Kasashen Waje

Rikicin Sudan: Saudiyya ta zama ƙasa ta farko wajen kwashe ‘ya’yanta

Rikicin Sudan: Saudiyya ta zama ƙasa ta farko wajen kwashe ‘ya’yanta

Daga BASHIR ISAH Wani jirgin ruwan Ƙasar Saudiyya ya isa Jidda bayan da ya yi jigilar 'yan ƙasar da suka maƙale a Ƙasar Sudan sakamakon rikicin da ƙasar ke fama da shi. A cewar tashar talabijin ta Jidda, “Jirgin ruwan farko da ya kwaso 'yan ƙasar daga Sudan ya isa gida ɗauke da mutum 50 tare da wasu daga maƙwabtan ƙasar." Bayanai sun ce an hangi wasu jiragen ruwa na ƙasashe daban-daban a Kogin Maliya ɗauke da mutum 108 daga Sudan wanda ake sa ran su isa ƙasashensu ba da jimawa ba. Wannan nasarar da Saudiyya ta samu ya sa…
Read More
Har yanzu ban dawo hayyacina ba kan abinda Hakimi ya min – Hiba

Har yanzu ban dawo hayyacina ba kan abinda Hakimi ya min – Hiba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Matar Achraf Hakimi, ɗan ƙwallon ƙungiyar PSG kuma ɗan asalin ƙasar Moroko, wato Hiba Abouk, ta ce, abinda Hakimi ya mata ta kadu sosai, wanda hakan ya sa har yanzu ba ta dawo hayyacinta ba. A shekarar 2020 ne dai suka yi aure da Hakimi inda a yanzu suna da yara biyu, amma sun rabu, matar ta nemi Hakimi ya ba ta rabin dukiyarsa, amma sai lauyanta ya gano Hakimi da sunan mahaifiyarsa ya ke ajiye kadarorinsa. A zantawar da ta yi da kafar Elle, Hiba ta bayyana cewa rabuwarsu ba abu ne me sauƙi ba…
Read More
Indiya ta zarta Chana da yawan jama’a

Indiya ta zarta Chana da yawan jama’a

Indiya za ta wuce Chana a matsayin qasa mafi yawan jama'a a duniya a ƙarshen watan Yuni, alqalumman Majalisar Ɗinkin Duniya sun nuna cewa, hakan zai haifar da babban qalubale ga ƙasar da ke ƙoƙarin samar da ababen more rayuwa daidai lokaccin da ta ke fama da rashin isassun ayyukan yi ga miliyoyin matasa. Alqaluman sun nuna cewa, yawan al'ummar Indiya ya kai sama da biliyan 1.400 inda ya haura adadin yawan al’ummar Ƙasar Chana da miliyan uku, wanda ke da adadin sama da mutum biliyan ɗaya, inji rahoton hukumar kula da yawan jama’a ta Majalisar Ɗinkin Duniya. A baya…
Read More
Saudiyya ta kama ‘yan ci-rani sama da 16,000

Saudiyya ta kama ‘yan ci-rani sama da 16,000

Hukumomin Saudiyya sun ce sun kama baƙin haure 16,407 da suka shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba, a yankuna daban-daban na ƙasar cikin mako ɗaya. Jaridar Saudi Gazette ta ambato ma'aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar na cewa an kama mutanen ne bayan wani samamen haɗin gwiwa da jami'an tsaro suka ƙaddamar a sassa daban-daban cikin wannan wata na Ramadan. Kamen ya haɗa da mutunen da suke zaune a ƙasar ba tare da izini ba, da mutunen da ba su da takardun shiga ƙasar, sai kuma mutunen da suka sava ƙa'idojin aiki na Saudiyya. Ma'aikatar ta ce ta kama wasu…
Read More
Donald Trump ya gurfana gaban kotu, ya musanta zargin da ake yi masa

Donald Trump ya gurfana gaban kotu, ya musanta zargin da ake yi masa

Tsohon Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya musanta zarge-zargen laifuka 34 da ake tuhumar sa da aikatawa, bayan wani bincike da ya gano cewa ya bai wa wata jarumar fina-finan batsa mai suna Stormy Daniels, toshiyar baki. Trump wanda ya miƙa kansa ga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Amurka da ke Manhattan, shi ne Shugaban Ƙasar na farko da ya fara fuskantar tuhuma da ta danganci aikata manyan laifuka. Rahotanni na nuni da cewa, Trump ya ba wa jarumar fina-finan batsar kuɗin toshiyar bakin ne a shekarar 2016. Bayan da ya bayyana gaban kotu, tsohon shugaban na Amurka ya wallafa…
Read More
Tashar TRT ta ƙaddamar da sashin Hausa da wasu harsuna uku

