Ra’ayin Manhaja

Rikicin Sudan da tsaron Nijeriya

Rikicin Sudan da tsaron Nijeriya

Ga waɗanda ke yawan kiran a yi yaƙi a Nijeriya su kalli abinda ke faruwa a Sudan. Tun a ƙarshen makon da ta gabata ne tashe-tashen hankula suka ɓarke a Sudan. Ƙarar harbe-harbe a Khartoum babban birnin Sudan da jirage masu saukar ungulu sun yi ta harba makamai a wuraren zaman jama'a, tsawon ƙarshen mako ana gwabza ƙazamin faɗa tsakanin sojoji da dakarun sa-kai. Asalin faɗan shi ne rikicin da ya daɗe ana takun-saka tsakanin manyan hukumomin soja biyu na ƙasar. Wato asalin sojin Sudan wadda ita ce rundunar soja ta gwamnatin ƙasa baki ɗaya, sai kuma rundunar sa kai…
Read More
Amincewar Gwamnatin Tarayya kan amfani da riga-kafin cutar Maleriya

Amincewar Gwamnatin Tarayya kan amfani da riga-kafin cutar Maleriya

Yaƙi da zazzaɓin cizon sauro ya sami ƙarin ƙarfafawa bayan amincewar Gwamnatin Tarayya a kwanan nan don amfani da riga-kafin cutar zazzaɓin cizon sauro ga yara. Masana kimiyya a Jami'ar Oxford ne suka samar da riga-kafin zazzaɓin cizon sauro na R21/Matrix. Amincewar da gwamnati ta yi na riga-kafin ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Ghana ta zama ƙasa ta farko da ta amince da riga-kafin, wanda aka ce tana da kashi 80 cikin ɗari. Cibiyar Serum Institute of India Pvt Ltd ce ta ƙera riga-kafin zazzaɓin cizon sauro. Da ta ke bayyana hakan ga manema labarai a Abuja, Darakta-Janar na…
Read More
Batun inganta tsaro a mulkin Buhari

Batun inganta tsaro a mulkin Buhari

A lokacin da wa'adin mulkin Shugaba Muhammadu Buhari na biyu ke daf da ƙarewa, jama'a da dama ma cigaba da tafka muhawara akan batun tsaro a ƙasar cikin ’yan shekarun baya-bayan nan. A hirar da ya yi a gidan talbijin ta Channels a ranar Litinin ɗin makon nan, Mai Magana da Yawun Shugaban Buhari, Femi Adesina ya ce, Muhammadu Buhari zai bar Nijeriya cikin aminci da gagarumin ci gaba a ɓangaren tsaro, idan an kwatanta da yadda ya same ta a farkon mulkinsa. Kalaman Femi Adesinan dai sun jawo cece-kuce a tsakanin al'ummar ƙasar, ciki har da masana harkokin tsaro,…
Read More
Haɗarin yaɗa ƙabilanci

Haɗarin yaɗa ƙabilanci

Tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo, ya yi Allah-wadai da ƙabilanci da kuma barazanar da ’yan ƙabilar Ibo ke fuskanta kafin zaɓen 2023 da kuma bayan kammala zaɓen 2023 a Legas. Dattijon wanda ya yi magana a ranar Asabar a Awka a yayin bikin cika shekara guda a kan karagar mulki na Gwamna Chukwuma Charles Soludo na jihar Anambra, ya yi gargaɗi kan kyamar ƙabilar Ibo, ya kuma buƙaci ɗaukacin ’yan Nijeriya da su zauna lafiya da juna. Hakazalika, ƙungiyar ƙoli ta al’adun ƙabilar Ibo 'Ohanaeze Ndigbo Worldwide', ta yi tir da hare-haren ba gaira ba dalili da aka…
Read More
Ƙarancin takardun kuɗin Naira

Ƙarancin takardun kuɗin Naira

Ƙarancin Naira na cigaba da shafar ’yan Nijeriya da ’yan kasuwa duk da cewa Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bin umarnin da Kotun Ƙoli ta yanke na cewa tsofaffin takardun kuɗin Naira za su ci gaba da yaɗuwa a kasuwa har zuwa ƙarshen shekara. Taɓarɓarewar sha'anin kuɗin dai na ci gaba da ƙaruwa duk da umarnin da CBN ya baiwa bankuna na ci gaba da fitar da tsoffin takardun kuɗi kamar yadda Kotun Ƙoli ta yanke. Wani bincike da masana da ƙungiyar masu tunani na CBN suka yi na sake fasalin manufofin Naira da kuma tasirinsa ga ’yan ƙasa da…
Read More
Matsalar mutuwar mata masu juna biyu a Nijeriya

