Ra’ayin Manhaja

Kawo ƙarshen cutar Kwalara

Kawo ƙarshen cutar Kwalara

A cikin rahotonta na baya-bayan nan, Cibiyar Kula da Cututtuka ta Nijeriya ta sanar da jimillar mutane 19,228 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara, ciki har da mutuwar mutane 466 a shekarar 2022. A ra'ayin wannan jarida, wannan lamari ne mai firgitarwa da ya kamata gwamnati ta ɗauki nauyinsa daqile shi a kowane mataki. Kwalara cuta ce da ake saurin kamuwa da ita da ta ke haifar da gudawa da amai. Ana kamuwa da ita daga najasa ta hanyar gurvataccen abinci, abin sha, da rashin tsafta, kuma yana haifar da rashin ruwa a jikin ɗan adam. Yawan masu…
Read More
Nijeriya da ƙasashe 12 mafi ci gaba a Afirka

Nijeriya da ƙasashe 12 mafi ci gaba a Afirka

Wani rahoto na baya-bayan nan da Insider Monkey ya fitar ya nuna cewa Nijeriya ba ta cikin jerin ƙasashe 12 da suka fi samun ci gaba a nahiyar Afirka. A cewar rahoton mai taken, “ƙasashe 12 Mafi Cigaba a Afirka”, Afirka na ɗaya daga cikin nahiyoyin da suka fi arziki a duniya wajen samar da albarkatun qasa. Abin ban mamaki kuma, nahiyar na ɗaya daga cikin yankuna mafi ƙarancin ci gaba a duniya. Ƙasashen da suka shiga jerin sun yi amfani da albarkatun qasarsu wajen inganta tattalin arzikinsu. Irin waɗannan qasashe su ne; Ghana, Zimbabwe, Masar, Maroko, Afirka ta Kudu,…
Read More
Gargaɗin NDLEA kan ta’ammali da miyagun ƙwayoyi

Gargaɗin NDLEA kan ta’ammali da miyagun ƙwayoyi

A baya-bayan nan Shugaban Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Muggan Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), Mohamed Buba Marwa, ya ce, a cikin watanni 22 hukumar ta kama fiye da ƙwayoyin tramadol miliyan 100 na haramtacciyar hanya da sauran muggan ƙwayoyi masu cutarwa. Yawan shan waɗannan ƙwayoyi na varna da rayuwar al'umma musamman matasa, wanda ake saran al’umma za su fahimci ɓarnar da matsalar ke haifarwa. Shugaban NDLEA, wanda ya bayyana hakan a yayin bikin bayar da lambar yabo da kuma ƙawata sabbin jami’an da aka ƙara wa girma a Abuja, ya ce, “A cikin ƙanƙanin lokaci, hukumar ta kama masu…
Read More
Taƙaita cire tsabar kuɗi da sauran batutuwa

Taƙaita cire tsabar kuɗi da sauran batutuwa

Manufar cire kuɗaɗe da Babban Bankin Nijeriya CBN ya yi a baya-bayan nan, wanda zai taqaita adadin kaɗaɗen da mutane da kamfanoni za su iya fitarwa a kowane mako, ya sha suka daga ’yan siyasa da sauran ’yan Nijeriya. Sabuwar manufar ta sanya mafi girman cire kuɗi a kowane mako akan Naira 100,000 ga kowane mutum da 500,000 ga ƙungiyoyi da kamfanoni. Manufar cire tsabar kuɗin ta zo ne bayan da CBN ya sake fasalin takardar Naira 200, 500, da 1000. Manufar babban bankin zai duba yawan kuɗaɗen da ake samu a wajen tsarin banki. A cewar CBN, kusan kashi…
Read More
Barazanar jefa ƙuri’ar ƙananan yara

Barazanar jefa ƙuri’ar ƙananan yara

Ƙuri’ar ’yan ƙasa da shekaru 18 wata ɓarna ce a tsarin zaɓen Nijeriya. Shekarun da suka cancanci shiga zaɓe a ƙasar sune ’yan shekaru 18 zuwa sama. Sai dai a lokacin zaɓe, ana barin yara su kaɗa ƙuri’a a wasu sassan ƙasar. Wani lokaci ma matattu ma suna yin zaɓe. Kuma wannan shine tushen fara rigingimu. Lokacin da aka ba wa yaran da ba su kai shekarun jefa quri'a damar jefa ƙuri'a ba, hakan yana kawo cikas ga sahihancin tsarin zaɓe kuma yana sanya alamar tambaya kan sakamakon aikin. A kwanakin baya, gamayyar ƙungiyoyin farar hula 10 (CSO) sun koka…
Read More
Ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa

Ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa, cin hanci da rashawa a matsayin barazana ga cigaban Nijeriya tare da yin kira da a ɗauki matakin gama gari a kan matsalar. Ya kuma hori ’yan Nijeriya da su guji cin hanci da rashawa, su rungumi gaskiya, su haɗa kai domin gina ƙasa mai inganci bisa gaskiya da riƙon amana. Mataimakin shugaban ƙasar, wanda ya bayyana hakan a Abuja a taron ƙaddamar da hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin qasa zagon ƙasa (EFCC) a hukumance na ƙungiyar makarantu, ya jaddada cewa duk wani cin hanci da rashawa a matsayin…
Read More
Ƙalubalen yaran da ba sa zuwa makaranta

Ƙalubalen yaran da ba sa zuwa makaranta

Dangane da ƙaruwar yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya, wanda a halin yanzu aka ƙiyasta su miliyan 20, Tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana lamarin a matsayin wani abu mai matuƙar tayar da hankali. A cewarsa, samun irin wannan adadi mai yawa na yara ba tare da tsarin ilimi ba, zai haifar da tarnaƙi ga ƙaruwar masu tada ƙayar baya da ’yan ta’adda a nan gaba. Tsohon shugaban, wanda ya yi magana a wani taron ƙoli na ilimi na manyan makarantu na ƙasa da Majalisar Wakilai ta shirya, a wani ɓangare na ƙoƙarin magance ƙalubalen…
Read More
Barazana ga zaɓen 2023

Barazana ga zaɓen 2023

Duk da cewa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da hafsoshin tsaron ƙasar sun tabbatar da cewa za a gudanar da zaɓen 2023 cikin lumana duk da matsalar tsaro da ake fuskanta a wasu sassan ƙasar. Sai dai kuma rahotanni sun nuna cewa ’yan Nijeriya na cikin fargaba game da yawaitar taɓarɓarewar tsaro a ƙasar. Hakazalika ana fargabar gudanar da zaɓen a wasu sassan ƙasar da har yanzu ba a daƙile matsalar ba. Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta kuma tabbatar da taɓarɓarewar yanayin tsaro a cikin sanarwar da ta fitar a baya-bayan nan cewa rumfunan zaɓe 242 da…
Read More
Canja fasalin Naira: Abubuwan da suka taso

Canja fasalin Naira: Abubuwan da suka taso

Sanarwar da Babban Bankin Nijeriya CBN ya bayar a ranar 26 ga Oktoba, ta sauya fasalin takardar kuɗin ƙasar ta Naira a ƙoƙarin daidaita tasirinta, daidai lokacin da tattalin arzikin ƙasar ke cikin mawuyacin hali ta janyo cece-kuce. Babu dai zato ba tsammani babban bankin Nijeriyar ya sanar da aniyarsa ta sake fasalin takardar kuɗin Nairar, tare kuma da bayar da wa'adi na lokacin da za a ƙaddamar da sabbin kuɗin zuwa ranar 15 ga watan Disambar wannan shekara. Wannan dai ya nuna sun kammala duk wani aiki a kan wannan aniya tasu, abin da zai shafi takardun kuɗi na…
Read More
Ambaliyar ruwa da ƙarancin abinci a Nijeriya

Ambaliyar ruwa da ƙarancin abinci a Nijeriya

Farashin kayayyakin abinci ya yi tashin goron-zabi a Nijeriya musamman a yankin kudancin ƙasar sakamakon matsalar ambaliyar ruwa wadda ta haifar da cikas wajen safarar abincin daga arewacin ƙasar zuwa kudanci, al'amarin da ke ƙara jefa jama'a cikin halin ni-’yasu. Ambaliyar wadda ta yi sanadiyar mutuwar mutane 600 tare da raba miliyan biyu da muhallansu, ta haddasa asara ga 'yan kasuwa da ke safarar hajojinsu daga Arewa zuwa kudanci sakamakon yadda ta mamaye hanyoyin da motoci suka saba ratsawa. A cikin wata sanarwa da ta fitar a baya-bayan nan, Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi nuni da cewa, ana sa ran…
Read More