Ra’ayin Manhaja

Magance cutar Sikila a Nijeriya

Magance cutar Sikila a Nijeriya

A Nijeriya, an ware ranar 19 ga watan Yunin kowace shekara domin tunawa da ranar cutar sikila ta duniya. Ana bikin ranar ne don wayar da kan jama'a na duniya kowace shekara da nufin havaka ilimin jama'a da fahimtar cutar sikila da ƙalubalen da marasa lafiyar da danginsu da masu kula da su ke fuskanta. Kafin mu san ya cutar ta ke, dole mu fara sanin yadda ake kamuwa da ita. Jini wanda ake gani a zahiri idan mutum ya ji ciwo ko kuma ya yanke jikinsa yana ɗauke da abubuwa iri daban–daban, kamar su 'plasma', 'Red Blood Cells' (RBC),…
Read More
Ranar bayar da gudunmawar jini ta duniya

Ranar bayar da gudunmawar jini ta duniya

A ranar Talata, 14 ga Yuni, 2022, ce ta yi daidai da Ranar Bada Tallafin Jini ta Duniya (WBDD). Da farko dai an yi bikin ne a shekara ta 2005, wannan rana ta musamman ta duniya ta kasance ƙarƙashin jagorancin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), da ƙungiyar agaji ta Red Cross da Red Crescent don gode wa waɗanda suka bada gudunmawar jininsu don ceto rayukan bil'adama ba tare da neman a biya su ba. Jaridar Blueprint Manhaja ta duba muhimmancin wannan batu na bada jini, fargabar da wasu ke bayyanawa kan wannan al'amari da kuma yadda wataƙila za a sake…
Read More
Yayin da Shugaba Buhari ke cika shekarar ƙarshe na wa’adin mulkinsa…

Yayin da Shugaba Buhari ke cika shekarar ƙarshe na wa’adin mulkinsa…

A ranar 29 ga Mayu, 2022, Shugaba Muhammadu Buhari ya cika shekaru bakwai daga cikin shekaru takwas da aka zaɓe shi a karo na biyu. A daidai wannan lokacin ne a shekara mai zuwa zai kammala wa'adin mulkin da kundin tsarin mulkin ƙasar ya amince da shi na tsawon wa'adi biyu ga duk wanda zai yi aiki a wannan matsayi na siyasa a Nijeriya. Bisa la'akari da wannan muhimmin cigaba, fadar shugaban ƙasa, a ranar 28 ga Mayu, 2022, ta fitar da takardar da ta kira ‘Takardar Gaskiya: Manyan Nasarorin da aka cimmawa kan Cika Shekaru Bakwai na Gwamnatin Buhari’.…
Read More
Samo ’yanci ga fasinjojin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da aka sace

Samo ’yanci ga fasinjojin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da aka sace

Barazanar baya-bayan nan da ’yan ta'adda ke yi na kashe fasinjojin jirgin ƙasa da aka sace idan gwamnati ta gaza biyan buƙatunsu cikin kwanaki bakwai, dole ne a mayar da hankali a cikin gaggawa. ’Yan ta’addan da suka yi garkuwa da fasinjojin da suke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga Maris, 2022, sun bai wa Gwamnatin Tarayya damar tattaunawa da su tare da neman ganin an sako waɗanda aka sace. Sun yi gargaɗin cewa rashin yin hakan zai sa a kashe Waɗanda aka sacen. ’Yan ta’addan Waɗanda suka gabatar da buƙatar ta hannun Malam Tukur Mamu, kakakin…
Read More
Gangancin mahaya babur a titunan Nijeriya

Gangancin mahaya babur a titunan Nijeriya

Barazanar mahaya babur musamman ma ’yan acaɓa a kan manyan tituna a sassan Nijeriya na ƙara ɗaukar hankali. Baya ga tuƙin ganganci da kawo matsala ga sauran masu amfani da hanyar, sun kuma vullo da wani sabon salo na zama ’yan fitina. Kwanan nan a Abuja, an ba da rahoton mutuwar mutane da dama, a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ’yan kasuwa a kasuwar Dei Dei da gungun ’yan iska da suka haɗa da ’yan acaɓa da wasu ɓarayin titi. A ƙarshe abin ya yi muni inda aka ƙare da fashe-fashen shagunan mutane, gidaje, da ababen hawa baya ga…
Read More
Babu tsawaita jaddawalin INEC!