Matsalar mutuwar mata masu juna biyu a Nijeriya

Matsalar mace-macen mata da yara a lokacin ciki ko haihuwa dai ta jima ta na ci wa ƙasashe masu tasowa tuwo a ƙwarya. Alal misali, ƙasashen da suka ci gaba mata 7 zuwa 15 ne ke mutuwa a cikin mata masu juna 100,000 daga lalurar ciki ko haihuwa; amma a ƙasashe masu tasowa har wajen mata 100-300 ne kan rasu sanadiyyar lalurorin ciki ko haihuwa. Wani sabon rahoton da hukumomin Majalisar Ɗinkin Duniya suka fitar na cewa a duk minti biyu mace na mutuwa a duniya yayin da take ɗauke da juna biyu ko haihuwa. Hakan na ƙara nuna rashin…
Read More
Tinubu a matsayin shugaba da zai jagoranci Nijeriya

Tinubu a matsayin shugaba da zai jagoranci Nijeriya

An ayyana Bola Tinubu, mai shekara 70 a duniya a matsayin mutumin da ya lashe zaɓen shugaban ƙasan Nijeriya mafi ɗaukar hankali tun bayan mulkin sojoji a shekarar 1999. Tinubu, wanda ake kallo a matsayin jajirtaccen ɗan siyasa da ya kawo cigaba a jihar Legas, cibiyar kasuwancin ƙasar, ya yi nasara ne kan babbar jam'iyyar adawa mai fama da ɓaraka da kuma ɗan takara na uku da ke da magoya baya matasa. A ranar 29 ga watan Mayu, na wannan shekara ta 2023, zai maye gurbin Shugaba Muhammadu Buhari a kan mulki. Nijeriya, ƙasa mafi yawan al'umma a Afirka na…
Read More
Ƙalubalen da ke gaban shugaban Nijeriya da za a zaɓa

Ƙalubalen da ke gaban shugaban Nijeriya da za a zaɓa

Kasancewarta mafi girman tattalin arziki kuma mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka, mai sama da mutum miliyan 214, hakan ya sa duk wani abu da ya faru a Nijeriya yake yin tasiri a faɗin nahiyar. Masu kaɗa ƙuri'a za su zaɓi sabon shugaban ƙasa bayan kwashe shekara takwas ƙarƙashin mulkin Shugaba Muhammadu Buhari, sai dai duk wanda ya yi nasara akwai wasu manyan ƙalubale da zai yi fama da su. A wannan ra'ayin, jaridar Blueprint Manhaja za ta kawo maku wasu muhimman abubuwan da suka fi damun masu kaɗa ƙuri'a. A shekarar da ta gabata, kamar sauran al'ummar duniya, ’yan…
Read More
Ƙarancin fetur da gabatowar zaɓe

Ƙarancin fetur da gabatowar zaɓe

Duk da alqawarin da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya yi na tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe a wannan shekara, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta yi gargaɗin cewa matsalar ƙarancin man fetur da ake fama da shi na iya kawo cikas ga zirga-zirgar kayayyaki da ma’aikata a ranakun zaɓe, idan ba a gaggauta magance shi ba. Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana fargabar da ke tattare da zaɓen 2023 a wani taron tuntuvar juna da Ƙungiyar Ma’aikatan Sufurin Jiragen Ruwa ta Ƙasa (NURTW) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ruwa ta Nijeriya (MWUN) kan zaɓen da…
Read More
Gargaɗi akan zaɓen 2023

Gargaɗi akan zaɓen 2023

A daidai lokacin da ake tunkarar babban zaɓen ƙasar na 2023, Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), Tarayyar Turai (EU) da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) sun yi gargaɗi game da tashe-tashen hankula a lokacin zaɓe da sauran laifuffuka da ka iya kawo cikas ga gudanar da zaɓen. Ƙungiyoyin sun yi magana kan illolin tashe-tashen hankula a lokacin zaɓen da kuma yin gargaɗin cewa illar na iya yin muni ga yankin da ma nahiyar Afirka bakiɗaya. Sun kuma jaddada cewa idan aka samu tarzoma a yayin zaɓen, babu wata ƙasa a yammacin Afirka da za ta iya shawo kan…
Read More