu na sake fuskantar ƙari. A ranar Talata ne sabuwar Hukumar kula da harkokin Sarrafa man fetur da tacewa da sufuri ta Nijeriya wato ‘Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority’ ta…
Read More
Sana’a: Babbar hanyar samun ingantacciyar rayuwa

Sana’a: Babbar hanyar samun ingantacciyar rayuwa

A wannan makon, Blueprint Manhaja za za ta jawo hankalin matasanmu maza da mata ne game da muhimmancin yin sana’a kowace iri ce, in dai ba ta sava wa doka ba, ko ta saɓa ƙa’idojin da gwamnati ta kafa. Mun taɓa yin bayani makamancin wannan a watannin baya, saboda muhimmancinsa ne ya sa muka ga ya kamata mu ɗan sake waiwayarsa. Sana’a ga duk magidanci, ko wani mai neman ya zama yana neman na kansa, ta zama wajibi bisa la’akari da halin da ake ciki a duniyarmu ta yau. Domin ba za a iya cewa gwamnati za ta iya sama…
Read More
Matsalar watsi da gine-ginen da ba a kammala ba

Matsalar watsi da gine-ginen da ba a kammala ba

Watsi da gine-ginen da ba a kammala ba, ya zama ruwan-dare a jihohin wannan ƙasa da ma Babban Birnin Tarayya, Abuja. Ko shakka babu, wannan wata gazawa ce ko abin kaico ga wannan ƙasa tamu baki ɗaya. A wani bincike na kwana-kwanan nan, ya bayyana kimanin sama da gine-gine 665 da aka gaza kammalawa a Abuja, da ya haɗa da gidajen zama da kuma na kasuwanci. Abu ne mai sauƙi ka ga an yi watsi da katafaren gida na Milyoyin kuɗi a Abuja. Haka nan, baya ga rashin kyan gani da waɗannan gine-gine da aka yi watsi da su ke…
Read More