Babu tsawaita jaddawalin INEC!

A kwanakin baya ne shugaban majalisar ba da shawara ta jam’iyyun siyasar Nijeriya (IPAC), Yabagi Sani ya yi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ta ƙara wa’adin gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasar Nijeriya. A yayin da ya ke yin wannan kiran, ya ce, matsalar shiyya-shiyya da canjin mulki ya mamaye tattaunawar da jam’iyyun siyasa ke yi wanda ya sa ya zama dole a tsawaita wa’adin ta yadda jam’iyyun za su yi aiki sosai. Ya ƙara da cewa, da wannan ne jam’iyyu za su iya gudanar da ayyuka masu ɗaukar lokaci kamar tuntuɓar…
Read More
Ceto kamfanonin jiragen sama daga rugujewa

Ceto kamfanonin jiragen sama daga rugujewa

Kamfanonin jiragen sama na Nijeriya sun fitar da wata sanarwar cewa, daga ranar Litinin 9 ga Mayu, 2022, za su rufe ayyukansu, saboda tsadar man jiragen da ake sayarwa akan Naira 700 kan kowace lita. Wata sanarwa da aka fitar tare da sanya hannun dukkan shugabannin jiragen a ƙarshen makon da ya gabata, ta shawarci jama’a masu tafiya da ke da niyyar tashi da su yi wasu shirye-shirye na daban, don guje wa maƙalewa a tashoshin jiragen saman ƙasar. A cewar ma’aikatan, bayan lokaci, farashin man jiragen sama (JetA1) ya tashi daga Naira 190 kan kowace lita zuwa Naira 700…
Read More
Kawar da zazzaɓin cizon sauro

Kawar da zazzaɓin cizon sauro

Haqiqa Nijeriya da mafi yawan ƙasashen kudu da hamadar Sahara har yanzu ba su yi nasara a yaƙin da ake yi da zazzaɓin cizon sauro ba, cutar da ake ganin kamar annoba ce a mafi yawan yankunan. A cewar Cibiyar Kula da Zazzaɓin Ciwon Sauro (SMO), kashi 76 cikin 100 na al’ummar Nijeriya suna zaune ne a wuraren da sauro suka yi yawa, sannan kashi 24 na zama a yankunan da kamuwa da cutar ke da ɗan sauƙi. A kwanakin baya, duniya ta yi bikin ranar zazzaɓin cizon sauro ta duniya mai taken, 'Sabbin hanyoyin da za a rage yaɗuwar…
Read More
Damina: Uwa ma-ba-da-mama

Damina: Uwa ma-ba-da-mama

Bahaushe na cewa ‘Damina Uwar Albarka!’ Wannan magana ta Malam Bahaushe haka ta ke, domin a lokacin damina ne ake samun albarkatu masu yawa, musamman a fannin abinci, a lokacin ne ake samun abincin da ake ci, wanda kuma abinci ne jigon rayuwar kowane halitta. Kuma alhamdu lillahi, ya zuwa yanzu za mu iya cewa damina ta kankama, sai dai fatan Allah ba mu dacewa. Duk da cewa a wannan zamani na damina, lokaci ne da ake samun albarkatu masu yawa, to haka kuma akwai wasu bala’o’i da sukan samu ɗan adam, waɗanda a lokuta da dama ma har abin…
Read More
Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai

Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai

A kwanakin baya ne wata Babbar Kotun Tarayya da ta ke zamanta a garin Fatakwal taJihar Ribas ta samu wasu mutane biyar da laifin satar man fetur da kuma safarar man fetur ba bisa ƙa’ida ba kuma ba tare da lasisin da ya dace ba sannan ta yanke musu hukunci daban-daban. Wannan dai na ɗaya daga cikin yawaitar satar mai da ake tafkawa a harkar mai da iskar gas wanda bisa ga dukkan alamu hakan ba wai a fannin mai kaɗai ya ke kawo cikas ba, har ma da ƙasa baki ɗaya. Tony Elumelu, Shugaban Kamfanin Bankin UBA kuma Shugaban…
Read More