Labarai

Kamfanin Boska ya raba wa masu babura hular kwano 698 a Gombe

Kamfanin Boska ya raba wa masu babura hular kwano 698 a Gombe

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Don ganin an rage yawan mutuwa a sanadiyar hatsari, Kamfanin Dexa da suke yi maganin nan na Boska ya raba wa mahaya babura sama da 600 hular kwano kyauta a Gombe. Kamfanin na Boska ya yi haɗin gwiwa ne da hukumar kiyaye hatsura ta ƙasa FRSC reshen Jihar Gombe don ganin cewa suna da ruwa da tsaki wajen faɗakar da masu baburan muhimmancin sanya hular kwano ga duk mai hawa babur. Da ya ke jawabi a lokacin raba hular kwanon Kwamishinan Ma’aikatar tsaron cikin gida na jihar Gombe Laftanal Abdullahi Bello mai ritaya, ya…
Read More
Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙalubalanci Obasanjo kan kalamansa ga dimukraɗiyyar Nijeriya

Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙalubalanci Obasanjo kan kalamansa ga dimukraɗiyyar Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Fadar Shugaban Ƙasa ta zargi tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo kan halin da dimokraɗiyyar Nijeriya ke ciki a halin yanzu. Da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin, Bayo Onanuga, mai bai wa Shugaba Tinubu shawara kan yaɗa labarai da dabaru, ya nuna cewa Obasanjo na da tasiri kai tsaye kan irin dimokuradiyyar da al’umma ke yi a yau. Ya ce tasirin Obasanjo ya kai wa’adi biyu a matsayin shugaban qasa, na farko a matsayin shugaban farar hula daga 1999 zuwa 2007 sannan a matsayin shugaban qasa na soja daga 1976 zuwa 1979.…
Read More
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Nasarawa inda ta tabbatar da nasarar Gwamna Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. A watan Oktoban da ya gabata ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a jihar ta soke nasarar Gwamna biyo bayan ƙarar da Jam'iyyar PDP a jihar da ɗan takarar Ombugadu suka shigar suna ƙalubalabtar sakamakon zaɓen. Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta ce ƙaramar kotun ƙarƙashin jagorancin Ezekiel Ajayi, ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke musamman wajen yin amfanin da bayanan shaidu ba bisa…
Read More
Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Daga BASHIR ISAH Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya garzaya Kotun Ƙoli domin ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na soke nasarar da ya samu a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Kano. Wannan wata alama ce mai nuni da Gwamna Abba ba zai bari ya yi ƙasa a gwiwa bs wajen kare kujerarsa a matsayin Gwamnan Kano. Haka nan, wannan shi ne matakin kotu na ƙarshe da Yusuf zai ɗauka don kare kujerar tasa. Kwannan ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe, inda ta sauke Gwamna Abba na Jam'iyyar NNPP daga kujerar gwamnan Kano tare da…
Read More
Gwamna Lawal ya kama hanyar farfaɗo da martabar ilimi a Zamfara

Gwamna Lawal ya kama hanyar farfaɗo da martabar ilimi a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sha alwashin gwamnatinsa za ta maido da martabar ilimi a jihar. Ya bada wannan tabbacin ne a wajen taron ƙaddamar da aikin gyaran makarantun da suka lalace da kuma gina sabbi jihar. Sanarwar da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, Gwamnatin Jihar na bai wa ɓangaren ilimin jihar fifiko ne domin cika alƙawarin da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe. Sanarwar ta ƙara da cewa, fara aiwatar da wannan ƙudiri ya yi daidai da manufar ayyana Dokar ta Ɓaci a fannin ilimi jihar. Haka…
Read More
Kotu ta bada belin Emefiele kan N300m