Tashar TRT ta ƙaddamar da sashin Hausa da wasu harsuna uku

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kafar yaɗa labarai ta ƙasar Turkiyya, wato Turke's Public Broadcaster (TRT), ta ƙaddamar da ƙarin ɓangarori guda uku da za su riƙa yaɗa labarai cikin harshen Hausa da Swahili da Turanci da kuma Faransanci. Tashar ta TRT ta yaɗa taron masu ruwa da tsaki a harkar na nahiyar Afrika da aka gudanar ranar Juma’a a birnin Istanbul babban birnin ƙasar Turkiyya. Tun da farko an ƙaddamar da tashar wacce za ta dinga kawo labarai da rahotanni bisa tsarin dokar yaɗa labarai a gaban mambobin ƙungiyar watsa labarai ta nahiyar Afirka da manyan jami’an gwamnati da…
Read More
Za mu hukunta ƙasashen da suka bijire wa yaƙi da ɗumamar yanayi – MƊD

Za mu hukunta ƙasashen da suka bijire wa yaƙi da ɗumamar yanayi – MƊD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta amince da ɗaukar wani mataki da zai fara hukunta ƙasashen da ke fitar da hayaƙi da sinadaran da ke gurɓata muhalli ba kuma tare da ɗaukar matakin da ya dace ba. A wata ƙuri’ar jin ra’ayi tsakanin ƙasashe mambobin majalisar mai cike da tarihi da aka kaɗa a ranart Laraba, da tsibirin Vanuatu ya bada shawara, ta kuma tanadi damar gurfanar da ƙasar da aka samu da saɓa wannan doka, gaban kotun duniya musamman idan wannan ƙasa ta yi kunnen ƙashi wajen bada gudunmawa a yaƙi da gurvatar muhalli. Da yake jawabi bayan kaɗa ƙuri’ar, Firaministan…
Read More
Mahajjatan Umarah 20 sun rasu, 29 sun jikkata a hatsarin mota a Makka

Mahajjatan Umarah 20 sun rasu, 29 sun jikkata a hatsarin mota a Makka

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Saudiyya sun ce, wasu mahajjatan Umarah su 20 sun riga mu gidan gaskiya, sannan 29 jikkata sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da su a Makka. Bayanai sun ce mahajjatan sun gamu da wannan jarrawar ce a kan hanyarsu ta zuwa aikin Umara a Makka a ranar Litinin. Wata majiya ta ce mai yiwuwa adadin waɗanda suka rasa ransu ya ƙaru duba da yanayin raunukan da wasunsu suka ji. Waɗanda lamarin ya shafa sun haɗa da 'yan asalin Saudiyya da kuma baƙi daga sauran sassan duniya da suka tafi Saudiyya don yin Umarah. An…
Read More
Sanatoci sun fatattaki sanatan da bai taɓa halartar zaman majalisa ba

Sanatoci sun fatattaki sanatan da bai taɓa halartar zaman majalisa ba

’Yan majalisar Japan sun kori wani sanata daga Majalisar Dattawan ƙasar bayan ya kwashe wata bakwai bai halarci zaman majalisar ba. Sanatan, wanda fitacccen mai amfani da shafin YouTube ne, ya zama ɗan majalisa na farko da aka kora ba tare da ya tava shiga zauren Majalisar Dattawan ba tun da aka zaɓe shi. Sanatocin sun kori Sanata Yoshikazu Higashitani ne a ranar Talata sakamakon rashin halartar zaman majalisar. Tunda aka zaɓe shi wata bakwai da suka gabata, ko sau daya bai taɓa halartar zaman majalisar ba. Kwamitin Ladabtarwa na majalisar ne ya yanke hukunci korarsa saboda ci gaba da…
Read More
Rashin haɗuwar tawagar alƙalan New York ya tilasta ɗage tuhumar Trump

Rashin haɗuwar tawagar alƙalan New York ya tilasta ɗage tuhumar Trump

Batun tuhumar da ake yiwa tsohon shugaban Amurka Donald Trump a game da bai wa wata jarumar fina-finan batsa maƙudan kuɗaɗe a matsayin toshiyar baki don kada ta tona abin da ta ce ya taɓa shiga tsakaninsu ya ɗauki sabon salo a ranar Laraba, bayan da tawagar alƙalan birnin New York ta gaza zama kamar yadda aka yi tsammani, lamarin da ya tilasta ɗage yanke hukuncin zuwa mako mai zuwa. Tun bayan da tsohon shugaban na Amurka Donald Trump da kansa ya sanar da cewa ana shirin kama shi a wannan makon, lamarin da ya sanya raɗe-raɗin yiwuwar gurfanar da…
Read More