Kotu ta bada belin Emefiele kan N300m

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a yankin Maitama a Abuja, ta bada belin tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele. Kotu ta bada belin nasa ne kan kuɗi Naira miliyan 300. Yayin zaman shari'a da kotun ta yi a ranar Laraba, Mai Shari'a Hamza Muazu ya buƙaci Emefiele da ya gabatar da shaidu guda biyu, kuma tilas shaidun ya zamana sun mallaki kadarori a yankin Maitama. Kodayake Emefiele bai halarci zaman kotun ba sakamakon yana tsare a gidan yarin Kuje tun a makon jiya. Kimanin makonni biyu da suka gabata wata Babbar Kotu a Abuja ta…
Read More
Al’ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa kan gwamnatina, cewar Gwamna Lawal

Al’ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa kan gwamnatina, cewar Gwamna Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya ce yana da yaƙinin al'ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa game da gwamnatinsa. Lawal ya samu tabbacin hakan ne ganin yadda masoyansa a birnin Gusau suka fito don tarbarsa bayan da ya dawo daga ziyarar aiki a ranar Litinin. Sanarwar da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce bisa la'akari da irin dandazon jama'ar da suka tarbi Mai Girma Gwamna, hakan manuniya ce game da ƙwarin gwiwar da al'ummar jihar ke da shi a kan gwamnatin jihar. A cewarsa, gwamnatin Gwamna Lawal ta samu soyayyar al'ummar jihar waɗanda…
Read More
Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna kaɗuwarsa bisa rasuwar fitaccen daraktan finafinan Hausa na Kannywood, Aminu S. Bono. Gwamna Abba ya bayyana hakan ne ta bakin Babban Sakataren Hukumar Tace Adabi na Jihar Kano, Abba El-Mustapha, wanda ya wakilce shi a wajen jana’aizar marigayin da aka gudanar ranar Talata, 21 ga Nuwamba, 2023, a maƙabartar Dandolo da ke birnin Kano. A ganawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala jana’izar, Abba ya kuma bayyana Marigayi Bono a matsayin mutumin ƙwarai mai haƙuri da yakana tare da kyakkyawar mu’amula, wanda kuma ya kai ƙololuwa wajen fikira…
Read More
Babban Hafsan Tsaro bai mutu ba, yana cikin ƙoshin lafiya – Hedikwatar Tsaro

Babban Hafsan Tsaro bai mutu ba, yana cikin ƙoshin lafiya – Hedikwatar Tsaro

Daga BASHIR ISAH Hedikwatar Tsaro da ke Abuja ta ƙaryata rahoton da ya ce Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya kwanta dama. Da safiyar wannan Talatar wasu jaridu suka yaɗa rahoto kan cewa, Musa ya rasu. Sai dai a martanin da ta mayar ta shafinta na X, Hedikwatar Tsaron ta ce rahoton ba gaskiya ba ne, don kuwa Babban Hafsan na raye kuma cikin ƙoshin lafiya. “Saɓanin wani rahoton ƙarya da aka yaɗa, Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa, yana nan a raye kuma cikin ƙoshin lafiya," in ji Hedikwatar. Sanarwar ta ƙara da cewa, jama'a su zamo…
Read More
Shugabannin tsaro sun bayyana gaban Majalisar Wakilai

Shugabannin tsaro sun bayyana gaban Majalisar Wakilai

Daga BASHIR ISAH Shugabannin fannin tsaro da Sufeto Janar na 'Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, sun bayyana a gaban Majalisar Wakilai domin tafka muhawara. Jami'an sun haɗa da Shugaban Tsaro (CDS), Janar Christopher Musa; Shugaban Rundunar Sojoji (COAS), Laftanal-Janar Taoreed Lagbaja; Shugaban Sojin Sama (CAS), Air Marshal Hassan Abubakar da kuma Shugaban Sojin Ruwa (CNS), Vice Admiral Emmanuel Ogalla. Wannan na zuwa ne biyo bayan caccakar da jami'an suka sha daga 'yan majalisar a makon jiya na tura wakilai da suka yi maimakon zuwa da-kai. A makon da ya gabata 'yan majalisar suka murtuƙe fuska na rashin zuwa zauren majalisar…
Read More